Dan Adam Complete
Dan Adam Complete
*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
*BABI NA D'AYA*
*KADUNA*
Misalin karfe 9:30pm Daidai na Daran Ranar Asabar,ya baro Office dinsa,Direbansa
Garzali ne ke Jansa Cikin Bakar Motarsa Bugatti.
Hon ya Zuba akofar Tamkamemen Get din gidan nashi Mai kama da Aljannar
Duniya,Megadinsa Habu ya Rugo da Gudu yazo ya Wangalemusu get Domin yasan Yallabai
ne ya Dawo Adaidai Wannan Lokacin.
Lokacin da Motar Ta Sulala parking Space kafin Tagama Daidaita Zama Sai ga Wasu
kyakyawan Yara Guda Biyu mace Da Namiji Wadanda Ashekaru bazasu Haura Shekara goma
ba Tsawonsu Daya Kuma kamaninsu Daya,sai dai mace Tafi Jiki da Kuma Tsukakkiyar
Fuska yayinda Namiji yake Siriri Ammh Fuskarsa nada Fadi,Farare Tas kamar Ka Taba
Jini ya Fito akallon Farko zaka musu ka Fahimci yaran yan gayu ne na Karshe Kodaga
ganin yanayin Kayan Kantin Dake Jikinsu Riga da Wando da Kuma yanayin Fatarasu na
Jin Dadi ne.
Da gudu suka isa jikin Motar Suka Bude Bangaren Baya Suna Fadin"Wlcm Daddy..."Atare
na Kallesu na sake sai alokacin Naga Dimple dinsu ya Lotsa Agefen Kumatunsu Lokaci
Daya Yaran masu kama da Juna Sosai Inaga ma yan"biyu ne,Bangama Mamaki ba Sai da
Naga Wani Cute and Handsome Ya Fito Daga cikin Motar yana Sanye da American Suit
masu Ruwan Toka ya Matse Wuyansa Da Tie,Fuskarsa Tana bayyana Tsantsan Farincikin
Dayake Ciki Naganin Kyakyawan Yaransa dayake Alfahari dasu
Rumgumesu yayi yana Shafa kansu yana Fadin"Thank u my Childreen..."Yake Fada Shima
Duka Kumatunsa na Lotsawa,aShe anan yaran Suka Dibe Tsantsan kyau da Kuma Kyan
Jiki,Dogone kakkarfan Namiji ne mai Tsawo da jiki da Fadin Kirji,Dan Kimanin
Shekara 43 aduniya ammh kuma Bazaka iya Kiramasa Wadanan Shekarun ba Saboda Yadda
ya Mori Jiki da kyan Fuska Ba Fari bane Tas,Ammh Kuma Bazamu Sanyashi alayin Bakake
ba,Fatarsa Tafi Kama da yan Maroco,Saboda Murjewa da jin Dadi,doguwar Fuska gareshi
mai Dauke da dogon Hancinsa da Kuma Zagayayyen Bakinsa wanda Wani Bakin Saje yama
Wajen Kwanya gwanin Bam Sha"awa yana da Daradaran ido masu Dauke da Wasu Sirrika,ya
mallaki Zara zara Gashin Ido Tamkar yana kari,sai Giras sa Dake Cike da gashi Kamar
Wani Mace.
*ALHAJI TAHIR MANSUR DA'N BATTA* Kenan babban Manaja ne Dake kula da kamfanin
*IBRAHIM KWATANO AND SONS LIMITED* Kuma Babban D"a Awajen Hakimin Dambatta Wato
Alhaji Mansur Danbatta,Kuma miji ga *FARIDA IBRAHIM KWATANO* Kuma Uba ga
*BASSAM,BASMA,NAILA...* Cikakken Jarumin Namiji mai Hakuri Hade Da Zati Da Haiba
Miskilin Namiji Wanda bai maida Rayuwar Duniya da Abunda Ke Cikinta ado ba,wanda
ake Alfahari dashi bayan iyayenshi Harta da Garinsa Danbatta Suna Alfahari da samu
D"a Irin Tahir daya Fito Daga Ahalinsu
Zumbura baki Basma Tayi Tana Fadin"Daddy ina Mami...? hararanta Bassam yayi
kafin yace"Eh ina Mami..? Kin manta dazu Munkirata da wayar *ANTY MUFEEDA* Tace
mana ba yau Zata Dawo ba.."Tura baki Basma Tayi kamar Zatayi Kuka Tahir Dake Tsaye
yana kallonsu Wani Takaichi yacikamai Ciki Jin Farida yau ma bazata Dawo ba,Hannun
Basma yakama yana Fadin"Bassam Karbomin briefcase Dina Hannun garzali muje
ciki.."da Hanzari Bassam yakarba Jakar Hannun Garzali yabi bayan Daddy Wanda ke
Rike da Hannun Basma yana lallashinta don Ita Haka Allah yayi ta akwai Kulafacin
Uwa ammh ba domin Haka ba yadda Farida ke Banzatar da Mijinta da ya"yanta yaci Ace
Basma Tadaina damuwa da Rashinta don ba yau Ake ba.
Suna Shiga Cikin Kayatattacen Falon Kukan Naila yafara Musu Maraba Inda Take
goye bayan Mufeeda wacce Ke Ta Faman Zagaye Falon Da Ita tana Faman Jijjigata ammh
Taki yin Shuru,Cike da Tsausayi da Takaichi Tahir ke Bin Mufeeda da kallo Wacce
Tajige da Zufa Duk da Sanyin Ac dake Falon Sakamon Naila Irin yaran nan Masu Kiba
kamar Kajin Agric,ayayinda Ita Kuma Mufeeda Take Doguwa Siriirya kamar Ta karye
saboda Rashin Nama,yarinyar sai Rinjayarta Take kamar zasu Fadi,daga gani Tafi
karfinta, gata yarinya karama Domin Ashekaru bazata Haura Shekara 16 ba,Doguwar
Fuska gareta mai Hade da Hancinta Shiba gajere ba,Kuma ba Dogo ba,Mufeeda baza ka
Sakata Cikin Jerin kyakyawan Mata ba sai dai Tsaka tsaki.
Tana ganin Sun Shigo Tayi Azaman Dukawa Tana Fadin"Sannu da Zuwa Daddy..."Cikin
Siririyar Muryanta Mai Cike da Yarinta,Amsawa yayi yana karisawa gareta bayan ya
saki Hannun basma yana Fadin"Mufee,Meya samu Naila ne Take Ta Kuka Haka..? Yafada
yana Mika mata Hannu Alamar Ta Kwantomai Naila din.
Batayi gaddama ba Ta Kwantota tana Mikamai ita Wacce Fuskarta Ta Hade da Majina da
Hawaye,Ya karbeta yana Kallon Mufeeda dake Fadin"Wlh bansani ba Daddy,Tundazu ta
Fara Kuka,na zata yunwa ne,sai na Hadamata Madara na bata taki sha,sai kuka take
ganin Haka sai iya ta amasheta nan ma Taki yin Shuru Sai Kuka take tana Kiran Sunan
Mamanita..."Tafada itama kamar Tayi kukan.
Mirmishi Tahir yayi yana Rimgume Naila wacce ke ajiyar Zuciya ta Kwanta Luf akan
Kafadarshi,Kallonsu Bassam yayi kafin yace"Kunci Abinci..? Suka gyada kai alamun
Eh,bai kara mgana ba ya Wuce ya Fara Haura Steps yana Dauke Da Naila kafin ya tsaya
ya waigo yana Fadin"Oya kuje ku kwanta sai da safe.."Yafada yana Tamke Fuska Sum
Sum Bassam da Basma kowanne ya Nufi Dakinsa yana Bata Fuska yayinda Da Mufeeda Tayi
Tsaye tana kallonshi Ido ya sakarmata Fuska ba Walwala yace"Tsayuwar me kikeyi ke
kuma..? Jikin Mufeeda na Rawa Tace"Ba...bakomai Dama dama..."Tafada tana Sosa kai
Ware idonshi yayi kafin yace"menene..? Akwai Matsala ne..?
Kanta na kasa tace"Dama zance ne Daddy baka ci Abinci ba gashi chan iya taga jera
maka akan Dinning..."Mirmishi ya saki kafin yace"Karki Damu bana jin yunwa,ki koma
daki ki kwanta.."Kallonsa Tayi kamar Zatayi mgana sai ta Fasa ganin yadda ya
Sakamata ido,jiki asanyaye ta juya tana Fadin"Sai da Safe Daddy..."Alebensa ya
Karba da Fadin"Allah tashemu lafiya.,yafada yana kallonta Tana Tafiya kamar Zata
Fadi Cikin Sanyinta ta Shige dakinta,.
Ajiyar Zuciya ya sauke kafin ya juya yana Dauke da Naila,Ya Karisa Haura Step ya
Bude Kofar Farko Mai Dauke da Kayattacen Royal bed Wanda yaji Shimfidun Alfarma
gwanin ban Sha'awa Dakin bashi da Yawan Tarkace sai Wani Cafet Wanda ya mamaye
Dakin gabadaya mai Taushi yana Fitar da Kyalli Gwanin Ban Sha"awa sai Makeken
Wardrope mai Cinye Rabin Dakin,sai Dreesing Mirror kusa da Kofar Tiolet.
Kai Tsaye ya Karisa gaban Gadon sai da ya Haura Tsakiyar gadon Kana ya Kwantar da
Nihal Wacce Barci ya Kwasheta Tana Sauke Ajiyar Zuciya Jin ya Sauketa,Hannu ya saka
yana Shafa Goshinta Ahankali alamar lallashi nan da nan Ta Koma barci Saukowa Yayi
Daga Kan gadon yana Sauke Ajiyar Zuciya kafin ya Cire Coat din Dake Jikinsa,Ya
Rataye Kan Wani Dogon Abu Alamar na Rataye kayane,Towel ya Dauka ya Bude Kofar
Tiolet ya Fada da Addu"a Dauke Cikin Abakinsa
Akallah ya Ashafe Tsawon Minti Talatin Kafin ya Fito Daga Tiolet,kugunsa Daure da
Wani Babban Towel sai Kansa yana Rike da Karami yana Goge Ruwan Dake Diga asaman
kanshi kai Tsaye Wardrope din Dake dakin ya Nufa ya sanya Hannu ya Bude Kayane Jere
Bisa Hanger Iya Kallanka Mallam,gefen American Suit bakake da masu Ruwan
Toka,Dabam gasunan Ajere na Kowani Kamfani sai Wanda ya Zaba zai saka kama daga
DKNY,Tommy,hilfiger,Armani,louls,button,Doke,and Gabbana,Bersace,hakama bangaren
Manyan kaya Tazarce Kama daga Shaddodi,gezner,yadika Masu Kyau da Tsada Suma
bangarensu Dabam Haka bangaren Shirt da Jeans Suma Waje Gudane,bangaren Kayan Shan
Iska Irinsu Short Niker Da Riga mai Gajeren Hannu Suma Suna Waje na Dabam sai Daga
Kasa bangaren Kayan barci ne gasunan kala kala masu Taushi Da Tsari.
Cikin kayan Barci nashi Pjm ya Dauko Riga da Wando Masu Ruwan Toka Ruwa Na
Diga Daga jikinsa ya Zura Kayan,Ammh Rabin Hankalinsa na kan Naila dake Barci,Baro
Gaban Wardrope din yayi ya isa gaban Madubi ya Dauki Wani Turare Spry ya Fesa kafin
ya Mtsa Chan Gefe Inda Wata Katuwar Darduma Ke Shimfide ya Tsaya Shuru kafin ya
Daidaita Natsuwarsa ya Tada Sallah,
Tsawon Wasu Mintina ya idar da Sallar Shafa"i da Wuturi ya Dade yana Addu"a Kafin
Ya mike Wata Yunwa na Kwakulan Cikinsa In Har Bazai Manta ba,Rabonsa da Abinci Mai
lafiya da Kwari Tun Jiya Da Daddare kafin ya Dawo Gida Ishaq ya matsa masa Suka
biya ta gidansa Sukaci Abinci Toh bayan Shi banda Ruwan Coffea bai kara saka Wani
Abu mai Nauyi abakinsa ba,Cikinsa ya Shafa yana Tuna Kalaman Mufeeda yarinyar Tana
bashi Mamaki gata Karama da Ita ammh Tafi Farida sanin Halayyarshi Ta Kuma Fita
Karantar yanayinsa..,wata Zuciya tace Toh Ita Ke Zaune dakai Farida Yawon Biki da
Suna da Zuwa Gidan Kawaye Bai barta ta Zauna dakai ba Balle ta Karanci Waye kai
Tahir
Kansa ya Shafa yana Sauke Numfashi kafin ya Nufi Karamin Fridge dinsa Dake gefen
Gado yazauna kafin ya Bude ya Ciro Madarar Hollandia Hade da Kofi Silba wani Karami
mai kyau ya Bude ya Tsiyaya,Ya Shanye Duka Kafin ya sake Cikawa ya Kafa kai ya
Shanye yana Ajiyar Zuciya mai da Komai yayi Cikin Karamin Fridge din Kafin ya Dora
Kafafunsa Duka biyu kan Gadon Yana Kuma Jingina bayansa da Gado,ganin kamar Sanyin
Dakin yama Naila Yawa ne yasa ya Dauki Remote din Ac ya Rageta yana Kuma Kokarin
gyarama Naila Kwanciya Aranshi yana Tunanin Farida Wata Irin Uwa ce.
Haushin Hakane yasa Ya Mika Hannu ya Dauki Wayarsa Wacce Da Zai Shiga Wanka ya
Ijiyeta akan Side Drower,Cikin Lokaci Kadan ya Lulubo Nombarta Wacce Yayi Sarving
dinta da *WIFEY*, yayi Shuru yana Bin Wayar da kallo kafin ya cije baki ya Latsa
mata Kira yana kallon Agogon Bangon Dakin 10 ta Wuce,wayar ta Shiga Haka Ta Dinga
Ringing har Ta Katse Bata Daga ba,bai Hakura ba ya sake Kiranta Nan Ma har ta
Karishi Ringing ta Katse bata Daga ba,Tsaki yaja ya kife wayar Gefensa Kafin ya
Dauko Karamin Qur'anin Dake kan Side din Drower din gadon ya Bude Suratul Maryam
Inda ya Tsaya Jiya Da Daddare Kafin ya Kwanta Domin ya Riga ya Zamemai Jiki baya
iya Barci sai ya Karanta al"qur"ani Shiyaasa baya Taba Kwana da Bacin Rai.
Yafara Karatun Kenan Ahankali Cikin Zazzakar Muryansa mai Cike da Amo da Sauti mai
Dadin Sauraro Wayarsa ta Fara Kara Tana Neman Dauki sai da yakai Karshen Ayar Kana
ya Dago da Kanshi ya Dauko Wayar ganin Sunan Wanda Ke Kirane yasa Yayi Mirmishin
Dayafi Kuka Ciwo ya Daga Kiran Yana Fadin"Yanzu Farida Rayuwar da kika Daukanma
Kanki mai Bullewa ce..?
Dagachan Bangaren Farida Dake Gefe Cikin Wani Kayataccen Hal Ana ta Dinner Wajen ya
Kaure da Hayaniya Tare da Kidan Dj,Sanye Take da Doguwar Rigar Wani Ubansu Fefe les
Wanda yaci Dinki mai kyau da Tsari kalan blue Head din kanta Kuma pick Fuska Taci
Uban Makeup kamar Wata Amarya Doguwar mace ce Ammh ba Sosai ba,Fara ce, sosai sai
Kuma Akwai Kyau da Dirin Mata gaba da baya Masha Allah,Baki ta Bude Zatayi mgana
tana Yatsina Fuska Wanda Fararen Hakoranta Suka bayyana Tare da Hakorin Makkanta
Yana Daukan Ido Wanda yake Karamata kyau.
Cikin Kosawa Tace"Toh Uban Korafi Ai ina ganin kiran ka Nasan Abun da Kakirani ka
Fadamin kenan,Haba Tahir wai Yaushe ne Zaka Daina Kunyatani ne Gaban Kawayena..?
Tafada Tana Hararan Gefen Wayar Kamar Tana kallonshi,Shuru yayi yna Kokariin Danne
Bacin Ranshi kafin yace"Au kinfison Kada Ki Kunyata gaban Kaawayenki Ammh Kin Manta
da Lahirarki da Abunda Kikeyi zai iya Kaiki Wuta Farida...? Baki ta Tura Kafin
Tace"Na Shiga Uku Wai Don Allah Tahir me nakeyi Ne..koda yaushe mganar ka kenan Zan
Shiga Wuta.."ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace"Yanzu Fisabillah Kwananki nawa
bakinan Kin Saka Kafa Kin Fita kin Zubar da ya"yanki Da Mijinki da Gidanki Abun
Takaichi Wai Da Sunan Bikin Kanwar Kawarki Farida Anya Kina Son Gamawa Da Duniya
lafiya..?
Daure Fuska Tayi Kafin Tace"Ikon Allah,duk mai ya Jawo Wannan mganar..? Inace Su
Bassam Sun Girma Suna da Wayon da Zasu Kula da kansu,..."Ya katseta da Fadin"Naila
fa..? Kin ijiye mai Bata Nono ne..? Yamutsa Fuska Tayi kafin Tace"Ina Mufeeda..?
Miye Amfaninta dama Don Ta Kula da Ita na Amince nama goggo Mgana Anemin ita,Mganar
Abinci Kuma I know iya bata Wasa Komai Kuke Bukata Zata Girka Ta Baku ,Toh kuma Wht
Else Tahir..?
Yar Dariya ta Saki kafin tace"ai dama na sani Duk Wannan Kumfar bakin naka Saboda
Ban Dawo na sakarma Jiki kayi yarda kaga dama bako..? Wai Tahir na Tambayeka..?
Bata bashi Ikon Mgana ba Ta Cigaba da Fadin"Kai baka gajiya da Sex ne,Narasa Wani
Irin Miji Allah ya Hadani Dashi Haba Abu kamar Bambaran Masara Kaga Mallam Nifa ba
Sex machine bane balle Ka Ringa Hawata Duk sanda Kaga Dama Ina laifin Sau Daya
Asati,ga Kawaye nan Su Binta su Zeenat Su Smarty Ba Wacce Mijinta ya Kirata balle
ya Takura mata sai ni Dayake Allah ya Hadani da Ustaz dan Jaraba Sai na Koma na
Nanike a gindinka Tahir Duk Shekara kana Min Ciki ina Haihuwa Kamar Waata Akuya
ko..? Toh Wlh Baka isa ba,Hakan bazata Taba Faruwa ba Don Allah kar ka sake Kirana
Zan Dawo Tunda ba dauwama Zanyi Achan ba,Muna Wajen Dinner so gobe zamu kai Amarya
Kano Dagachan Zan biya na kwana Awajensu Abba may be Sai Jibi zan Dawo..."
Daga Haka ta yanke Kiran Tana Hararan Wayar Kafin Ta saki Tsaki Tana
Fadin"Fitinanne..."Wayar ta kashe Gabadaya Ta Wurgata Jaka kafin Takoma Wajen
Kawayenta Wadanda Keta Kallonta Tundaga Nesa Suna Dariya
Tahir yaji Wani Abu na Tasomai Daga Kasan Ransa mai kama da Fushi Da Bacin Rai ammh
yana Dannewa Wayar yabi da Kallo kafin ya Sauketa yana Sakin Ajiyar Zuciya,yana
Kokarin bama kanshi Hakuri,Ammh Dole ne gobe yayi sammako yaje Kauye wajen Goggo ya
sanar da Ita an Kawo Limit din Daya Gaji da Zama da Farida Saboda Haka In bata
Amince ya Saketa ba Toh Dole Ta Yarjemai ya Kara Aure,Domin Shi ba Dutse bane
lafiyayyan Namiji ne mai Bukatar Kulawar Mace Wanda Keson Ya"yan sa Fiye Da
Kansa,yana Bukatar Wacce Zata Kula da Duka bukatunsa dana ya"yansa Wacce Take
Daraja Aure ba Sakarya Irin Farida ba,wacce In Har ya Lissafa Daidai Wlh Tafi Wata
biyar Rabon Data Hada shimfida Dashi,ko bayan Haihuwan Naila bai Wuce Sau Uku Suka
Hadu ba.
Ijiye Qur"anin yayi yana gyara Kwanciyarsa Hannu ya saka ya Kashe Hasken Dakin
Kafin ya Kunna Dumlight,blanket yaja Ya Rufe kafafunsa Zuwa Kugunsa Inda ya Hada da
Naila ya Rufe Mata Rabin Jiki kafin ya maida Kanshi Bisa Filo yana Nanata Dalilin
Goggo na Banza Data Dogara dashi Ta Hanashi Kara Aure,Wai da Cewa yana Aiki
karkashim Mahaifinta Shi ya Rikeshi Kome ya Zama Shine Sila,Shi kuma Wannam bai
Dameshi ba Tunda Son da Iyayen ke mata yasa Suka kasa Tsawarta mata ,Shikan Wannan
Karon ba Gudu baja da baya Koda Kuwa hakan zai saka Alhaji Ibrahim Mahaifim Farida
ya Yanke Harkan Nemanshi yaji ya yarda Arziki na Allah ammh In yafada Halaka fa..?
Ba wanda Zai Zargi Farida Illah Shi da Zai Shiga Cikin Duniyar Nadama na Har Abada.
*Comment,Share,vote..And Like..*
*Shakira*
*Aisha Alto*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA BIYU*
Tun bayan daya dawo daga masallaci shida Bassam lokacin 7 saura na safe, kai
tsaye ɗakinsa ya koma ya iske Naila ta tashi tana ta kuka, ɗaukanta yayi yana
lallashinta ya shiga toilet da ita ya tuɓe mata kaya ya zage yayi mata wanka tsab
domin taji daɗin jikinta amma duk da haka Naila 'yar wata goma sha ɗaya bata bar
kuka ba daga gani yunwa takeji shiyasa yana gama mata wankan ya naɗota cikin towel
ya sauko ƙasa zuwa ɗakin Mufeeda yana ƙwala mata kira.
Iya dake kichen ta fito jin yana kiran Mufeeda agaggauce in kaji ance Iya zaka zata
tsohuwa ce ko ɗaya matashiyar dattijuwa ce mai kimanin shekaru hamsin da wani abu
kawai su Basma ne ke kiranta Iya tun sanda Mami ta aiko ma Farida da ita daga Kano,
shine kowa ya kama.
Ganin Tahir da kanshi yasa ta washe baki tana faɗin "Alhaji kai ne..? Kar dai 'yar
rigimar ta tashi da kukanta yau, barka da safiya..?" Yana murmushi ya ranƙwafa yana
faɗin "Ina kwana Iya..?" Ta amsa cike da jin daɗin yadda Tahir ke girmamata da
darajata, take faɗin "Hala rigima Naila keyi bata ga uwarta ba..?" Yana sosa kai
yace "Eh wallahi Iya inaga yunwa takeji ne, na mata wanka amma har yanzu bata bar
kuka ba shine nazo zan bama Mufee ita ta bata madara ko tayi shiru.." Iya ta miƙa
hannu ta karɓeta tana faɗin "Eh kuma da yunwar inaga bari na dama mata inaga
Mufeeda barci ne ya kwasheta don nima yau najita shiru bata fito ba..." Miƙa mata
ita yayi kafin yace "To Iya..." Daga haka ta juya ta nufi ɗakin Mufeeda inda kayan
madaran Nailan suke da komai nata, shi kuma ya juya ya haura sama.
Wanka ya shiga yafi minti talatin kafin ya fito domin Tahir akwai daɗewa wajen
wanka, yana fitowa ko mai bai tsayawa shafawa ba don Tahir kwata kwata baya ƙaunar
shafama jikinsa wani abu, wardrope ɗinsa ya buɗe ya ɗauko ɗaya daga cikin fararen
gezner ɗinshi ɗinkin tazarce, wanda ya amsheshi sosai aikin jikin shaddar baƙi ne,
hular kansa zanna bukar mai zanen baƙi ce, haka rufaffen takalmin ƙafarsa ma baƙi
ne, sai kyakkyawan haɗaɗɗen baƙin agogon fatar dake hannunsa na kamfanin Rado, shi
kanshi Tahir daya kai duban kanshi a cikin madubi sai da ya murmusa a ransa yasan
cewa tabbas shi mai kyau ne kuma ko a cikin maza sai an tona uwa uba kuma Baba
Hakimi zaiji daɗin ganinsa yau cikin shigar manyan kaya.
Yana gyara zaman hulan kansa wayarsa riƙe a hannunsa yake saukowa daga saman
step ƙamshin turarensa na Man na tashi tun kafin ya ƙariso, Basma da Bassam da
Mufeeda wacce ke goye da Naila bayan ta bata madaranta ta sanya mata wata bulawus
mai kyau tayi shiru ta goyata ram a bayanta, haka itama tana sanye da riga da siket
na atamfa cikin wanda Daddy ya ɗinka musu ita da Basma, sai Iya dake gefe suna
zaune bisa wani ƙaton ƙayataccen teburin cin abinci mai kama dana alƙarya guda,
dama haka aƙidar gidan Tahir yake ba'a nuna bambamci da bare dana gida duk ɗaya
ake, kowa dake gidan, in ka ɗauke Megadi da Direba ne kaɗai basu haɗuwa suci abinci
tare Farida kuma bata damu ba, don bata cikama zama agidan ba balle ra'ayin Tahir
ya dameta, tun Iya da Mufeeda basu saba ba har sunzo sun saba domin dukkansu sun
haura shekara biyu a gidan..
Tun daga nesa yaran suka zuba mai ido suna kallonsa harda Mufeeda wacce duk sanda
taga Tahir sai taji ta raina duka mazan duniya domin ya gama cika kowani mizami da
zati, ga kyau ga asali ga nasaba da kyan hali har misaltawa takeyi a cikin ranta
Allah ya bata miji irin Daddy wanda ya iya ɗaukan wanka da gayu, tunaninta ya katse
ne sanda taji su Bassam na gaisheshi, amsawa yayi yana shafa kan Basma yana faɗin
"Babyna kin tashi lafiya..?"
Tana haɗiye chips ɗin data tura abakinta tace "Lafiya lau Daddy. Allah Daddy Today
u look so Fine kamar ɗan saurayi ko Bassam..?." Ta faɗa tana dariya gyaɗa kai yayi
yana faɗin "Eh mana Daddy.." Dariya yayi fararen haƙoranshi suka bayyana yana
kallon 'ya'yan nashi cike da jin daɗi ya ɗago kenan karaf idonshi ya faɗa ana
Mufeeda data shagala da kallonsa rage fara'arsa yayi yana faɗin "Mufee uwar Naila,
har tayi barci ne..?"
Saurin dawowa cikin hayyacinta tayi kafin ta sadda kai ƙasa tana faɗin "Eh Daddy,
Ina kwana..?" Yana duba agogon hannunshi ya amsa Iya tace "Ai da zarar Mufeeda ta
goyata zaka nemi kuka ka rasa sai kuma barci ai inaga ko aure Mufeeda zatayi Alhaji
sai kun yi haƙuri Naila tama Mufeeda zaman ɗaki.." Ta faɗa Tana dariya, shima
murmusawa yayi Basma ko dariya ta saka tana faɗin "Mufeedan Iliya mai rake..." Ta
faɗa tana ma Mufeedan gwalo, itako tana ɓalla mata harara, duk yana lura dasu, bai
tanka ba sai ma ya maida hankalinsa wajen kallon agogon hannunshi yana faɗin "Kunga
lokaci na tafiya ku kula da kanku zan tafi Ɗanbatta.."
Ya faɗa kanshi tsaye yana ƙoƙarin ɗaga fulas ɗin ruwan zafi dake wajen ya tsiyaya
ruwan cittan cikin wani kofi Basma ce ta miƙe tana faɗin "Kai Daddy shine bakace mu
shirya ba." Bassam yace "Eh mana Daddy don Allah zamu bika mun kwana biyu bamu bika
ƙauye mun je mun gaida Goggo da Inno ba.." Ya faɗa yana ɓata fuska, Mufeeda ko
tunda taji an ambaci Ɗanbatta idonta ya ciko da hawaye tana tunanin kullum sai tayi
mafarki gata gaban Inna Fulera suna hira da dariya, amma sai ta tashi taga ba haka
ba, rabonta da garin yau wata biyar kenan tun auren Lantana data roƙi Daddy ya saka
direba ya kaita tayi kwana ɗaya ta dawo.
Yana kurɓan ruwan cittan daga tsaye ya dakata yana faɗin "Islamiyanku fa..? Kuna
so yau kuyi missing ne..?" Ya faɗa yana kallon fuskokin Bassam da Basma, Basma ce
ta fara buga ƙafa tana faɗin "Plz Daddy na yau kadai...plz Don't say no..." Ƙura
mata ido yayi yana kurɓan ruwan Lipton dake hannunsa kafin ya sauke yana faɗin
"Ok..ok kuje ku shirya sai mu tafi.." Ya fada yana ajiye kofin ruwan lipton ɗin
dake hannunsa.
Jin abunda yace ne yasa Bassam da Basma suka daka tsallen murna suka rungumeshi
suna faɗin "Tanque Daddy..." A tare suka bashi peck agefen kumatunshi kafin su
sakeshi kowa ya rumtuma zuwa ɗakinsa yana murna, Iya na musu dariya, Mufeeda kuwa
shiru tayi ta duƙar da kai tana ƙoƙarin share ƙwallar data biyo gefen ƙunnenta,
Tahir na lura da ita sai ya murmusa yace "Kema Mufee tashi kije ki shirya ki kuma
shirya Naila duka mu tafi harda Iya, tunda bazamu barta ita kaɗai a gida ba.."
Mufeeda jitayi kamar an sakata agidan aljannah Firdausi haƙoranta duka awaje tace
"Da gaske Daddy...?" Kai ya gyaɗa mata yana kallonta yadda jikinta yake rawa saboda
murna, ga goyon Naila amma haka ta kwashi gudu ta shige ɗaki da mamaki Tahir ke
kallonta ganin goyon na rinjayarta Iya kuwa miƙewa tayi tana dariya tace "Nagode
Alhaji kamar kasan ko ina son komawa garin nan naku gaskiya iyayenka ko nace
gidanku suna da kirki sosai..." Ɗan murmusawa yayi baiyi magana ba illah ficewa da
yayi yana faɗin "In kun shirya ku sameni awaje.."
Mintina talatin yayi musu yawa kowannensu ya shirya baki yaƙi rufuwa karma
Mufeeda taji labari wacce ke ji kamar ta buɗe ido ta ganta gaban Inna Fulera saboda
yadda ta zaƙu ta ganta, ta chanza kayan jikinta wannan karon less ne ajikinta riga
da zani, sai hijabinta hakama Basma itama wata shadda ce ajikinta iri ɗaya dana
Bassam itama hijabin ta saka don Tahir bai yarda da sanya mayafi ba kwata kwata
bama ya yarda ya siyo musu ko Farida ta siyama Basma bata sakawa in Daddy na nan
saboda tasan baya so, hakama Iya ta shirya itama tsab, kayan abinci Tahir yasaka
aka ɗebo daga Store aka cika booth ɗin motar kafin Garzali ya shiga mazaunin direba
Tahir ya shiga gaba Mufeeda da Basma da Iya da Bassam suka shiga gidan baya da yake
motar nada yalwa, nan da nan yayi ma mator key ya saki horn lokaci ɗaya Megadi ya
wangale musu get suka sulala waje yana musu fatan isa lafiya da kuma dawowa lafiya.
******
*ƊANBATTA*
Ƙarfe 11pm na safe motarsu ta tsaya adaidai ƙofar gidan Hakimi wanda tunda suka
shigo garin Ɗanbatta yara ke bin motarsu da gudu ana faɗi ga Tahir ɗin gidan Baba
Hakimi nan yazo saboda yara da manya sunsan yadda in yazo suke warkewa domin haka
zai fito ƙofar gida yayi ta rabon kuɗi baya tsayawa sai ƙudin dayazo dashi duka sun
ƙare, shima tunda suka shigo garin yake ta amsan gaisuwan mutane daban daban har
zuwa ƙofar gidan mahaifin nashi wanda ke zaune a ƙofar gida kan wata kujera daga
ƙasa kuma wata ƙatuwar tabarma ne mutane na zazzaune talakawa masu kawo ƙorafe
ƙorafansu, shiko mai girma Hakimi Mansur na zaune bisa kujeran nan yana sanye da
babbar riga kansa da rawani farin dattijo ne mai farin gashi da dattako, tunda
motar ta tsaya farin ciki ya cikashi na zuwan ɗan nashi mafi soyuwa a cikin ranshi,
nan da nan mutanen wajen suka miƙe kafin ma Garzali ya zagaya ya ɓude mai murfin
motar har ansamu waɗanda suka buɗe mai suna mai barka da zuwa kamar wani babban
mutum zakuyi mamakin yadda dattawa ke girmama Tahir sakamakon mutum ne nagari
hankali da hikima kuma duk abokan mahaifinsa ne ya zauna cikinsu lokacin yana zaune
agarin kafin ya koma cikin garin Kano domin yin makaranta sakamakon shine ɗa ƙwara
ɗaya tak namiji da Allah ya bama Baba Hakimi.
Hannu ya basu suna musabaha lokaci ɗaya yana ranƙwafawa alamar girmamawa har zuwa
bisa tabarman dake wajen ya duƙe yana gaida mahaifinsa hakama Bassam yayi, miƙa
masa hannu Baba Hakimi yayi yana faɗin "Yaka nan samarin birni.." Ya faɗa yana
dariya tashi Bassam yayi yaje kusa da Baba Hakimi ya zauna ya miƙa mai hannu sukayi
musabaha yana tambayanshi ya karatu daidai ƙarisowan su Mufeeda suma durƙusawan
sukayi suna gaisheshi da mutanen dake wajen amsawa yayi cike da murna yana kallon
fuskokinsu kafin yace "A'a amaryata me kika zomin dashi..?"
Basma na dariya tace "Kaji ka me nazo maka dashi ko kuwa mai ka tara min? Nazo
karɓan nawa kajin ne da zabbin wannan shekarar.." Ta faɗa tana dariya gaba ɗaya
wajen sai da aka murmusa ganin duka haƙoran Hakimi awaje yana dariya kafin yace "Au
hakane, toh ki shiga ciki ki kama iya iyawarki, amma in Abu ta ganki ba ruwana.."
Miƙewa tayi tana faɗin "Sai me..? Nida abun mijina.." Ta faɗa kamar da gaske,
Dariya yayi yana kallon Mufeeda wacce ta sauko Naila data fara rigima hannu ya miƙa
mata yana faɗin "A'a wanake gani kamar 'yar wajen Fulera...?" Tahir dake gefe ya
taso ya karɓi Naila ya miƙa ma hakimi yana faɗin "Eh itace ranka ya daɗe.." Karɓan
Naila yayi yana faɗin "Masha Allah...Allah yayi maka albarka Attahiru, kai kaga
yara duk sun girma gama wata amaryar tawa inaga fa nan zan dawo.." Ya faɗa cike da
barkwanci yana kallon fuskar Naila wacce ke zare ido tana bin kowa da kallo, dariya
aka sakama Hakimi jin abunda yace, miƙewa su Mufeeda sukayi suka shiga cikin gidan
suka bar Bassam da Tahir da Naila dake hannun Hakimi.
Gidansu Tahir babban gida ne mai ɗauke da shashe huɗu ginin bana ƙauye bane amma
ginin gidan sarauta ne, duk da yanzu Tahir ya ƙara gyara gidan sosai shashen farko
na Baba Hakimi ne na biyu kuma na uwargida sauratar mata wato mahaifiyar Tahir
Zainabu Abu wacce suke kira Goggo, sai shashe na uku na mai bi mata ne Salamatu
wacce suke kira Innaro sai shashen ƙarshe wacce na marigayiya Binta ne aka mai
dashi ɓarayin 'yan aiki da kuma wajen ajiye hatsi, gidan Hakimi cike yake da
al'umma daban daban kuma babu 'ya'yansa ko ɗaya sai 'ya'yan talakawa da mutanen
gari da kuma masu musu hidima acikinsu harda Inna Fulera mahaifiyar Mufeeda tana
ɗaya daga cikin hadiman gidan Hakimi masu dafa musu abinci.
Tun isowarsu yara suka shiga da gudu suka sanar da zuwansu toh dayake Basma ta
rigasu shiga suna shiga suka isketa kwance kan ƙafar tsohuwa mai ran ƙarfe Goggo
Abu kana kallonta kaga inda Tahir ya kwaso kyawawan idanuwa da dogon hanci, gashin
kanta cike da furfura ta zauna bisa wani lallausar cafet daya mamaye tsakar ɗakinta
mace mai kirki da sanin ya kamata suna shigowa da sallama ta ɗago tana amsawa cike
da fara'a lokaci ɗaya tana yi musu maraba.
Gefenta suka zauna Iya ta fara gaisheta ta amsa cikin sakin fuska kafin Mufeeda
wacce ke wulga ido tana son ganin ta inda mahaifiyarta zata ɓullo, cikin fara'a
Goggo Abu tace "Mufeedan Fulera an zama 'yan mata ko..?" Ta faɗa tana dafa kanta
murmushi tayi tana sadda kai kafin Iya tace "Aikam duk sun girma Goggo harda wannan
lukutar banzar data haye miki ƙafa.." Ta faɗa tana zungurin Basma wacce ta tura
baki tana faɗin "Kai Iya don ma ta samu na hau wannan ƙafar nata data kusa
expier.." Make mata kai Goggo Abu tayi tana faɗin "Tashi ja'ira so take ta ƙarisa
ni ta samu damar auren min miji ita kaɗai.." Dariya suka saka banda Mufeeda datayi
shiru ganin haka yasa Goggo Abu ta tattaka ta miƙe bayan ta ture kan Basma tana
faɗin "Ku tashi ku shiga shashen Innaro ku gaisheta inaga bataji zuwanku ba.." Ta
faɗa tana nufar hanyar ɗakinta na ƙurya, miƙewa sukayi suka fita sai shashen Innaro
ita ma falonta kamar na Goggo Abun ne durƙushewa sukayi suna gaisheta ta amsa cikin
sakin fuska tana yafito Basma da hannu ta ƙariso da sauri ta kwanta ajikinta cike
da shagwaɓa tana faɗa mata wai Goggo Abu ta hanata zama a cinyarta Innaro na dariya
tace "Aiko zata gamu da mai girma Hakimi amarya guda ai dole mu lallaɓaki.." Ta
faɗa tana dariya Iya na tayata Mufeeda ce tace "Innaro ina Innata tunda nazo ban
ganta ba, ko ta koma gida ne..?" Innaro tace "A'a Innarki na madafi Mufeeda.." Jin
haka yasa Mufeeda ta tashi da sauri ta fice kamar zatayi tuntuɓe su Basma suka bita
da kallo Innaro tace "Yi a hankali Mufeeda karki faɗi, ina ruwan Mufeeda akwai
ƙulafucin uwa ni banzaci ma zata yarda ta zauna gidan Attahiru har tayi wannan
daɗewar ba.."
Iya tace "Toh ya zatayi amma fa ranar da aka tuna da Inna Fulera toh wuni za'ayi
sharan ƙwallah.." Innaro ta saki murmushi kafin tace "Allah sarki ina ruwan Mufeeda
haka itama uwar take sai dai dayake ita tana da kunya da kawaichi ko tana kewar
ɗiyar tata bata taɓa nunawa.." Iya tace "Allah sarki..Haka abun yake bagashi yanzu
tasamu kyakkyawar rayuwa ba ai wallahi babu abunda zamu ce ma Alhaji sai fatan
gamawa da duniya lafiya.." Innaro ta gyaɗa kai tana faɗin "Ameen Ameen...Haka
Attahiru yake kowa nashi ne, yafi son kyautatama mutane fiye da ya kyautatama
kanshi.." Iya tace "Ba shakka munga zahiri muda muke zaune tare dashi.."
Mufeeda ko tana fitowa daga shashen Innaro ta nufi babban madafin gidan Hakimi nan
tayi ta gamo da 'yan aikin gidan suna gaisawa kowa na mamakin ta ƙara girma gabda
shiga madafin sai ga Inna Fulera ta fito da sauri domin itama ta samu labarin zuwan
su Mufeedan kamar a mafarki suka ci karo ido Mufeeda ta zaro tana faɗin "Innata..."
Da ƙarfi kafin ta rumgumeta cike da murna itama cikin tsantsar farin ciki ta
ƙanƙameta tana murnan ganin ɗiyarta tilo ƙwara ɗaya da Allah ya bata.
Ɗagowa Mufeeda tayi tana hawayen farin ciki tace "Innata banzata zuwa ganinki ba
ayau...Kina lafiya..?" Kanta Inna Fulera ta shafa kafin ta gangaro tana share mata
hawayen fuskarta tace "Nima haka farin cikina, yanzu Gaje ke sanar dani zuwanku
kunzo lafiya..?" Farin cikina kin ƙara girma kina jin daɗin zaman gidan Alhaji ko?"
Gyaɗa kai Mufeeda tayi idanunta cike da ƙwallah tana dariya tace "Innata mu koma
gida akwai labari.." Dariya Inna Fulera tayi kafin ta riƙo hannunta tana faɗin
"Yanzu kuwa farin cikina, bari na barma Maman Lantana sallahu sai mu tafi.." Da
sauri Mufeeda tace "Yauwa Innata Lantana fa..? Ko sun tafi birnin ita da
Ladonta..?"
Inna Fulera tace "Tun yaushe bayan auren da wata biyu suka tafi can Kano gidan da
yake gadi da zata tafi tazo tamin sallama tayi tacewa na gaisheki.." Kawai sai
Mufeeda ta hau sharar ƙwallah tana faɗin "Allah sarki Lantana Allah sa mugana.."
Murmushi Inna Fulera ta mata suna riƙe da hannun juna suka nufi madafi Mufeeda
maƙale da ita tana mata surutu.
*******
Tahir ya daɗe awaje wajen Baba Hakimi da jama'ar wajen bai shigo ba sai da ya gama
rabama mutanen wajen kuɗin da yazo dashi yara da manya, Bassam ya aika yace ya
sanarma Goggo Abu ta dama mai fura shida Garzali, nan ya shiga ciki ya barsa toh
bai shigo ba sai da yaq gama da wajen kana yama Hakimi sallama da zai shiga wajensu
Goggo.
Goggo Abu na zaune ta gama dama ma Tahir furarsa kenan ta tsiyayarma Garzali
nashi cikin wani kofin silba mai kyau ta miƙama Bassam kenan yayi sallama ya shigo
kafaɗarsa ɗauke da Naila wacce tayi barci hannun Hakimi, Goggo Abu ta ɗago tana
amsa sallamar nashi fuskarta cike da annuri kai tsaye gabanta ya nufa yana ƙoƙarin
zama ta miƙa hannu tana faɗin "Kawo ta nan dama da ita kukazo..? Ina uwarta take ne
kuka zo da ita ita kaɗai..?" Ta faɗa tana karɓanta lokaci ɗaya ta miƙe ta shiga da
ita ciki ta kwantar da ita shi kuma Bassam tuni ya fice zuwa waje ɗauke da fura zai
kaima Garzali Allah Allah yake ya fita ko ya samu damar shiga cikin gari kafin
Daddy ya farga bayanan don Bassam akwai son ƙauye musamman ma na Babansu.
Sai da ta fito kana tazo ta zauna inda ta tashi tana turamai kwanon sha mai cike
da fura da nono tana faɗin "Lafiya na ganku kamar daga sama inace shekaranjiya
mukayi magana da kai sai sati na sama zaka shigo ba.." Ta faɗa tana kafeshi da ido,
rausayar da kai yayi kafin yaja kwanon furan ya buɗe yana motsawa da ludayi kafin
yace "Goggo Farida bata nan ta tafi bikin ƙanwar ƙawarta Abuja tun wajen kwana uku
da suka wuce.."
Ya faɗa yana sadda kansa ƙasa, shiru Goggo Abu tayi kafin tace "Naji, shine dalilin
zuwanka kenan ko..?" Ta faɗa fuskarta ba annuri bai ce komai ba illah maida kanshi
ƙasa da yayi yana kurɓan fura itama ganin ya mata banza sai ta ƙyalesa sanin
halinsa na miskilanci, bai ƙara magana ba sai da ya gama shan furan nashi kafin ya
ture kwanon yaja murfi ya rufe yana faɗin "Alhamdulillah..."
Ya faɗa kafin ya gyara zama yana faɗin "Goggo ya jikin ɗan wajen Ashe..? Jiya munyi
waya take sanar dani Muda ba lafiya..?
Tana matsa ƙafanta data miƙar dasu take faɗin "Yaji sauƙi sosai ɗazu da safe nan
yake.." Daga haka bata ƙara magana ba matsowa yayi yana tayata matsa ƙafar yana
faɗin "Wai har yanzu ƙafar bata bar matsa miki ba Goggo..?" Bata kalleshi ba tace
"Tayi sauƙi kasan jikin tsufa fa abun sai a hankali..." Ta faɗa kai tsaye murmushi
yayi ganin yadda Goggo abun ke wani cin magani duk don karya mata maganar daya saba
ne, amma duk da haka bai haƙura ba gyara zama yayi yana matsa mata ƙafa yana faɗin
"Goggo akan maganar Farida ne, tsakani ga Allah na gaji da haƙuri da ita da kuma
hallayarta nazo ne na ƙara roƙonki ki bani dama na sanar ma da Baba Hakimi zan ƙara
aure..." Ya faɗa yana ƙoƙarin son su haɗa ido.
Ƙur kuwa tamai da ido kafin tace "Har sau nawa zan ce maka kabar wannan maganar
Attahiru, maganar Farida nace kayi haƙuri yarinta ke damunta banaso ka yi abunda
iyayenta zasu ga kamar mun ɗaure maka gindi ka tozarta musu yarinya. Cike da wani
jin haushi ya marairai ce yana faɗin "Toh amma Goggo..." Kabar maganar nan nace ko
Attahiru...?" Goggo Abu ta katseshi rai ɓace, kansa ya sadda a ƙasa yayi shiru yana
jin kamar ya kurma ihu, ganin yadda yayi ne sai tausayinsa ya kamata ta dafa kanshi
tana faɗin "Kayi haƙuri zan yi magana da ita Faridan insha Allahu kaji..." Kai
kawai ya ɗaga mata idanuwansa sun canza launi saboda ɓacin rai.
Ya daɗe zaune shuru kafin ya saki ajiyar zuciya ya miƙe yana gyara hulan kansa yana
faɗin "Bari na leƙa na gaida Innaro daga can zan gangara wajen Ashe naga jikin
Mudan." Kai ta gyaɗa kafin tace "Adawo lafiya.." Jiki asanyaye ya fice ta bishi da
kallo wani tausayinshi na ratsata amma kuma bazata bari ya sanar da Hakimi wannan
maganar ba sai ta ƙara magana da Faridan tunda abu na zumunci ana tare tun ba'a
haifesu ba bazata bari Tahir ya ruguza wannan zumuncin ba.
Koda ya shiga wajen Innaro Iya kaɗai ya gani koda ya tambayi Basma sai Innaro tace
ta tafi gidan Innarsu Ashe bai daɗe ba ya fito zuwa waje ya sanya Garzali ya buɗe
booth yace ya shiga da kayan ciki, shi kuma yayi sallama da Hakimi akan zai gangara
gidan Ashe dayake babu nisa da ƙafa ya taka, duk inda yabi ana gaisheshi cike da
girmamawa da ban sha'awa har ya isa gidan Ashe can ya iske Basma da Bassam wanda ya
gansu a ƙofar gida shida Mudan wanda sa'an Bassam ɗin ne, ita kuma Basma suna cikin
gida ita da Laila ƙanwar Mudan ce 'yar wajen AShe dayake tana da tsawon ƙafa har
takamo girman Basma.
Nan Mudan ya ɗuka yana gaida Kawun nashi shi kuma ya riƙoshi yana hararan Bassam
da wasa shiko yana dariya riƙe da hannayensu suka shigo gidan Ashe na ganin Yayan
nata ta shiga ina zata saka dashi Laila ma tazo ta gaisheshi ya riƙe hannunta yana
tambayanta karatu bai wani daɗe ba ya miƙe ya mata sallama zai tafi 30k ya fito
dashi daga aljihu ya bata ta karɓa tana ta godiya 5k ya bama Mudan da Laila yace su
siya wani abun buƙatar nasu suna ta murna har waje suka rakosu Ashe natama Yayan
nata godiya su Mudan kuwa har gidan Hakimi suka rakasu inda Tahir yace suyi haraman
tafiya nan fa aka nemi Mufeeda aka rasa Goggo Abu tace yanzu haka sun koma gida ita
da Inna Fulera Tahir bai damu ba yace sai su biya su ɗauketa nan ya cika Goggo Abu
da Innaro da kuɗi hakama Baba Hakimi wanda ya dinga sakamai albarka tare da nasihan
riƙo da gaskiya Allah ya taimakesu har sukazo tafiya Naila nata barci, wajen karfe
3 na yamma motar su tabar ƙofar gidan Hakimi bayan su Laila da Mudan sun sanar da
Kawun nasu wannan hutun yasa azo aɗaukesu agidanshi zasuyi hutu yace karsu damu in
sun samu hutun zai turo Garzali yazo ya tafi dasu, murna ta cikasu harda su Bassam,
wadanda suka kwaso zabbi da kaji gidan Hakimi wai zasu kiwata Tahir na kallonsu ko
tankasu baiyi ba bazai shiga tsakanin jikokin da Kakanninsu ba.
Daganan sai ɗan karamin gidan da Inna Fulera ke zaune suka tsaya Iya ne da Basma
suka shiga basu daɗe ba sai ga Mufeeda ta fito ita da Inna Fulera ganin haka yasa
Tahir ya fito yana amsa gaisuwan Inna Fulera wacce ke neman dukamai tana ta zubamai
godiya harda ƙwallarta kuɗi ya ciro 20k ya bata ta kasa karɓa sai kuka take tana
faɗin "Nagode Alhaji wallahi basai kabani ko sisi ba alherinka ga Mufeeda kaɗai ya
isheni ka tufatar da ita ka ciyar da ita haka zalika ka ilimantar da ita kuma baka
taɓa bambamceta da 'ya'yanka ba duk da ta kasance ita ɗin hadimarka ce mai renon
'ya'yanka wallahi bani da bakin gode maka sai dai nayi fatan Allah yasa kagama da
duniya lafiya ya kuma sakamaka da gidan aljannah Firdausi.." Da Ameen yake ta
karɓawa cike da jin nauyin godiyarta gareshi da ƙyar ta karɓi kuɗin suka rungume
juna ita da Mufeeda suna kuka gwanin ban tausayi kafin su saki juna Mufeeda ta
shiga mota suna dagama juna hannu har suka bar ƙofar gidan, sun fita cikin garin
kenan Naila ta tashi wacce ke hannun Tahir ya waigo yana kallon Mufeeda yana faɗin
"Toh Maman Naila bar kukan haka nan gashi tana kukan neman uwar ɗakinta.." Ya faɗa
cikin barkwanci yana miƙa mata Naila cikin jin kunya ta share ƙwallarta ta miƙa
hannu ta karɓeta nan da nan ta ɓalle jakar data zubo kayan madaranta da Flaks ɗin
ruwan zafi da ƙaramin kofi da cokali ta dama mata madaranta ta shiga bata nan da
nan takoshi sai kuma ta koma barci bisa kafaɗarta ta kwantar da Naila ita kuma ta
jingina kanta jikin ƙofar motar tana sharae ƙwallah..
Ta madubin gaban motar yake kallonta ajiyar zuciya ya sauke kafin ya murmusa yana
faɗin "Tasan kan renon yara.." Ya faɗa yana maida kanshi cikin jikin cussinon ɗin
kujeran motan shi kuma Garzali ya saki kan mota yana bata wuta.
*Aisha Alto*
*Anitha..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA UKU*
*ASALIN LABARI*
*HAKIMI MANSUR ƊANBATTA* Shine asalin sunan mahaifin Tahir wanda gabanshi da
bayanshi haifaffan garin Ɗanbattan ne kuma ya fito daga tsatson Hakimin Ɗanbatta ne
daboda haka sarautar Hakimi daya samu ba haye yayi ba gadon gidansu ne.
Tun suna samarinsu lokacin tasowarsu basuyi karatun boko ba lokacin bai yawaita
ba sosai sai dai karatun allo wanda yabi gari lokacin inda ake ɗaukan yara dawaya
daga kowane yanki suna zuwa karatun allo cikin Kano da sauraran garuruwa basu
dawowa har sai sun sauke alqur'ani wasun suma har sai sun fara sana'a, sunyi ƙarfi
kafin su waiwayi gida, toh hakan ne ta faru da Mansur wanda ɗane ga mai garin
Ɗanbatta, lokacin dayake da shekara tara a duniya aka tafi dashi cikin garin Kano
aka damƙashi hannun wani malamin addini mai suna Malam Haruna wanda amini ne yake
ga Hakimi Hayatu.
A lokacin ba dan talaka ko ɗan mai kuɗi ba ko yaron gidan sarauta a'a lokacin ilimi
bai yawaita kamar yanzu ba shiyasa zaka samu yara daga mabambantan garuruwa
ankawosu wajen Malam Haruna karatun allo duk kuma daya ke iyayen yara a lokacin
basu sake kamar na yanzu da in suka kawo yaro sai sun manta dashi a'a su kowane
bayan wattanni suna zuwa ganin 'ya'yan nasu kuma suna musu aike akai-akai.
Wannan shine dalilin haɗuwar amintakan Hakimi Mansur da kuma Alhaji Ibrahim Kwatano
wanda shima iyayensa suna da hali suka kawoshi nan makarantar Malam Haruna domin ya
sauke Qur'ani lokaci ɗaya haɗuwar jini da abota mai ƙarfi ta haɗasu kuma Allah
yayisu hazikai masu kaifin ilimi wanda har iyayensu duka suka shaida amintarsu
ahaka suka shafe shekara bakwai kafin suyi sauka murna ba'a magana Malam Haruna ya
shirya musu walima duka iyayensu suka zo suka tayasu murna, kafin kowa iyayenshi su
tafi dashi gida.
Ibrahim yayi sa'a dama already kafin yazo makarantar allon ya gama Primary Sch
ɗinshi suna komawa gida iyayensa suka mai cuku-cuku ya koma makarantar SS1,
ayayinda shi kuma Hakimi Mansur koda ya koma sai ya fara daga Primary 1 duk da
lokacin yana da shekara goma sha biyar ne toh kafin ya gama Secondry tuni Ibrahim
yana BUK inda yake karantar Business Admistration, shi kuma Mansur yana gama
Secondry karatunsa ya tsaya saboda rasuwar Hakimi Hayatu wanda dama Mansur ne kaɗai
ɗansa namiji sauran duk mata ne so sai aka ɗaura ƙaninshi ya cigaba da riƙon
sarautar maigari.
Mansur da Ibrahim suna ƙoƙarin ziyarar juna duk wanda ya samu dama Ibrahim na
shekarar ƙarshe mahaifiyar Mansur ta matsa mai sai yayi aure kafin ta mutu taga
kwanshi aduniya shine dalilin daya sanya ta nema mai auren ɗiyar ƙanin mahaifinshi
Zainabu Abu, wanda cikin lokaci akayi komai aka gama akayi biki lafiya sai bayan
bikin ne Ibrahim ya tafi service shi kuma Mansur yana zaune agidansu ɓarayin gadon
mahaifinsa shida matarshi Zainabu Abu mai kunya da kawaichi shekararsu ɗaya da rabi
da aure ta haifi kyakkyawan ɗanta mai kama da ubansa sak aka sanya masa suna Tahir
to bayanshi ta yi haihuwa biyu duka basu zo da rai ba, lokacin ne kuma itama
mahaifiyar mansur Allah yayi mata cikawa, wanda har iyayen Ibrahim sunzo gaisuwa
shi baya ƙasar yana ƙasar Ughanda yatafi haɗa Masters ɗinshi, tun kuma bayan
rasuwarta sai Abu ta shiga ɓari data samu ciki baya zama sai tayi barinshi kamar
bazata rayu ba abunda ya fara damunsu har suka fara neman mata magani amma kuma sai
cikin yayi kamar zai zauna sai kuma tayi ɓarinshi.
Sai da Tahir ya shekara 9 aduniya kana Ibrahim yayi aure bayan ya daɗe da dawowa
ya haɗa Masters ɗinshi Babanshi ya bashi kuɗi sosai ya ɗorashi kan kasuwancinsa
dayake dama shi ɗin motoci yake saidawa 'yan kwatano shiyasa yake amsa wannan
laƙabi bikin da Zainabu Abu ita da Mansur da Tahir sukaje suka kwana uku suka dawo
domin Mansur da Ibrahim basu yarda zumunci ba.
Matar Ibrahim Aliya itama 'yar gidan masu dashi ne irin yaran nan da jin daɗi yayi
musu yawa, shekaransu ɗaya da aure ta haifi yarta mace wacce aka sakama suna
Farida, yarinyar data ga gatan duniya sosai daga ɓangaren iyayenta zuwa na
kakanninta kuma tunda ga ita Allah bai ƙara basu haihuwa ba.
Tahir nada shekara sha uku aduniya lokacin har ya kammalah zana jarabawarsa na
Primary, Abu ta haifi 'yarta mace mai suna Aisha suna kiranta Ashe wacce Tahir yafi
ma iyayensu murna da ɗokin haihuwar Ashe tafi tafi rayuwa na nisa har zuwa lokacin
da Tahir ya kammalah Secodary School ɗinsa acikin makarantar Secondry dake garin
Ɗanbatta.
Tahir tun yana ƙaraminsa yaro ne mai son yayi karatu shima ya zama wani abu ya
taimaki iyayensa da garinsa na haihuwa wannan dalilin ne yasa wani ziyara da Alhaji
Ibrahim Kwatano ya kawo mai suka tattauna batun Tahir ɗin shikuma yayi mai
alƙawarin zai tafi da Tahir domin ya inganta rayuwarsa labarin dayayima Tahir dadi
sosai bai tafi dashi a lokacin ba sai da ya karɓi takardunsa ya tafi dashi ya nema
mai gurbin karatu a jami'ar BUK kafin yazo ya tafi dashi shi kanshi Mansur yaji
wani iri balle Abu da Ashe da suketa kuka amma sai Alhaji Ibrahim ya lallashesu da
cewa in suka samu hutun makaranta Tahir ɗin zai dinga zuwa yana gaisheshi.
Kai tsaye ya nema masa Admission bayan ya zaɓar masa course d'in da yayi wato
Business Asmitration domin yana sha'awa tare da burin Tahir ya zama yayi karatu ko
don ya taimakeshi bisa harkan kasuwancinsa tun bayan da mahaifansa suka rasu duka
kula da kamfanin mahaifin nashi ya dawo hannunshi gashi shi kuma ɗiya mace Allah ya
bashi zuwan Tahir gidan sai Farida ta samu Yaya duk lokacin tana da shekara tara da
wani abu sai ya kasance shike kula da ita koda home work d'in makaranta ne shi ke
mata in bai da lakca kuwa suna tare yana koya mata karatu inda bata gane ba kafin
kace me shaƙuwa mai zurfi ta shiga tsakaninsu duk kuma sanda ya samu hutu zai tafi
Ɗanbatta tare da Farida yake tafiya saboda bata yarda ya barta agida duk inda ya
saka ƙafa anan take saka nata al'amarin daya ke ma iyayenta daɗi domin basu da abar
farin ciki irin Farida shiyasa suka sangarta komai sai an mata basu la'akari da ita
macece, abun na cima Tahir tuwo a kwarya yadda Farida bamai gaya mata taji tun tana
ƙaramarta yarinyace mai ƙawayen bala'i da tarkace kowa nata ne ga kuma shegen zuwa
gidan ƙawaye tun tana ƙaramarta jikinta rawa yake in taji labari biki kowani event
da za'aje achashe sukuma iyayenta sun bata freedom wani lokacin ma Tahir ke taka
mata burki taji dayake tana tsoronshi.
Yana shekarar ƙarshe a BUK Allah yama Hakimin rasuwa aka kuma naɗa mahaifinshi wato
Mansur bai samu zuwa ba sai lokacin bikin mahaifinshi inda ya ƙara aure da Salamatu
Innaro, lokacin ne ya daɗe agida kafin ayi posting ɗinsu su tafi service ɗinsu suna
gamawa Abba Alhaji Ibrahim ya matsa mai ya tafi birnin US ya ɗora Masters ɗinshi
yana chan har mahaifinshi ya ƙara aure da Binta itama irin Salamatun ne har ta
shekara Allah bai bata haihuwa ba sai Hakimi Mansur ya haƙura ya fara tunanin ƙila
iya ƙwanshi da zai gani a duniya kenan.
Sai da ya shekara uku kana ya dawo lokacin Farida har ta gama Secondary Sch ɗinta
ta shiga BUK aji ɗaya a yayinda Ashe kuma take SS1 wanda yaje yaji wai za'a mata
aure shi ya hana yace don Allah abarta ta ƙarasa toh dalilin haka aka barta sai da
ta kammalah Secondry Sch ɗinta kana aka mata aure da yaron limamin garin Badamasi
suna zaune anan garin Ɗanbatta.
Dawowarshi ne yasa Abba ya buɗe mai kamfani a garin Kaduna wato *IBRAHIM KWATANO
AND SONS LIMITED* Wanda ya bama Tahir ragamar kula da wajen amatsayin manaja murna
sosai yayi ya dingama Abba godiya haka Hakimi Mansur da yaji sai da yazo har Kano
yamai godiya kowani masoyin Tahir in yaji wannan labarin sai ya tayashi murna da
farin ciki, lokaci kaɗan kamfani ya fara aiki bayan an zuba ma'aikata da masu kula
da abubuwa lokacin ne kuma Tahir suka haɗu da Ishaq wanda ke matsayin Accounting
Manager a kamfanin, sai tasu tazo ɗaya sakamakon amana irin ta Ishaq da kuma
hankali da sanin mutumcin kanshi shiyasa lokaci ɗaya abota mai ƙarfi ta shiga
tsakanin Tahir ɗin da Ishaq wanda shima ɗan asalin Kaduna ne.
A nan Kadunan Abba ya siyama Tahir gida wanda yake zaune da motar hawa mai tsada
saboda taƙaita zirga zirga daga Kano zuwa Kaduna da zuwa Ɗanbatta shekara uku
kamfanin yayi da buɗewa amma yayi ma saura zarra dama Tahir haka yake komai ya sama
hannu sai anga albarka kafin kuma wannan shekarun abba na matuƙar alfahari da samun
Tahir hakama iyayenshi don zuwa wannan lokaci hatta gidansu ya gyarashi tsab ya
kuma sakama duka iyayen nashi mata ababen more rayuwa a duka shashensu daya gina
musu, lokacin kuma shekara biyu da rasuwar Binta, Ashe ma sha tara na arziki yake
mata bama itama kaf al'ummar Ɗanbatta suna alfahari da samun ɗa irin Tahir saboda
shi baya da burin ya tara abun duniya illah yama jama'a hidima da kuma garin
haihuwarsa.
Cikin wata uku aka gudanar da bikinsu wanda yabar dimbin tarihi domin shagali akayi
kamar ba gobe, bidi'a kala kala don ma shi Tahir ɗin ya doje Ɗanbatta ya tafi bai
yarda ya zauna a kano ba sai ranar aure yazo shida Ishaq da tawagar Hakimi da
daddare kuma akayi dinner wanda Tahir yasha mamaki uban mutanen dasu kazo wanda shi
baisan ko ɗaya ba ashe duk jama'ar Farida ne, saboda tsabar zuwa bikinta har laƙabi
ake mata da Farida biki-biki, abun bai bashi mamaki da saninta da uban ƙawaye da
kuma son zuwa sha'ani ita ko bikin waye ko ba'a gayyaci Farida tana zuwa indai
tasan cewa za'ayi Event aji daɗi ashana ta sake yadda ranta keso balle shiganta BUK
ta ƙara samun ƙawaye na gari dana banza kuma ta ƙara yawo idonta ya buɗe amma bana
iskanci ba na wayewa.
Washegari aka kawota Kaduna Anguwar Rimi Gra a babban gidan da Tahir ya gina da
guminsa Farida taga gata gaba da baya domin da tsala tsalan motocinta biyu aka
kawota gidan, ko wata ɗaya basuyi da aure ba Tahir ya fara gaya musu, saboda ko
girki Farida bata iya ba ko kichen bata shiga sai dai shi in ya dawo daga Office ya
zage ya shiga ya sama musu wani abun su ci, ko kuma in zai dawo yayi musu takeaway
baima wahalar da bakinsa ganin bata iya ba balle tayi ganin haka yasa tama Umma
magana ta kawo mata 'yar aiki itama basu daidaita ba watanta biyu ta ƙara gaba
saboda halin Farida na faɗa komai aka mata ba'a mata daidai ba, watansu huɗu da
aure akayi posting ɗinsu zuwa service a kuma lokacin ne ciki ya ɓulla ajikin Farida
wacce ta dinga kuka wai zai hanata tafiya service Bauchi, abu har sai da iyaye suka
shigo ciki Abba ne da kanshi ya mata cuku cuku ta dawo Kaduna amma ba haka ranta
yaso ba ciki zai mata cikas wajen zuwa biki ko sha'anin kece raini amma bata da
yarda zatayi don Tahir ya kasa ya tsare kan cikin jikinta taga ainihin kalanshi
Sai da cikinta yayi wata goma cur kana ta haihu shima C.S aka mata aka ciro 'yan
biyu mace da namiji murna wajen Tahir ba'a magana, saboda shagwaɓan Farida da
sangarta sai dai Tahir ya barta aka tafi da ita Kano wajen Umma, ta kula da ita
yara kuma suka ci sunan Basma da Bassam, Farida bata dawo ba sai da ta kusa wata
uku kana ta dawo har su Basma sun fara wayau data dawo har da 'yan aikinta guda
biyu ɗaya ta kula dasu Basma ɗaya kuma tayi girki da gyaran gida, zamanta a Kaduna
yasa Farida tayi ƙawaye fita biki sai wanda bata jiba Tahir kuma haƙuri gareshi, ko
tayi wani abun bai cika mata magana ba saboda miskilancinsa, uwa uba kuma fifikon
soyayyarta azuciyar iyayenta da kuma damar da iyayensa ke ganin taimakon mahaifinta
gareshi karya wulaƙanta ta amma zamansu da Farida duka haƙuri yafi yawa a ciki.
Haka dai rayuwa ta cigaba da gangarawa da daɗi ba daɗi Tahir dai na haƙuri da halin
Farida rayuwarsu Basma da Bassam kuwa ta walagigi ce hannun 'yan aiki da kuma shi
saboda in ya dawo daga Office yana zama ya kula dasu Farida kuma bakin yawo ke
cinta daga yau tana wajen bikin ƙawarta sai gobe bikin ƙanwar ƙawarta gashi ita
kuma bata da sha'awar yin aiki amma kuma bata iya zama agida ita kenan yawon biki,
gashi shi mutum ne da bayason hayaniya da ɓacin rai ya kai ƙararta sau biyu wajen
su Abba amma ba wani chanji shiyasa ya kawo ido ya sakamata yana ƙoƙarin shanye
ɓacin ranshi akanta duk babu abunda zai ɗaurar na jin daɗin aure shi kam.
Matsala ta biyu kuma shine Farida tana daga cikin jerin matanan masu ƙarancin
sha'awa kuma basu ba hakan muhimmanci ba balle ta nemi magunguna ko na musulunci ne
saboda shi Tahir yana daga sahun maza mabuƙata, wani lokacin sai suyi sati biyu
Farida bata kalleshi ba in ko ya nemeta sai ranshi ya ɓaci ya rasa meke damunta
wani lokacin yana buƙatar saboda gudun ma kanshi ɓacin rai yake ƙoƙarin daurewa
shiyasa koda yaushe cikin yin azumi yake koda bana ranar Litinin da Alhamis ba.
Bayan haihuwar su Basma tayi family plaining ba tare da Tahir ya sani ba shiyasa
har su Basma suka kai shekara takwas bata ƙara haihuwa ba, tunda har sun shiga
makaranta Commond sch Kaduna, har tuhumarta ya taɓa yi ta turje tace batayi komai
ba taƙi gaya mai gaskiya haka da suka je Ɗanbatta Goggo Abu ke tambayanta Allah sa
ba ƙwayoyin zamani Tahir ɗin ya ɗorata akai ba tace ba komai. Da yake ba'a ma Allah
dubara cikin wannan tsukun ta samu cikin Naila wanda ya wahalar da ita shima C.S
aka mata tana haihuwarta Farida tayi alƙawarin ta gama haihuwa itama wannan
haihuwar gida ta koma, 'yan aikinta kuwa tuni ta sallamesu da zata dawo daga wankan
Naila ne ta dawo da Iya.
Tahir ya rasa shi wani irin ƙaddaran rayuwa ce ta faɗa mai yana ganin Ishaq da
matarsa Zahra gwanin ban sha'awa amma shi ƙarya ne ya dawo daga Office ya iske
Farida agida ko tana gida bashi da wani matsayin da zai shigo tazo ta mai sannu da
zuwa tayi kwalliya don ya gani yaji daɗi tana ciki tana waya da ƙawayenta ana tsara
yadda bikin ƙanwar wanche zai kasance kullum cikin yi mata nasiha da nusassheta
yake amma bataji saboda misalin dayake yawan mata da Zahra matar Ishaq ta yanke
alaƙa da ita bata wani sakarmata fuska sai itama Zahran taja baya da ita.
Goggo Abu ce kaɗai da ƙanwarsa Ashe suka san halin dayake ciki in ya gaya mata
sai ta bashi haƙuri ta kuma ce zatama Faridan magana toh ko Faridan taje garin in
Goggo Abu ta mata faɗa sai tace insha Allahu zata gyara kuma bata gyarawan kuma
Goggo Abu ta hanashi sanarma Hakimi wai kada ya zama sanadiyyar raba amintantakar
dake tsakanin Abba da Hakimi.
Mufeeda Kuma Tahir da kanshi ya ɗauko ta faga Ɗanbatta bisa umarnin Goggo Abu
bayan Ita Faridan da kanta ta Nemi Goggon data samo mata matashiyar yarinyar wacce
zata tayata kula da Naila amatsayin NANNY...."
*Aisha Alto.*
*Shakira.*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA HUDU*
*MALLAM BELLO GURGUN DANBATTA* Sunan mahaifin Mufeeda wanda shima ya kasance
haifaffan garin na Ɗanbatta ne gaba da baya, haka ma matarsa Inna Fulera itama
haihuwan nan ce kuma tashin nan.
Sai dai kuma tun asali dukkansu biyun sun fito daga tsatson talakawa ne futuk
marasa ƙarfi kuma dama auren zumunci ne tsakanin Bello da Fulera, bayan haka kuma
dangin nasu basu da yawa saura sun mutu sauran kuma sun lula garuruwa neman kuɗi.
Bello gurgun Ɗanbatta ya samo asali ne da tun yana yaro ciwon daji yakamashi ahannu
wanda yayi sanadiyar cire mai hannu guda ɗaya shikenan in za'a kirasa sai adinga
mai in kiya da Bello gurgun Ɗanbatta, daga Malam Bello har Inna Fulera duka sun
rasa iyayensu so suna zaune awani ƙuntataccen gidan ƙasa cikin matsi da wahalar
rayuwa, dukkansu babu wanda yayi ilimin boko sai na allo shima ɗin sama sama don
lokacin bawai sanin darajan abun sukayi ba, balle su damu dashi baida wata sana'a
sai sana'ar noma kayan lambu kamarsu tumatur dasu kabeji da albasa, yana shiga
cikin gari yana siyarwa da hannun nasa guda har su samu su rufama kansu asiri.
Sun shekara kusan goma da aure kafin Allah yabasu Mufeeda wanda bayan ita ta haifi
'yan biyu duka maza basu zo da rai ba daga lokacin kuma haihuwa ta tsayama Inna
Fulera sai suka cigaba da rainon Mufeeda wacce suka ɗauki son duniya suka ɗora mata
saboda ita kaɗai garesu itace 'yarsu kuma ahalinsu sannan abokiyar hirarsu shiyasa
itama Mufeeda ta taso cikin so da ƙaunar duka iyayen nata guda biyu, duk da tazo ta
iskesu cikin wahalan rayuwa amma suna iya bakin ƙoƙarinsu akanta don ita kanta Inna
Fulera bata zauna ba tana saida dafaffen kabeji acikin gida ana zuwa siya ba laifi
tunda tana da tsabta...
Haka suka cigaba da gangara rayuwarsu da daɗi ko ba daɗi har lokacin da Mufeeda
keda shekara goma sha uku a duniya ta girma duk wasu alamun budurci basu bayyanar
mata ba sakamakon siririyace ita bata da jiki sosai, kwatsam suka tashi da wani
rashi, rashi mai girma daya taɓa zuciyarsu wanda har yau suka kasa mantawa dashi na
rasuwar Bello Gurgu sanadiyar faɗawa rafi ruwa ya cinyesa Inna Fulera da Mufeeda
sunyi kuka kamar ransu zai fita, duk da a lokacin Mufeedan nada ƙarancin shekaru
amma wannan rashin da sukayi ya tsaya mata sosai a cikin ranta.
Ko takaba Inna Fulera bata fita ba suka fara shiga tasku da wahalar rayuwa na babu
sai su kwana basu ci ba, abun na damunta duba da ƙarancin shekarun ita Mufeedan
shiya sanya tana gama takaba labarin neman ma'aikata daga gidan Hakimi ya sameta
inda Tahir ya bada cigiyar neman waɗanda zasu dingama iyayensa hidima yana biyansu
duk wata Inna Fulera batayi ƙasa agwiwa ba ta isa gidan Hakimi gaban Goggo Abu sai
dai koda taje an riga angama ɗaukan adadin ma'aikatan, nan Inna Fulera ta faɗi
gaban Goggo Abu tana kuka tana roƙonta data rufa mata asiri ta taimaki rayuwarta
data marainiyar Allah Mufeeda toh a lokacin sai taausayin ƙarancin shekarun Mufeeda
ya ɗarsu a zuciyar Goggo Abu har yayi sanadiyar data ɗauki Inna Fulera amatsayin
hadimarta amma in tagama da shashenta takan shiga madafi ta taimaka duk wata 15k
Tahir ke biyansu dukkansu wanda cikin lokaci kaɗan ya taimaki rayuwar mutane dadama
ciki harda Inna Fulera wanda cikin haka ne ta sanya Mufeeda a makarantar Primary
Ɗanbatta tana zuwa idan ta taso sai ta biyo gidan Hakimi wajen Innarta taci abinci
ta ƙoshi ba shashen datake zuwa sai shashen Goggo Abu ta zauna tayi shuru dake bata
da yawan magana wani lokacin in Goggo Abu ta ganta sai Tahir ya faɗo mata acikin
ranta tana tunanin shigen miskilancinsa amma in ta kalli yanayin Mufeeda sai taga
ta shanyeshi haka kurum take jin tausayin yarinyar shiyasa take janta ajiki sosai.
Mufeeda bata da wata ƙawa agarin sai Lantana wacce maƙotansu ne itama Mamarta tana
aiki agidan Hakimi ita kaɗai ce ƙawarta kuma gashi makarantarsu ɗaya kuma ajinsu
ɗaya, shiyasa sai tasu tazo ɗaya kuma in sun tashi daga makaranta tare suke wutowa
gidan Hakimi wajen iyayensu, Mufeeda bata da saurayi kamar na sauran 'yanmatan
ƙauye ko nace bata bi ta kansu kwata kwata saboda ita bata son auren wurin da'ake
musu mutum ɗaya ne take kulawa shima sai ya dameta Iliya mai rake, tun tana
ƙaramarta yake bibiyarta abokin saurayin da Lantana zata aura ne Murtala shiyasa
wani lokacin in sun biyo hanyar makarantar allo in Murtala yaja Lantana gefe itama
sai Iliya ya jata duk dai bata sakarmai fuska bai damu ba saboda yaci ace ya saba
da yanayin rayuwar Mufeeda.
Inna Fulera bata rufe shekara da samun aiki agidan Hakimi ba Farida tazo garin
inda ta samu Goggo da shawaran tana buƙatar a nema mata wata yar yarinya wacce zata
tafi da ita amatsayin Nanny saboda kula da Naila sai su dinga biyanta duk wata suna
aikoma da iyayenta tunda ta lura duk waɗanda Umma ke samo mata daga Kano ita basu
mata, Goggo Abu na jin haka sai Mufeeda ta faɗo mata arai amma sai ta fara tunanin
kamar ba zata iya ba, ilai ko Faridan na ganin Mufeedan tace ko itama aka bata ta
isa, Goggo Abu bata yanke hukunci ba sai da ta nemi shawaran Hakimi da Innaro suka
kuma bada goyon baya Duk Da Tahir ɗansu ne amma suna da kyakkyawan sheida akanshi
shi da matarshi basu wulaƙanta mutane...
Cike da ƙwarin gwiwa Goggo Abu tasa aka mata kiran Inna Fulera ta labarta mata
muradinta azahirin gaskiya taji firgicin maganar duba da Mufeedan kaɗai gareta kuma
ta ƙwallafa rai da ita amma kuma Goggo Abu bazata nemi alfarma taƙi mata ba, bata
da yarda zatayi ta amince amma zuciyarta ba daɗi duk da ko ta tabbatar Mufeeda zata
samu ingantacciyar rayuwa agidan Tahir, amincewar Inna Fulera ya sanyayama Goggo
Abu rai nan ta mata alƙawarin insha Allahu bazatayi nadama ba, Farida ta koma bayan
ta bar sallahun Mufeeda ta shirya sati mai zuwa direba zai zo ya ɗauketa.
Inna Fulera data koma gida tayi kuka sosai kuma bata iya sanarma da Mufeeda ba,
fahimtar haka yasa Goggo Abu ta saka Inna Fuleran ta turo mata Mufeedan ta sanar da
ita, wayyo gwanin ban tausayi duk da ta kasance mai rauni wajen kazar kazar ɗin
rayuwa amma kukanta ya kasa ɓoyuwa tana kiran ita bazata bar Innarta ba Goggo Abu
ke ta lallashinta amma taƙi yin shiru ƙarshenta ma ta tashi da gudu ta fita sai
gida chan taje ta sakama Inna Fulera kukan ba inda zata tafi ta barta, kwana tayi
lallashinta da bata baki amma Mufeeda taƙi yarda.
Sati kuma na cika sai ga Tahir yazo garin Garzali ya kawoshi kuma shi Farida bata
sanar dashi komai ba, Goggo Abu kuma tana ganin haka sai ta zata ya sani ne shine
yazo tafiya da Mufeedan nan da nan tasa aka kiramata Inna Fulera tace tayi maza
taje ta shiryo Mufeeda da kayanta ga Attahiru nan yazo tafiya da ita Kaduna, Allah
sarki raba uwa da 'ya sai Allah da kuka da komai Inna Fulera ta kawo Mufeeda gidan
Hakimi sai lokacin ma Tahir yasan da maganar bai wani damu ba sanin dama Farida
bata ɗaukeshi bakin komai ba, abun kuma yayi mai daɗi ko banza yana daraja garin
haihuwarsa haka Mufeeda ke kuka Inna Fulera nayi taƙi shiga mota ta ƙanƙameta
Innarta tana wani kuka mai ban tausayi tare da ƙawarta Lantana, har sai da Hakimi
yace a haƙura da tafiya da Mufeedan asamu wata saboda yadda daga Mufeedan har Inna
Fuleran suka bashi tausayi haka shima Tahir wanda da kanshi yaje ya riƙo hannun
Mufeeda yana kallonta ƙwarjininsa ya hanata yi mishi gardama gaban Inna Fulera ya
duƙa yana ƙara jaddadamata insha Allahu zai kular mata da Mufeeda kamar 'yar da ya
haifa kuma alƙawari ne yayi mata zai dinga kawo Mufeeda lokaci bayan lokaci tana
zuwa ganinta, wannan kalaman nashi su suka sanyaya ran Inna Fulera da kanshi ya
saka Mufeeda cikin mota da ƙullin kayanta wanda ƙwarjininsa da kimarsa yasa ta kasa
mishi gardama amma har motarsu ta ɗaga daga ƙofar gidan Hakimi Mufeeda na kuka tana
ɗagama Inna Fulera hannu itama tana kuka tana ɗagamata Iliya ma yana laɓe daga chan
yana leƙen tafiyar Mufeedan sai da ya share ƙwallah saboda an rabashi da
masoyiyarsa zuwa birni shima Murtalan Lantana ke gaya mai..
Koda Farida taga Tahir da Mufeeda bata damu ba dama tunda yace yau zashi Ɗanbatta
ta sani Goggo Abu zata bada Mufeeda azo mata da ita shiyasa bata damu ba, lokacin
da Mufeeda ta tsinci kanta agidan Tahir ta sani ta shiga wata sabuwar rayuwa na
bambamcin komai kama daga wayewa da garin ma gaba ɗaya, da farko bata iya sakin
jiki ba duk da ko ɗakinta ita kaɗai Farida ta bata bayan ta miƙa mata amanar Naila
wacce lokaci ɗaya yarinyar ta shiga ranta abunda ya ƙara sanyayamata rai shine
yadda ko su Basma basu nuna mata bambamci duka ɗaya suke ga Iya itama tana mata
kyakyawan mu'amala ta ɗauketa kamar 'yar data haifa da cikinta, balle Farida da
bakomai take bama muhimmanci ba, kuma ance mai ɗa wawa balle data lura yadda Naila
ke samun kulawa sosai wajen Mufeeda cikin lokaci kaɗan tayi kiɓa ta chanza shiyasa
komai nata na ɗakin Mufeedan awajenta yake kwana in ba Tahir bane ya matsa ta
ɗaukota nono kuma in tana nan ne take bata in ko bata nan sai dai ta wuni shan
madaran ruwa.
Farida bata da matsala ta ɓangaren ƙyashi ko wulaƙanta mutane ta fito daga gidan
arziki shiyasa Allah bai ɗora mata wannan ƙyashin ba, komai zatama Basma da Bassam
sai ta haɗa da Mufeeda da Iya haka ma Tahir baya nuna bambamci akan komai abinci
tare suke ci, tun Mufeeda na ɗari ɗari har ta saki jiki ta saba, kuma duk wata
Tahir na turama Inna Fulera 20k da farko cewa tayi bazata karɓa ba yayi yawa sai da
Goggo Abu ta matsa mata.
Watanta uku da zuwa Farida tabama Tahir shawaran asanya Mufeeda a makaranta nan da
nan ko ya yarda da shawaranta shima abun na ranshi cikin sati ɗaya cike cikenta ya
tabbata ta samu gurbin karatu a Model School Kaduna inda ta fara daga Js1 duk da
tana Primary 4 ta tsaya lamarin dayama Mufeeda daɗi sai da tayi kuka da farko ta
fara samun matsala ta ɓangaren wayewa da kuma turanci, sai kuma Tahir ya sama musu
Lesson Teacher ita dasu Basma yana koya musu suma kuma suna ƙoƙarin koya mata
abunda bata gane ba tunda suma Js1 ɗin suke sai dai su Commond School sukeyi sai an
kaisu kana direba ya wuce da ita in ta tafi makaranta sai Iya ta karɓi kula da
Naila wacce tasha kuka kafin ta saba da rashin Mufeeda kafin ta dawo makaranta ta
gaji da kuka ta haƙura.
Sai da suka samu hutun farko kana ta roƙi Tahir wanda take cema Daddy don
amatsayin uba ta ɗaukesa zata je Ɗanbatta direba ya kaita ta kwana biyar ta dawo
saboda Naila, zuwan daya yima Inna Fulera dad'i haka suka ƙanƙame juna Lantana da
wasu mutanen gari basu iya gane Mufeeda ba saboda yarda ta zama 'yar gayu tayi kyau
kamar ba ita ba, hakama Iliya daya ganta sai da hankalinshi ya tashi na ganin
tabbas Mufeeda tafi ƙarfinsa koda ta koma bikin Lantana ya kusa, bata saran zuwa ba
amma data roƙi Mami Farida ta roƙar mata Daddy sai gashi ya barta taje ta kwana
ɗaya ta dawo zuwan daya sanya ta zama zara cikin wata saboda kyanta da kuma ilimi
da wayewar data samu tare da cigaban rayuwa.
Matsalar Farida da Tahir ta fara girma tunda yanzu sai ta shafe wata da watanni
bata bashi hakkinshi ba, kuma shi ba dutse bane yana buƙatar wajen ɗebe kewa da
damuwa, amma sam Farida hakan baya gabanta in ya nemeta tayi ra'ayi to laba'asa ne
da komai ya kammala shikenan ko ajikinta, abun na damunshi kullum cikin azumi yake
gashi bata zama agida abun haushi yawon gidajen ƙawaye in Farida taji biki jikinta
na rawa tun ada yana ɗauka yarinta ne in taƙara girma zata bari amma ina ko raguwa
baiyi ba, su Abba ko ya gaya musu suka mata faɗa zata nuna taji amma kuma ta bayan
kunnanta yake wucewa haka Goggo Abu wacce ke tausanshi kada ya sanarma Hakimi halin
dayake ciki, maganar ƙarin aure kuma ba ra'ayinshi bane tunda shi mutum ne mara son
hayaniya gashi kuma da haƙuri amma ƙanwarsa Ashe ce ta bashi shawaran ya ƙara aure
ya bar Faridan ita taje chan ta ƙarata da halinta tun bai yarda da shawaranta ba
har ya fara tunanin shine mafita toh Goggo Abu ce ta takamai burki sau uku kenan
yana zuwar mata da maganar tana dakatar dashi, saboda dalilinta na kada azo ayi
abunda zai lalata zumuncinsu, abun na damun Tahir amma haƙurinsa da kuma kawaicinsa
yasa ba'a gane halin dayake ciki banda abokinshi kuma amininshi Ishaq.
Wannan kenan.
******
*Kano*
_Tarauni Gra_
Ƙudundune take a cikin lallausan bargo tana sharar barcinta hankalinta kwance Umma
ce ta shigo cikin bedroom ɗin tana bin Faridan da kallo lokaci ɗaya tana duba
agogon bangon daya ƙawata bedroom d'in ƙarfe 12 daidai kai ta girgiza kafin ta
ƙarasa kusa da Farida gefenta ta zauna tana ƙara gyara zaman doguwar rigar leshin
dake jikinta matashiyar dattijuwa ce fara mai yalwar fara'a kallo ɗaya zaka mata ka
fahimci hutu da jin daɗi sun zauna mata fuskarta kuwa ɗauke da kwalliyarta don
Hajiya Aliya bata yarda da zama haka ko kuma girma ya cuceta ba a'a tafi kowa kula
da mijinta da tattalinshi, inda ace Farida tana lura da yanayin rayuwar iyayen nata
da har abada Tahir bai taɓa complain akanta ba.
Bargon ta yaye kafin ta fara buga ƙafarta tana faɗin "Farida...Ke Farida..." Miƙa
tayi tana wani ƙara narkewa bargon take ƙoƙarin ƙara ja, da sauri Umma ta fizge
tana faɗin "Wai miye haka..? Tun jiya da kika iso kike kwance kina wannan barcin,
bazaki tashi kiyi ƙoƙarin komawa gidanki ba baki tunanin wani hali mijinki ke ciki
da 'ya'yanki balle ma ki riƙa tuna ƙaramarsu Naila mai shan nono..."
Ta fada cikin damuwa, miƙa Farida tayi tana turo baki kafin ta miƙe da ƙyar tana
gyara gashin kanta wanda duk ya baje saboda barci, fuska ta yamutsa kafin tace "Toh
Umma me zai samesu..? Lafiyansu ƙalau su fa, Basma ba yara bane, Tahir ma haka
Naila kuma Mufeeda na kula da ita, in ma ta tafi makaranta iya na gida zata kula da
ita.." Ta faɗa tana zuro ƙafarta ƙasa, kallonta Umma tayi kafin ta dafa kafaɗarta
tana faɗin "Toh naji tashi dai ki yi wanka ki shirya ki fito ki karya ki yi haraman
tafiya kinji Faridata..?" Ta faɗa da sigar lallashi da lalama, miƙewa Farida tayi
bayan ta zura wani takalmi mai taushi tace "Umma ina Abba..?
Miƙewa itama tayi tana faɗin "Abbanki ya fita tun safe yana da baƙi, amma ya bar
sallahu direba ya tuƙa ki zuwa Kaduna yace bayason kina doguwar tafiya ke kaɗai.."
Murmushi ta saki kafin tace "Abbana kenan toh me zai sameni nifa ko achan Kaduna
Tahir baya tuƙani duk inda zani da motata nake zuwa har Ɗanbatta in kinga direba ya
tuƙamu tare ƙila tafiyar tazo ɗaya ne.." Murmushi Umma tayi kafin tace "Hakane, toh
kindai ji sakonsa ko..? Toh kiyi maza ki shirya ki fito.." ta faɗa tana kama hanyar
ficewa, ƙara tura baki Farida tayi kafin tace "Kai Umma sai wani koro na kikeyi.."
Ta faɗa tana tura ƙofar toilet Umma bata ba zancenta muhimmamci ba tace "Eh saboda
baki da gatan daya wuce gidan mijinki da 'ya'yanki.." Faridar na jinta daga bayi
sai ma ta kyaɓe baki don ita basu dameta ba gani take da ƙafarsu da lafiyansu sai
ta zauna ta ƙoƙarin ƙare rayuwarta akansu.
Sai da Farida ta shafe wajen awa ɗaya kana ta fito daga cikin bedroom ɗinta na
gidan iyayenta, sanye da wata irin shadda Gezner mai ruwan brown ɗinkin doguwar
riga, sai ɗaurin Maryam Babangida data cukashi, fuskarta ba kwalliya amma kuma
kallon farko zaka mata ka fahimci bata da wata damuwa, vail ne yafe akanta sai
ƙaramar jakarta Umma ta tarar akan dining tana breakfast cikin yanga ta ƙarasa
itama taja kujera ta zauna tea kad'ai tasha sai ferfesun kayan cikin ta miƙe tana
share bakinta da tissue, kallonta Umma tayi kafin tace "Don Allah Farida ki dinga
zama agidanki ba don niba sai don ki girmama darajan aure ki kuma girmama haƙurin
mijinki akanki plz.."
Rausayar dakai tayi kafin tace "Umma kenan Tahir ya gama shanye ku kuma, kamar
yadda ya gama da iyayenshi, shikenan kuma ni ban san ciwon kaina ba Umma nafa girma
nima daidai gwargwado na mallaki hankalin kaina ai nasan me nakeyi, bikin fa ƙanwar
Beauty akayi fa Umma kuma kinsan yadda muke da Beauty tun muna makaranta, kawai
shegen ƙorafin shi ne yayi yawa..." Ta faɗa tana ɓata fuska kafin ta wuce ta koma
cikin bedroom ɗinta ta ɗauko ƙaramar trolley ɗinta ta fito tana faɗin "Umma zan
tafi sai munyi waya.."
Umma ta bita har waje inda direba ke jiranta trolley d'in direban ya karɓa ya
saka cikin wata baƙar Venz ɗin Farida, kafin ya buɗe mata gidan baya sai da ta
shiga kana ta leƙa tana fadin "Umma zan bashi kuɗi ya shiga motar haya in mun isa,
ki gaida Abba..." Kai Umma ta gyada tana faɗin "Allah ya kiyaye hanya kar dai naji
kin sake fita har zuwa nan da sati biyu Allah kuwa.." Dariya Farida ta saki har
haƙorin Makkanta sai da ya bayyana kallonta Umma tayi kafin tace "Kinji ni ko baki
ji ba..?"
Kai ta gyaɗa kawai batayi magana ba amma acikin ranta tana tunanin irin shagalin
da suke dashi ranar sati anan Kaduna, ƙanin Bilkisu zai yi aure dole suje su
raƙashe, har motarsu ta fice daga haraban gidan Umma na ɗaga musu hannu ita kuma
Farida sai ta ƙara gyara zama ta jingina kanta jikin kujera ta fito da wayarta ta
fara latsawa tana sakin murmushi lokacin data shiga WattsApp, inda taga group ɗinsu
na Classes Bbys na waɗanɗa sukayi makaranta tare ya cika da massagea tasan ƙila
maganar yadda bikin ƙanin Bilkisu zai gudana ne jiki na rawa ta shiga ta fara bin
Chat ɗin cike da farin ciki.
*Aisha Alto*
*Shakira*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman: *
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR (Janafty*💕
*BABI NA BIYAR*
Ƙarfe 3:30pm. Suka shigo garin Kaduna direct suka nufi Unguwar Rimi GRA suna zuwa
maigadi ya buɗe tangamemen gate ɗin gidan direba ya sulala motar ciki ya yi parking
ya fito da sauri ya buɗewa Farida ta ziro ƙafafuwanta waje sannan ta fito riƙe da
wayarta da ƙaramar jaka a hannunta ta buɗe jakar ta ɗebo kuɗi ta miƙa masa "Gashi
kaje tasha ka shiga motar haya ka koma gida. Allah ya tsare." Cike da ladabi ya
karɓa yana mata godiya, hannu kawai ta ɗaga masa ta juya ta ɗauki ɗan ƙaramin
akwatinta ta shige cikin gidan, direban ya juya shima ya fice daga gidan.
Falon tsit yake babu kowa a ciki da alamu yara basu riga sun dawo daga makaranta
ba, a gajiye take dan haka bata bi takan komai ba ta nufi ɗakinta, tana gab da
shiga ɗakinta ta tsinkayo muryar Iya cike da murna tana faɗin "Sannu da zuwa
Hajiya, ashe kece? Ina kichin zan haɗawa Naila madararta na jiyo motsin
shigowa..sannu da dawowa." Iya ta faɗa fuskarta cike da fara'a tana tahowa inda
Farida take tsaye da Naila riƙe a hannunta tana murmushi.
Murmushin itama Faridan tayi ta aje ɗan akwatin hannunta ta miƙa hannu ta karɓi
Naila ta ɗagata sama ta sumbaci goshinta ta shafa kanta sannan ta miƙawa Iya ita ta
ɗauki akwatinta tace "Sannunku da gida Iya." Ta faɗa kawai tare da shigewa ɗakinta,
turus iya ta tsaya tana bin bayanta da kallo kafin ta girgiza kai kawai ta juya ta
koma kichin dan cigaba da abinda take yi, dan in dai halin Farida ne na nuna halin
ko in kula da 'ya'yanta da duk wani abun daya shafi gidan aurenta yaci ace zuwa
yanzu duk sun saba dashi, bai kamata a kullum ya zama wani sabon abu ko baƙon abu a
gurinsu ba.
Kwana da kwanaki bata gida bata tare da 'ya'yanta da mijinta ga yarinya ƙarama mai
shan nono wacce ko yayeta bata yi ba amma ta dawo ko ta tsaya ta tambayi yanda suke
balle ta ji ina suke da bata samesu a gida ba, gashi ko ƙaramar 'yarta mai shan
nonon ma bata wani damu da ita ba ko ta nuna kulawarta a kanta ba, shiyasa itama
'yar ko murna da ganin uwar tata bata yi ba sai kallonta kawai da take kamar wata
baƙuwa.
Tana shiga bedroom ɗinta ta zube wayarta da jakarta ta tuɓe kayan jikinta ta jawo
tawul ta ɗaura ta faɗa toilet, bata wani daɗe sosai ba ta watsa ruwa ta fito ta
faɗa gado tai kwanciyarta abinta saboda wani irin bacci take ji duk ta gaji jikinta
sai ciwo yake mata.
Ƙarfe 4pm. Bassam da Basma suka dawo daga makaranta, suna shigowa suka tarda Iya na
bawa Naila madara a falo a gajiye duk suka zube saman kujera suna maida numfashi,
Iya ta ɗago tana kallonsu da murmushi akan fuskarta tace "Sannunku da dawowa ya
makarantan?" Basma na turo baki tace "Ba daɗi Iya, yau munsha wuya ga rana ga
zafi." Dariya Iya tayi tana kallonta tace "To Mummy dai ta dawo..." Da murna duk
suka miƙe suka kwasa da gudu suka nufi ɗakinta tana kwance suka shigo cike da farin
cikin ganin mahaifiyarsu suka faɗa kanta da gudu suna murna suke faɗin "Oyoyo
Mummy..!"
haɗe rai tayi ta yatsine fuskarta ta tashi zaune haɗe da janyesu a jikinta ta ɗaure
fuska tace "Please kuje waje ina so zan huta ne, idan na tashi zan nemeku.." ta
faɗa tare da janye hannunta ana Basma tana nuna musu ƙofar fita, a sanyaye yaran ke
kallonta kafin su juya a hankali suka fice daga ɗakin suna waigenta, ƙaramin tsaki
taja ba tare da tunanin komai ba ta gyara kwanciyarta abinta ta lumshe idonta tana
jira bacci ya ɗauketa.
Yanda Iya taga sun fito daga ɗakin jikinsu a sanyaye yasa ta miƙe da Naila dake
bacci a hannunta ta nufesu ta kamo hannun Basma tana ɗan murmushi tace "Kuje ku
cire kayan makarantan kuyi wanka sai ku fito ku ci abinci, kafin nan Mufeeda ta
dawo itama sai ku shirya ku wuce islamiyya.." gyaɗa mata kai suka yi kafin kowa ya
nufi ɗakinsa, itama ta juya ta nufi ɗakin Mufeeda ta kwantar da Naila ta fito.
Sai da sukayi wanka sukayi sallar La'asar sannan suka fito falo cikin shirinsu na
tafiya islamiyya, lokacin itama Mufeeda ta dawo har tayi wanka ta saka uniform irin
nasu tayi shirin islamiyya.
A dinning suka haɗu suka ci abinci kafin da suka gama suka ɗauki jakunkunansu suka
fice Garzali ya kwashesu zuwa islamiyya.
Ƙarfe 6:20pm. Suka dawo suna shiga falon kowa ya nufi hanyar ɗakinsa.
Suna shiga falon motar Tahir na shigowa cikin gidan dawowarsa kenan, bayan yayi
parking ya buɗe motar ya ɗauki wayoyinsa da rigar suit ɗinsa daya cire ta saman
yabar ta cikin a jikinsa ya kulle motar ya nufi cikin gidan da takunsa mai cike da
kuzari da izza ya shiga falon da sallama, da gudu Basma da Bassam da suka buɗe
ɗakunansu zasu shiga suka rugo gurinsa suka faɗa jikinsa tare da ƙanƙamesa suna
masa barka da zuwa, yana murmushi ya riƙe hannun Basma yayinda shi kuma Bassam ya
karɓi rigarsa da makullin mota ya riƙe fuskarsa cike da fara'a da murna yace "Daddy
Mummy ta dawo tana ɗakinta.." ɗif Tahir yayi ya gimtse fuskarsa yay kamar baiji
abunda Bassam yake cewa ba, kallon juna suka yi da Basma kafin Bassam ya ƙara
kallonsa yace "Daddy Mummy fa ta dawo.." karɓar rigarsa da makullin motarsa kawai
yayi a hannunsa yace "Maza kuje ɗaki ku cire uniform ku canza kaya, sai kuyi alwala
ka fito muje masallaci an kusa kiran sallah." Yana faɗa ya saki hannun Basma suka
nufi ɗakunansu shima ya juya ya nufi bedroom ɗinsa yana jin wani takaici da ɓacin
rai a zuciyarsa.
Yana shiga ya tuɓe kayan jikinsa ya shige toilet a gurguje ya watso ruwa ya haɗo da
alwala ya fito ya zira jallabiya ya fesa turare ya ɗauki casbaha ya fice daga ɗakin
yana fita ya samu Bassam da Mufeeda zaune a falo, tana ganinsa ta miƙe ta ɗan
rusuna ta gaishesa ya amsa yana kallonta kafin ya kama hannun Bassam suka fice zuwa
masallaci itama Mufeeda ta nufi ɗakinta don gabatar da sallar Magriba da ake kira.
Basu dawo ba sai da suka sallaci sallar Isha'i kana wajen after 8 suka shigo
gidan, suna shigowa suka iske Mufeeda da Basma suna taya Iya jera warmers akan
dinining, kallo ɗaya yayi musu sanda Mufeeda da Basma suke mishi sannu da suwa kai
ya gyaɗa ba tare da yayi magana ba ya fara haura step Mufeeda ta bishi da kallo
asace tana so ta karanci yanayinsa, karaf ya waigo suka haɗa ido gabanta ne ya faɗi
tayi saurin sadda kai jikinta ya fara rawa ganin yadda ya sakar mata ido Basma ce
ta lura da tsayuwarshi idonshi na kallon Mufeeda amma bai bari kowa ya fahimta ba
cikin kulawa Basma tace "Daddy plz kai da Momy ku fito muyi taking dinner tare
tunda all of u yau kuna gida.."
Bassam dake zaune kan ɗaya daga cikin kujerun falon tun bayan shigowarsu shida
Tahir yace "Eh mana Daddy plz...We miss u.." Ya faɗa cikin muryan taausayi wani
haushin Farida ya ƙara kamasa, amma bai nuna ba sai ma ya murmusa yana fadin "Mufee
Naila tayi barci ne...?" Kanta na ƙasa tace "Eh Daddy tun ɗazu dana bata madararta
na goyata tayi barci.." Gyaɗa kai yayi kafin ya juya yana faɗin "Gud.." Bai ko ƙara
kallon su Basma ba waɗanda suka sakamai ido ganin yana neman haurawa sama ne yasa
Basma ta ɗaga murya tana faɗin "Daddy...." Juyowa yayi cike da wani fushi yana
kallonta baya taja ganin yadda fuskarsa ta chanza cikin rawar murya tace "Am Sorry
Daddy...I didn't mean to hurt u..." Ta faɗa kamar zatayi kuka Mufeeda ma dake gefe
yanayin Tahir ɗin yasakata sanyin jiki balle Bassam dayayi tsam a saman kujera yana
bin Daddynsu da kallo a tsume.
Ganin yadda duk sukayi ne yasa tausayinsu ya kamashi sai ya ƙaƙalo murmushin dole
yana faɗin "It's Ok, don't worry kuyi taking dinner ɗinku me am ok, na biya wajen
Ishaq naci abinci ok..?" A sanyaye Basma ta ɗaga kai kafin tace "What abount
Momy...?" Atsume ya kalleta kafin ya bi ƙofar bedroom ɗin Faridan da kallo daga
inda yake yana jiyo sautin dariyarta da alamu waya take bai bama takaichinsa
muhimmanci ba yace akausashe "Basma kuje kuci abincinku ku shiga ciki ku kwanta u
know tomorrow akwai school ko..?" Gyaɗa kai tayi kafin yace "Oya bana son wata
magana kuma, ita Momyntaku ai ta fiku sanin cikinta in tana buƙata zata fito taci,
saboda haka kuci abincinku kowannenku ya tafi ɗakinsa ya kwanta and don't forget
kowannenku yayi Assigment ɗinsa Basma Bassam Mufeeda am i clear..?" Ya faɗa cikin
bada umarni.
Gaba ɗayansu suka amsa da yes Daddy, gyaɗa kai yayi kafin ya juya ya ƙarashe hayewa
steps d'in ko kallon ɗakin Farida baiyi ba ya tura ƙofar ɗakinshi ya shiga yana
sakin siririyar ajiyar zuciya yana ƙoƙarin danne fushinsa yana ƙara tunanin wani
irin raini Farida tamai da zata fi kwana biyar bata gida kuma ta dawo gidan
bayanan, bayan ya dawo kuma ta kasa fitowa ko sannu da zuwa tamai alhalin yasan ta
ji dawowarshi? Tsaki yaja yana ƙoƙarin zama gefen gadonshi lokaci ɗaya zuciyarsa na
zafi duk da haƙurinsa wannan karon Farida ta ƙureshi, bai ƙara ƙoƙarin saka ɓacin
ranta a cikin ranshi ba ya cire jallabiyar jikinsa ya haye gadonsa daga shi sai
dogon wando baƙi duka zatinsa da kwantaccen baƙin gashin ƙirjinsa ya bayyana
ƙaramin Qur'aninsa ya ɗauka ya buɗe ya fara karantawa cikin natsuwa lokaci ɗaya ya
nemi ɓacin ran Farida ya rasa duk ya gushe acikin ranshi, a hankali ya cigaba da
karatunsa cikin jin daɗi da shaukin abun.
*****
Washegari ƙarfe 7 da wani abu Tahir ya fito daga ɗakinshi cikin shirin fita yau ɗin
shigar manyan kaya yayi saboda juma'a ce, wata farar Gezner ce mai maiƙo da yarari
ajikinsa ɗinkin matasa ne da samari masu jin kansu wato ɗinkin Muhammed, kansa
sanye da hula Zanna Bukar mai kalar blue irin aikin jikin shaddar sai agogon fatar
dake hannunsa na kamfanin Rado ne, ƙafarsa sanye da buɗaɗɗen takalmi na fatar
damisa.
A kallon farko in kamai zaka fahimci tsantsar zatinsa da haibarsa uwa uba kyau da
nasaba ga ƙwarjini, fuskarsa na fitar da annuri amma kuma zuciyarsa tana ɓoye ɓacin
ransa daidai lokacin daya fito yana ƙoƙarin gyara zaman hulan kansa sai ga Farida
itama ta fito daga cikin bedroom ɗinta suka kusa bangazan juna shi yana sauri ya
sauka ƙasa zashi Office suna da baƙi daga Lagos ita kuma ta fito sanye da wata
doguwar riga ƙirar Armani baƙa sai wani jan vail data naɗa akanta hankalinta na kan
wayarta amma kuma ƙamshin turaranshi shiya sanar da ita Tahir is here.
Cak ta tsaya tana binshi da kallo, shima kallonta yayi amma kallo ɗaya yayi mata ya
ɗauke kai lokaci ɗaya yana ƙara haɗe ransa itama sai ta kauda kai tana wani basarwa
saboda kada ya kawo mata wata mgana cikin dakewa ta furta "Good morning Abban
Basma.." Kamar bazai yi magana ba sai da ya raɓata ya fara saukowa daga steps kafin
ya amsa da cewa "Morning..." Daga haka bai ƙara mata magana ba ya sauko falo da
hanzari inda Mufeeda da Basma da Bassam ke zaune kowanne da uniform ajikinsa suna
karyawa, suna ganinshi dukkansu suka miƙe suna faɗin "Good morning Daddy..." Yana
sakin murmushi ya ƙaraso yana dafa kan Basma da Bassam harda Mufeedan kafin yace
"Morning how are u...?" A tare suka amsa da "We are fine Daddy.."
Fuskarsa na kallon Mufeeda yace "Mufee ya kwanan Naila..?" Tana wasa da gefen
hijabinta tace "Ta koma barci Daddy tana tare da Iya.." Gyaɗa kai yayi daidai
lokacin da Farida ta ƙaraso falon shi kuma ya juya yana faɗin "Bassam hau sama ka
ɗaukomin briefcase ɗina, idan kun shirya kuzo mu ajiyeku kafin mu wuce in kuma yaje
ya kaini ne ya dawo toh.." Da sauri Bassam ya miƙe yana faɗin "No Daddy zamu
bika.." Ya faɗa yana isa gaban Farida kafin ya ranƙwafa yana gaisheta ta amsa tana
shafa kanshi kafin ya nufi upstairs da sauri hakama Basma ta taso ta rungume Farida
tana gaisheta Mufeeda dai sai da ta koma ɗaki ta ɗauko ƙatuwar jakarta ta fito kana
ta durƙusa tana gaida Farida ta amsa ba yabo ba fallasa Tahir na gefe hannunsa na
harɗe kan ƙirjinsa yana kallonta cike da mamaki tana ɗagowa suka haɗa ido sai ta
wani ƙara haɗe rai kafin ta koma kan ɗaya daga cikin kujerun falon ta zauna tana
wani tamke fuska.
Takaichinta yasa ya fice daga falon har yana jan siririn tsaki da kallo ta bishi
kafin tace a fili.. "Fitinanne, nema na kake da fitinarka niko bazan biye maka
ba.." Tsaki taja daidai lokacin dasu Bassam ya ƙaraso ɗakinsa ya koma shima ya
ɗauko jakarsa suka fito Basma ta rigasu ficewa kafin Mufeeda da Bassam su fice suna
ma Faridan sallama ko ɗaga kai batayi ba hannu kawai ta daga musu.
Sai da aka fara kaisu Basma School ɗinsu kafin akai Mufeeda har suka ajiyeta tana
satan kallon Tahir tausayinshi na ratsata domin agabanta Farida ta faɗi maganar
ɗazu ranta bai mata daɗi ba duk da ƙarancin shekarunta tasan hakan bai dace ba,
ranar dukuku ta isa ajinsu duk zuciyarta da ranta ba daɗi Tahir ke cikin ranta tana
matuƙar tausayama rayuwar mutum mai nagarta da kamala kamarshi.
*Aisha Alto*
*Anitha..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA SHIDDA*
......Har ya isa Office fuskarshi ba annuri, har suka gama sallamar baƙinsu waɗanda
abokan harkarsu ne daga Lagos, office d'in Ishaq suka wuce suna cigaba da tattauna
abunda ya shafi kasuwancinsu, suna shiga Tahir ya nufi ɗan ƙaramin fridge d'in dake
Office d'in ya buɗe ya ɗauko musu ruwa guda ɗaya bayan ya ɗauko wasu ƙananan kofuna
guda biyu kai tsaye bisa kujeran dake fuskartar wacce Ishaq ya zauna shima ya zauna
ya ajiye kofunan bisa teburin dake gabansa batare da yace komai ba ya tsiyayama
Ishaq ya miƙa mai ya karɓa da murmushi kafin yace "Thanks."
Bai yi magana ba illah murmusawa kawai da yayi kafin shima ya tsiyayama kanshi ya
kafa kai yana sha, dukkansu atare ko wannen su ya ajiye kofin ruwan kuma suka
sakarma juna murmushi alokaci ɗaya, ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana wani lumshe
ido kansa ya jingina jikin kujera yana ƙara takure fuska kafin ya sanya hannu yana
taɓa naman goshinsa daya tattare, Ishaq na lura dashi ganin yadda yake yamutsa
fuskane yasa ya gane akwai matsala sosai.
Gyara zama yayi kafin yace "Uhm..Tahir meke damunka ne..? Tun shigowarka Company na
lura baka cikin walwalarka..?" Bai ɗago ba illah sauke hannunshi dayayi yana ƙara
lumshe dara daran idanuwansa har Ishaq ya fidda rai da zai yi magana sai chan yaji
ya furta.."Kai ma da neman magana kake, a duk duniya ni Tahir ina da wata damuwa ne
bayan damuwar Farida..? Bani da ita komai na duniyar nan na mallakeshi Ishaq sa'ar
mace tagari ne kaɗai banyi ba, shi kaɗai ne matsalata a yanzu da damuwata
Ishaq..wallahi halin Farida ya isheni, na kai maƙura..."
Ishaq ya saki ajiyar zuciya kafin yace "Nasani Tahir buh ya maganar da mukayi dakai
last week da kaje Ɗanbatta baka ƙara ma Goggo Abu maganar auren naka bane..?" Sai
lokacin Tahir ya miƙe daga kishingiɗan dayayi yana faɗin "Hmmm bari kawai Ishaq,
narasa me Farida tama Goggo Abu da take gudun ɓacin ranta, amma ni take ƙoƙarin
danne min hakki wallahi ko wannan zuwan taƙi kuma tace zata saɓamin in na sake na
tunkari Hakimi da maganar, wai zata ƙara ma Farida magana in sunyi waya.." Tsaki
Ishaq yaja kafin yace "Wallahi baji zatayi ba, ai da tana jin magana dataji tasu
Alhaji, gaskiya in na samu lokaci zanje ƙauye nama Goggon bayanin za'a cutar dakai
kuma Farida bata da asara." Murmushin dayafi kuka ciwo Tahir yayi kafin yace
"Kadama ka wahalar da kanka Ishaq, domin Goggo bazata taɓa sauraranka ba daga
ƙarshema zatace haɗa baki mukayi na turo mata kai. Kawai nidai yanzu na cire
lamarin Farida araina ina ta addu'a amma tabbas Ishaq na kai maƙura nifa mutum ne
mai lafiya ba dutse ba ina buƙatar macen da zan dinga samun natsuwa awajenta.."
Saurarawa yayi yana maida numfashi cike da ɓacin rai kafin ya cigaba da faɗin "Ko
bama haka ba Ishaq ina buƙatar macen da zata kula dani nima, taji dani nima ina so
naga ana bani girma amatsayina na namiji, yanzu ka duba kagani Ishaq rainin da
Farida tamin har yakai ta tafi tsawon kwana biyar bata agida, amma jiya data dawo
basai ta nemeni ba..? Toh sai ma kallon rainin data bini dashi da ƙyar ta iya cemin
ina kwana, fisabillahi wannan wace irin rayuwa ce? Duk haƙurinka sai an ƙureka.."
Ya faɗa yana dafe kanshi. Ishaq dake kallonsa cike da tausayinshi tsam ya miƙe ya
zagayo gabanshi yasaka hannu ya dafa kafaɗarsa yana faɗin "Is Ok...Ya isa haka
Tahir maganar duk bashi da amafani tunda ba ji zatayi ba, ni narasa wane irin
taurin kai ne Farida ke dashi ko Aliya fa tayi tayi da ita amma ƙarshenta ma yanzu
sama sama take mata magana bazata chanza ba, haƙuri zaka ƙara da kuma tausan Goggo
Abu har ta amince maka ka sanar da Hakimi kana buƙatar ƙara aure..."
Tahir baiyi magana ba illah sauke ƙananun ajiyar zuciya dayakeyi kafin ya miƙe yana
sauke jannun Ishaq dake kafaɗars bai bari sun haɗa ido ba sai ma ƙoƙarin duba
agogon hannunshi da yayi lokaci ɗaya yana faɗin "Ishaq zamu makara fa, muyi alwala
mu isa masallaci.." Ya faɗa yana kama hanyar ficewa, ajiyar zuciya Ishaq ya sauke
kafin yace "Ok..." Daidai lokacin da Tahir ya fice daga Office d'in shima bai zauna
ba wayarsa ya ɗauka ya tura cikin aljihu yabi bayan Tahir ɗin da sassarfa.
Farida ko tun bayan fitansu take zaune a falo tana latse latsen waya, sai da ta
gaji taga dama kana ta tashi ta nufi dining tayi breakfast ta gama kenan sai ga iya
ta fito ɗauke da Naila wacce ta tashi daga barci Iya tayi mata wanka ta saka mata
wata riga doguwa bulawus mai kyau rigima takeji don yau ko madarar nata data dama
mata bata sha ba, shine ta fito da ita zuwa wajen Farida karɓan ta tayi ta cilla ta
sama alamar wasa duk yadda Naila keson wasa yau bata nuna ba don kuka ta saka mata
tana binta da kallo, Farida ta kyaɓe fuska tana faɗin "Meya sameta ne Iya..? Baki
bata madararta bane..?"
Iya tace "Na bata ta ƙi karɓa Hajiya gwada bata nono ƙila shi takema kewa.." Dariya
Farida tayi tana shafa kumatun Naila tace "Wannan babbar yarinyar? Ai tayi girma da
shan nono, kinga ina ɗaukanta ina haki shiyasa nake jinjina ma Mufeeda don tana
ƙoƙarin ɗaukan Naila, tunda naga tafi sabawa da madararta na yayeta domin bazan iya
ma tuna rabon da na bata nono ba gaskiya.."
Iya tayi galala da baki kafin tace "Haba Hajiya Naila fa yarinyace ƙarama har yanzu
ko shekara bata rufe ba fa.? Gaskiya bai kyautu ki yayeta tun yanzu ba, don Allah
ki barta ko wata sha takwas tayi in bazaki barta ta cike biyu ba..." Tun kafin Iya
ta ƙarasa Farida ke jifanta da wani banzan kallo batayi magana ba sai da ta miƙe ta
miƙama Iya Naila kafin ta ɗauki wayarta tana fadin "Iya ki kama bakinki, ina
ruwanki da hukuncin dana yanke? Ai nima nasan ciwon kaina ko..? So plz ki tsaya iya
matsayinki bana so kina shiga hurumin da banaki ba.."
Iya ta rausayar da kai tana ƙara riƙe Naila dake rigima tace "Allah ya baki haƙuri
Hajiya.." Bata bi ta kanta ba ta haura sama ta amsa kira, da kallon kaiconki Iya ta
bita kafin ta kaɗa kai ta koma ɗakin Mufeeda da Naila da ƙyar ta lallasheta ta sha
madararta kuma ma harda rigimar bata ga Mufeeda ba goyata tayi kafin ta fito falo
ta fara tsabataceshi, bata gama ba Naila tayi barci sai ta maidata ɗaki ta kwantar
ita kuma tazo ta cigaba da aikinta lokaci bayan lokaci tana leƙa Naila acikin ranta
kuma tana fatan Allah ya kawoma Alhaji mafita amma tabbas baiyi dacen abokiyar
arziki ta gari ba duk da ba Alhaji ya kawota gidan ba amma kuma kyawawan
halayyarshi da kyautatarwarshi garesu yasa take ganin girmanshi da darajanshi kuma
take zaune dasu da zuciya ɗaya.
******
Duk tsawon wannan kwanakin zaman doya da manja ke gudana tsakanin ma'auratan, shi
Tahir ya riga daya fita sha'anin Farida sam domin yana ganin yana gaba da ita amma
baida daraja da arzikin da Farida zata nemeshi, shiyasa yayi burus da ita dagashi
sai 'ya'yanshi suke harkar rayuwarsu ko alama bai sakama ranshi yana da wata mata
agidan, toh itama Farida bata damu dashi ba, hakan da yayi ma yayi mata daɗi domin
batason fitinar Tahir sam gani take da zarar ta nemeshi fitinarshi zata tashi
shiyasa ta shareshi a zuwan in ya gaji zai nemeta lokacin ya huce sai su daidaita.
Kwana biyu ne da dawowarta bata fita ba saboda gajiyar dake jikinta, ranar data
kwana uku bata wuni a gida ba, baima san ta fita ba, sai da ya dawo gidan wajen 6
na yamma Iya ke sanar dashi Farida bata gida ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yayi amma na
yau kam Farida takaishi bango sosai. Garzali yaje ɗauko su Basma daga Islamiya sama
ya haura ɗauke da Naila wacce ya amsheta hannu Iya har ya shiga wanka ya fito
zuciyarsa tafasa take, koda ya fito Naila tayi barci dama ita rigimarta kaɗan ce
dan dataji taushi da iska sai barci yana ƙoƙarin zura jallabiyarsa ne yaji ƙarar
buɗe gate alamun Garzali ya dawo daga ɗauko su Mufeeda, carbinsa ya ɗauka ya fito
kansa na ɗigar da ruwa kaɗan, dasu ya cikaro duk suka gaisheshi ya amsa fuskarsa ba
walwala kafin ya kalli Bassam yana faɗin "Oya shiga ka fito mu tafi Masjid.." Kada
kai yayi kafin ya shiga ɗakinsa agurguje Bassam ya ɗauro alwala ya fito Tahir ya
kama hannunshi suka fice zuwa masallacin dake kusa dasu yayinda Mufeeda da Basma
kowacce tayi ɗakinta domin ɗaura alwala tunda wasu masallatan ma sun riga sun tada
Sallarsu.
A ƙa'idar Tahir baya baro masallaci sai an idar da sallar Isha'i yau ma ɗin hakane
ta kasance riƙe da hannun Bassam kamar koda yaushe suka shigo gidan megadi na musu
barka da zuwa basu kai ga isa ƙofar da zata sadasu da babban falon gidan ba horn
d'in motar Farida yayi musu maraba da hanzari megadi ya wangale mata gate ta sako
hancin motarta cikin gidan, cak Tahir ya tsaya ya waigo yana kallonta tana ƙoƙarin
faka motar a parking spaces, ta cikin motar itama take kallonsa ganin yadda yake
mata wani kallo ne yasa tasha jinin jikinta sosai tana ƙoƙarin fitowa daga motar ne
nepa suka ɗauke wuta wajen yayi duhu shi ya taimaketa don Tahir hannun Bassam
yasaki yace mai ya shiga cikin gida shi kuma ya nufi wajen Garzali yana sanar dashi
ya duba Genaretor ɗin Allah yasa akwai diseal, lokacin ne Farida ta samu sa'a tayi
wuf ta fada cikin falon, yana ganin haka shima ya juya ya take mata baya tana
ƙoƙarin haura steps d'in benen ne taji kakkausar muryanshi yana faɗin
"Da zinin wa kika fita Farida....?" Muryansa cike da amon sauti mai cike da
tsantsar ɓacin rai, rass gabanta ya faɗi sai ta kasa juyowa don muryansa kaɗai ta
isa ta bayyana mata yau Tahir ya gama haƙuri da ita, bata samu zarafin juyowa ba ya
sake daka mata wata uwar tsawar data gigita ta, bama ita kaɗai ba hatta su Basma da
Bassam da Mufeeda da Iya dake ɗakunansu sai da suka firgita suka fito falon da
sauri daidai lokacin da aka kunna Genaretor haske ya gauaraye ko'ina.
"Nace da izinin wa kika fita Farida...? Saboda raini kina jina ina magana kina min
banza..?" Ya faɗa yana tattare naman goshinsa saboda fushi, Farida ta juyo a
hankali tana kallonshi tana kuma ƙoƙarin ɓoye razanarta haɗe fuska tayi kafin tace
"Dama na saba tambayar izininka ne idan zan fita...? Na ɗauka nida kai mun wuce
wannan ƙarnin..." Ta faɗa tana kaɗa key ɗin motar dake hannunta ba tare data jira
komai ba ta kaɗa kai ta juya ta cigaba da taka steps d'in cikin halin ko in kula
wani ɓacin rai mai zafi ya ziyarci zuciyar Tahir ko gani bayayi yayi kukan kura ya
bi bayanta a harzuƙe kafin ma ta ankara ya cimmata sai ji tayi ya jawota baya da
sauri ƙiiiiii.....kamar wata kayan wanki, bai direta ko'ina ba sai tsakiyar falon
bayan ya ingizata baya tayi taga taga zata faɗi, ba domin Allah ya taimaketa ta
daddage ta riƙe kujeran dake falon ba da sai ta faɗi ƙasa..
Cike da mamaki take binsa da kallo kafin ta buɗe baki tace "Tahir...Lafiyanka ƙalau
kuwa..? Ta faɗa tana binsa da kallo ganin yanda yake huci bai bata amsa ba illah
cewar daya ƙarayi "Nace da izinin ubanwa kika fita Farida...?" Baki buɗe take
kallonshi kamar yadda Basma da Bassam suka zura musu ido, cike da wani yanayi
hakama Mufeeda, Iya ce dake tsaye ranta duk ba daɗi tunda suke da Alhaji basu taɓa
ganinshi cikin fushi hakaba tana ƙoƙarin isa gareshi Farida tace "Kace da izinin
ubanwa na fita ko..? Toh da izinin ubana ko..." Ai bata ƙarasa ba taji Tas! Tas!
Maruka biyu kyawawa Tahir ya wanke fuskar Farida dama da hauni lokaci ɗaya, kamar
walƙiya taji marukan saboda azaba sai gata zaune daɓas da ɗuwawunta akasan cafet
ɗin falon hannayenta dafe da kuncinta tana bin Tahir da kallo hawayenta na sauka
kamar an buɗe famfo.
Ba Farida kaɗai ba hatta Basma da Bassam saboda razana sai da ya ƙanƙame Basma suna
rawar jiki a tare lokaci ɗaya suka fashe da kuka, hakama Mufeeda da ta maƙale jikin
ƙofa tana rawar jiki, Iya ko ƙirji ta dafe tana faɗin "Innalillahi Wa'inna
Ilaihirraju'un...Alhaji mezan gani jaka..? Ashsha abu baiyi daɗi ba.." Ta fada cike
da damuwa.
Ko sauraranta baiyi ba ya kalli Farida yana nuna ta da yatsa kafin ya fara faɗin
"Wannan ne na farko kuma na ƙarshe... wallahi in kika ƙara fita bada izina na ba
Farida daga ranar zaki tabbatar da babu wani amfanin da kike dashi a cikin rayuwar
Tahir..." Ya faɗa cikin kakkausar murya, kuka Farida ta fashe dashi bilhaƙƙi da
gaskiya kafin ta miƙe cikin kuka tana faɗin "And So What...Nima ai baka da wani
amfani a wajena, waye kai awajen Farida? Ka sakeni in ka isa tunda bani da amfani
juz Tahir ka sakeni ka gani in rayuwata zata yanke ko ta wulaƙanta daga yau ka
sakeni don Allah..." Ta faɗa tana hargowa cikin kuka.
Basma ce ta saki ihu tana faɗin "No..Momy Daddy Stop plz..." Ta faɗa tana duƙawa
haka shima Bassam yayi suna kuka suna faɗin "Plz Daddy Momy don Allah ku bari kuna
sakamu muna jin ba daɗi..." Suna faɗa suna kuka, Mufeeda ma kukan take, da kallo
Tahir ya bisu lokaci ɗaya kuma sai jikinsa yayi sanyi sosai idanuwansa sunyi jawur
kai kawai ya kaɗa kafin ya wucesu da sauri ya haura sama cikin sassarfa, ganin haka
yasa Farida tabi bayanshi da sauri tana kuka sai dai kafin ta ƙarasa ya shige
bedroom ɗinsa ya banko ƙofa a ƙofar ɗakin ta tsaya tana kuka tana faɗin "In ya isa
ya fito ya saketa dama ita tagaji da aurensa..." yana jinta ya mata banza kan
gadonsa ya hau ya saka kanshi cikin gwiwoyinsa yana ƙoƙarin daidaita numfashinsa.
Basma da Bassam ko kuka suke sosai na ganin abunda ke faruwa tsakanin iyayensu
wanda basu taɓa gani ba da ƙyar Iya ta lallashesu kowanne ya nufi ɗakinsa cikin
damuwa, haka ma Mufeeda ta koma ɗakinta ta faɗa bisa gado tana kuka, wanda tarasa
dalilinshi, ranar dai gaba ɗaya gidan ba wanda ya yi dinner haka kuma barci sai dai
sama sama, daga Tahir ɗin har Farida barci ɓarawo ne ya ɗaukesu balle su Basma da
suka tashi fuskokinsu duk a kumbure saboda kuka.
*Janafty..*
*Aisha Alto.*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA BAKWAI*
....Duk da yaran Sun Tashi Zuciyarsu ba Dadi bai Hanasu Shirin Tafiya mkaaranta
ba,Suna bisa Dinning Suna Breafsat,Kowa ka gani Fuska ba Walwala Don Daga Tahir din
Har Faridan ba Wanda Sukaji Motsinsa Har Gwarashi yazo da Asuba ya Tashi Bassam sun
Tafi masallaci.
Batare da Sun saka iyayen nasu a ido ba garzali ya Kwashesu Zuwa Mkranta Naila Kuma
dama Wajen Tahir Ta Kwana,Sun Fita ba Dadewa Farida ta fito Daga Cikin Bedroom
Dinta Dauke da karamar Trolly dinta Fuskarta ta Kumbura Idanuwanta Sun Chanza kala
Saboda Kuka Tana Sanye da Riga da Sikat na Wata Atamfa Holland,Daurin Dankwalin dai
gashi ga kamarshi,sai karamin Gyale Vail Data Yafo Bisa kafadarta,karamar Jakarta
na Hannunta Hade da Wayarta sai Key din motarta Dake Hannunta.
Ahaka ta Sauko Har Zuwa Main Falo din Tana Tafiya tana Share Hanci da Iya taci
karo Wacce Tafito Daga Kichen,cikin mamaki Take kallonta kafin Tace"Hajiya lafiya
Kuwa..? Wata Uwar Harara Ta maka mata kafin Ta Saki Tsaki takama Hanyar Fita Daga
Falon,iya bata Dandara ba Tace"Haba Hajiya gaskiya Wannnan ba girmanki bane,Ina
Zaki Tafi ki bar mijinki da ya"yanki Kefa ba yarinya bace Yaji bai kamace ki ba,kin
kai Munzalin Da Zaki ma Wata Fada bama Kanki ba..."Tafada Cikin Nuna Alamun Abun
bai mata Dadi ba.
Juyowa Farida Tayi Afusace kafin Tace"Wlh iya sai na Tafi nagaji da Irin Tozartanin
Da Tahir yake yi nagaji..!kina gani Jiya gabanku gaban ya"yana Ya Tsinkeni da
maruka har biyu Saboda ga baiwarsa ko,Allah sai na Tafi Sai ya Zauna Shi
kadai.."Tafada Tana Sharbe Kwallah kamar Wata yarinya.
Iya tayi kasake kafin Tace"Hakuri Ake Hajiya,Kowa fa kikagani yana Zama lafiya
agidan Mijinshi karki Tambayeshi Hakuri,Kema Kiyi Hakuri Don Allah In kika Tafi
Gida Kicema su Umma Mene Don Allah.."?Tana Sharan Ido Tace"Ai ba Kano Zani ba
Danbatta zani Wajen Goggo Abu taga Shaidan Yatsun Tahir Akan Fuskata..."Tafada Tana
juyawa da Sauri Ta Fice Daga Falon Tana kara Rike zaman karamin Akwatin Dake
Hannunta Iya Dake Tsaye ta Yunkura Zata Bita sai Taji Muryan Tahir Daga Sama yana
Fadin"kyaleta iya..."yafada Cikin Halin ko Inkula
Iya ta Waigo Jiki asanyaye kafin Ta Rusuna Tana gaisheshi,Shiko yana Daga saman
Benen ya amsa mata Fuskarsa na Nuna Alamun baida Damuwa yana Sanye da Amarican
Suit,Ash colour,Yar jakar Briefcase dinsa ne Ahannunshi da alamun Fita Zaiyi Tana
Kokarin Barin Falon ya Karisa Saukowa yana Fadin"Naila tana Room Dina iya Ta Koma
barci plz ki Haura ki Daukota Ta Zauna Kusa dake.."Ya Fada yanq Nufar hanyar da Zai
Sadashi da Haraban Gidan Lokaci Daya yana kallon Agogon Fatan Dake Hannunshi.
Iya tabi bayanshi da kallon Tsausayi kafin Tace"Insha Allahu Adawo lafiya
Alhaji.."Bai Jita ba Don ya Riga yaFita Daidai Lokacin Kuma Garzali ya Sawo kan
Motar Cikin gidan ya Dawo Daga kai Su Basma mkranta batare da bata Lokaci ba ya
Shiga ya Juya Dashi Zuwa Office don Ya Makara gashi Kuma Meeting garesu Suna Tafe
yana kallon Agogon Dake Tsitsiyan Hanmunshi kafin Wayarsa kirar iphone 11
promo,tadauki Tsuwa Sunan Ishaq ya Fito baro baro Afuskar Wayar Dauka yayi Da
Hanzari suka gaisa kafin Su Cigaba da mgana Cikin Kulawa da Tsantsan Ilimi.
********
*D'ANBATTA*
Goggo Abu Sai Dai Taga Farida Kwatsam Tazo Tana Mata Kuka Wiwi kamar Wacce Aka
yanka Ko Akace Uwarta ta Mutu Lokacin Data Iso Ashe na gidan,nan Goggo Abu Ta Rude
Ta Shiga Tambayanta Abun ya Faru,Farida na Kuka tana Zayyanama Goggo Wai Tahir ya
mareta Har guda hudu Dukkanta ma yaso yi sai da iya mai aikinsu Ta Shiga Tsakani
Farida na Kuka Tanama Goggo Abu Rantsen Rantsen Cewa Tahir yace ma bata da Wani
Amfani Acikin Rayuwarshi.
Ran goggo Abu ya baci Ta Dinga Sauke Numfashi Takaichi Attahiru na Damunta Ashe ce
Tace"goggo Kada ki yanke Hukunci Cikin Fushi yakamata Shima yayan Ki kirashi ki
Fara jin Ta Bakinshi Tukunah.."Tafada Da Sigar Lallashi,Cikin Kuluwa Farida Ta Dago
Tana Hararan Ashe kafin tace"Eh mana Akirashi mana ai ba karya namai ba Jiya agaban
ya'yana Da yan Aiki ya Tozartani nidai kam goggo Ki kirashi na Gama zama da Tahir
kamar yadda yace banda Wani Amfani Acikin Rayuwarshi Nima Tahir baida Amfani
Awajena ya"yana yaje ya Rike na barmai Dama badasu nazo ba..."Tafada Tana
Shesshekan Kuka Lokaci Daya Tana Hararan Ashe din Domin Dama Jininsu baizo Daya
Saboda yadda Tahir yake matukar ji da Ashe Ita Kuma Duk Abunda ya Shafi Dan"uwanta
bata Wasa Dashi.
Ashe bata mata mgana ba illah kallon Goggo Abu Datakeyi kafin Tace"Kinji goggo Don
Allah Kifara Kiranshi Tukunnah.."Jin Haka yasa goggo Ta Mike Ta Shiga Ciki Ta bar
Ashe da Farida Anan Cikin Falonta Kowa na kallon Kowa Cike da Takaichi Mikewa Ashe
tayi ta Fice Zuwa Shashen Innaro Tana Fadin"Allah ya kawo maka mafita
Dan"uwana..."Tafada Cike da Habaici da Kuluwa,Da Ido Farida Ta Bita kafin Ta Rakata
da Tsaki Tana Share Kwallah.
Fitowarsu kenan Daga Meeting yana Hanyar Komawa Office ya Fito da Wayarshi Wacce
Tun Shigansu meeting din ya sakata A Silent Hankalinsa ne ya Tashi Ganin Misseds
Rututu Na goggo Abu gabansa sai dai ya Fadi yana Bude Kofar Office din ya Na
Kokarin Kiranta gabda zata Katse Ta Dauka yana Kokarin gaisheta ta katseshi A
Fusace Tana Fadin"Dagata min Attahiru Nagode da Abunda Kamin in Har na Isa dakai
kazo gida yanzu ka sameni mutumin banza kawai..."Tafada Cikin Fushi kafin ta yanke
Kiran,Dafe kai yayi yana salallami,Domin yasan Cewa Farida Tagama Hadama goggo Abu
Famfo shi bama Wannan ya Dameshi ba Irin yadda Ta Dau Zafi Dashi Allah ne kadai Zai
Kwaceshi.
Office din Ishaq ya Tafi Agurguje Sukayi mgana Sama sama Kafin Suyi sallama ya
Fito bai Tsaya bata Lokaci ba yace ma garzali Su kama Hanyar Danbatta sai da Sukayi
Nisa ne Garzali ke Tunamai dasu basma Ba Wanda Zai Daukosu Daga Sch,Dafe kai yayi
yana Salati kafin ya Dauki Wayanshi Shugaban mkrantan Su Basma ya Fara Kira inda
yabada Umarnin Indan Antashi Daga Mkranta Basma da Bassam Su bi Sch Bus Su Dawo
gida Saboda Dukkansu basunan bamai Zuwa ya Daukesu,Daganan sai Shugaban Mkrantar su
Mufeeda Itama Abunda yace Kenan Kafin ya Katse Kiran,yana Sakin Numfashi kadan
yasan yau sai sunyi Rashin Islamiya Saboda baita yarda Sun Fita Waje Su kadai ba
Duk inda Zasu sai dai garzali ya kaisu Kuma yana Da Tabbatacin Tunda Sukaga babu
mai Kaisu bazasuyi gangancin Fita ba.
Wajen 2pm suka iso Kofar gidan Hakimi,Shikanshi Hakimi da Jama"arsa Sunyi mamakin
ganinshi don Akasari bai Cika Zuwa Cikin Sati ba Sai karshen Sati,Hakimi bai yi
mamaki Sosai ba Saboda yaga Zuwan Farida Hartazo ta gaisheshi Yaga Fuskarta ta
Chanza kamar tayi Kuka Daya Tambayeta sai tace bakomai tatashi Ta Shiga To Tunda
yaga Zuwan Tahir sai yasha Jinin Jikinsa Ammh Dayake yana da Miskilanci sai bai
Nunama Tahir din Komai ba Wanda Sai da yagama gaisawa da Jama"ar Wajen kafin ya
Karisa garesa yana Kwasan gaisuwa,bayan Tambayi Aiki da yara,bai Zauna ba ya Mike
yacemai Zai Shiga Cikin gida,Hakimi yayi Mirmishin su na manya kafin ya kalli Tahir
din yana Fadin"Attahiru yau kazama Mara Hakuri ko...? Akullum ina maka Nasihan ka
Rika kai Zuciyarka Nesa Domin Akasari mata akarkarce suke Kana Kokarin Daidatasu
Suna kara famdarewa ne,Toh Dole sai munyi Hakuri Dasu kaji...?"Yafada kasa kasa
Wanda Inba Tahir din ba Wanda yakejin meyake Fada,Sadda kanshi yayi kasa yana
Fadin"Naji Hakimi Insha Allahu Zan Kiyaye.."Kai ya gyada kafin yace"Tashi ka Shiga
Ciki Allah yayi maka albarka.."Da Ameen ya amsa kafin ya Wuce Zuwa Cikin Gidan...
Sheshen Innaro ya Wuce Direct nan Suka Ci karo da Inna Fulera ta Zube Tana
gaisheshi ya amsa Cikin sakin Fuska Kafin ya Wuce Zuwa Babban Falon Innaro Dake
Shashenta,Nan ya iske Innaro da Ashe Suna Hira,Ashe Dataji Dadin ganin Dan"uwanta
sai da tatashi ta Fada Jikinsa Tanamai Oyoyo Riketa yayi yana Dariya Lokaci Daya
yana Shafa Kanta,Tare Suka Zauna gaban Innaro,Tahir yafara gaisheta ta amsa Cikin
Sakin Fuska da Fara"a Tana Tambayanshi su Basma ya amsa da Suna Mkranta,Yadade
Awajenta Suna gaiswa da Hira kafin ya barota Zuwa Shashen Goggo Abu Ashe bata
biyoshi ba Saboda tasan Goggo Abu Korarta Zatayi.
Lokacin Daya Sawo kanshi Falon goggo Abu Da sallama Abakinshi da Farida yaci karo
Tayi Rashe Rashe Atsakiyar Falon Tana Shan Fura,Suka Hada Ido,Daure Fuska yayi
kamar bai Taba Dariya ba yana karisowa Cikin Falon Goggo Abu Tana Fitowa Daga Uwar
Dakinta Suka Ci karo,Takalmin kafarsa yacire kafin ya Zauna yana gaishe da goggo
Abu Wacce Ke Dankaramai Harara kafin Tace"Tashi Tsaye bana Bukatar gaisuwaarka
Attahiru,domin ka gama Nunamin Iyakata..."Tafada Cikin Kakkausan Murya.
Kasa yayi Dakai yana Jin Wani Daci Acikin Ransa,Dagowa yayi yana Kallon Farida
Wacce Ke kallonshi gabanta ne yafadi ganin Irin Kallon Dayake Jifanta Dashi bai iya
mgana baa,sai ma Sauraran Goggo Abu Dayayi Tayi Ta Inda Take Shiga batanan Take
Fita ba Sai da Tagama Wanke shi Tas Kamar Zata Dakeshi Ta Koma Gefe Tana Haki,sai
da yaga Ta gama kana ya Dago yana kallon Goggo Abu kamar yayi kuka yana Fadin"Goggo
Ta Fada miki Fita Take bada Izinina ba,Ta sanar dake batamin Kallon Mijinta Dauka
na Take tamkar Wani yaronta ko Ma"aikacinta Ta gayamiki Wannan Ko bata gayamiki
ba.."?Yafada kamar Zai Fashe da Kuka.
Daga Farida Har Goggo Abu Jikinsu yayi Sanyi Saboda yadda Tahir din yayi mganar,Sai
goggo Abu Ta Koma Da Kallonta kan Farida tana Fadin"Kinji Abunda Mijinki yace In
Hakane To Tabbas baki kyauta ba,Taya zaki Dinga Fita bada Izininsa ba Ai ba Zaman
kanki kikeyi ba Ko Farida,Gaskiya ki gyara Kina Cikin Fushin Allah da Tsinuwar
mala"iku matukar baki Roke Mijinki Gafara ba.."
Farida ta kanta ke kasa ta Fashe da Kuka,Jawota Jikinta goggo Abu Tayi Tana
lallashinta Lokaci Daya Tana Fadin"Yi Shuru kibar Kuka,Ki bama Mijinki Hakuri Kune
mi gafaran Juna Don Allah bana Jin Dadin Wannam Rashin Jituwar naku,kufa ba yara
bane Kune fa Kuke da yara kamar basma da bassam Haba Don Allah Farida Don Allah Ku
Sansanta kanku.."Tafada Cikin Sanyi Dagowa Farida Tayi Tana Share Kwallah kafin
tace"Toh Goggo.. "Muryanta ta Dishe Sosai...
Mirmishi goggo Abu Tayi kafin Ta Mike tana Fadin"Yauwa Naji Dadi bari naje na
Karboma Atrahiru Fura Wajen Innaro yanzu zan Komo ."Tafada Tana Ficewa Don ta basu
Waje bayan Fitanta Falo ya Dade Shuru kafin Farida ta yanke Shurun bayan Ta Dago
Tana kallon Tahir Daya Tsurama Cafet din Goggo Abu Ido Fuskarsa ba Annuri ko Kadan
Duk da gabanta na Fadi hakanan ta Daure Ta Furta.."Srry...'Tafada Muryanta na Rawa
Ko kallonta baiyi ba,ganin Haka yasa sai Jikinta yayi sanyi Tatashi Ta Koma Side
din daya ke kallo Ta Sake Furta"Am Srry..."Kauda kai yayi Yana Neman Tashi sai Ta
Riko Hanmunshi Da Sauri ta Fashemai da Kuka bayan ta Dora kanta bisa
Cinyarsa,tsayawa yayi yana Kallonta Kukanta na Dakarmai Zuciya,Runtse ido yayi
kafin ya Dora Hannunshi bisa kanta yana Tapping cikin Ajiyar Zuciya yake
Fadin"Shiii...is ok.."..
Jin Abunda yace ne yasa Ta Dago Da Sauri Fuskarta Jage jage da Hawaye,tana
kallonshi Mirmishi ya sakarmata kafin ya Zaro Wani Farin Hankey Daga Aljihunsa,yana
Share mata Hawaye yana Fadin"Nace komai ya Wuce ko..? Kece fa kike ja muna Fada
Farida,in da bakiyi Saurin Zuwa Wajen goggo Abu banayii Regreating din marin da
nayi miki zan baki Hakuri,plz Farida..."Bai karisa ba goggo Abu Ta Shigo Dole yayi
Shuru ganinsu haka sai ya sanyayamata Rai,Furar ta mikamai ta sake Ficewa,yana
kallon Farida kasa kasa yafara Shan Furarsa,yana gamawa ana Kiran sallar La"asar
nan yafice Zuwa Msallaci Ita Kuma goggo Abu Ta Dingama Faridar Nasihan bayan Suma
Sun Idar da Sallar.
Bai komo dakin Goggo Abu ba sai da ya sallami kanwarsa Ashe,Har gida ya karata
akafa suna Tafe Suna Hiransu gwanin ban Sha"awa,sai da ya Dawo ya Shigo bangaren
Goggo Abu yace Farida tataso Su Tafi,nan ma goggo Abu Hadasu Tayi tana musu nasiha
Sosai kafin Su mata sallama Shashen Innaro Suka Koma Suka mata sallama nan Tabada
Sakon Fura mai Dadi Tace akaima basma da Bassam,Awajema Sallama Suka ma Hakimi ya
bisu Shima da Sanya albarka.
Tahir shi ya Tukasu Shida Farida Acikin Motarta Shi Kuma garzali ya Tuko ta
Tahir,acikin Motan Ma Hannunshi Farida Ta Damke tana Fadin"Shine ni baka bani
Hakuri ba.."Tafada Cike da Shagwaba,Hankalinsa na Wajen Tuki ya Waigo yana
Fadin"Ah...Waht Are u Eating na baka is Fooling Down,Zan baki mana ammh ai kinsa
nawa Is so Special ko.."Yafada yana kallonta Lokaci Daya yana Kashe mata ido,Dariya
tayi tana Kwantar da kanta Cikin kujeran Mota batace komau ba Ammh Hannayesu Sarke
da Juna Jefi Jefi suna Hira Har Suka Kariso gida.
Abun mamaki Haka yaran Suka ga Iyayen nasu Sun Shigo Hannuwansu Sarke da
Juna,Saboda Jin Dadi basma da bassam Suka Ruga suka Rumgumesu suna Ihun Oyoyo momy
da Daddy,Hatta Iya da Mufeeda Sunji Dadin ganin Farida da Tahir Da Alamun Komai ya
Wuce,Ranar dai gidan Gabadaya yayi Dadi Dukkansu tare Sukayi Dinner Suna Yi Suna
Hira Fuskar ya"yansu cike da Farinciki,Da Suka gama Cin Abunci Suka koma Falo Suna
Hira da ya"yansu Hatta Naila Taji Dadi Sosai ganin yadda Take Tsallake Tsakanin
Cinyar Tahir dana Farida,sai Wajen Goma Kana Suka Umarcin yaran da Su Tafi Dakinsu
su kwanta Naila Kuma Farida Ta Mikama Mufeeda.
Awannan Daren dai Farida ta Hakura ta bama Tahir Ahakkinshi nan Suka Fahimci Duka
Sunyi Kewar Juna,Farida tagayama aya Zagi,domin Tahir dai sai da ya Fanshe,koda
Asuba ma Daya Dawo masallaci sai da Ya Dora Farida Tafara gajiya Sosai Sai Tura
baki Takeyi Domin Abunda Ke Hadata Tahir kenan Jarabarsa.
*Aisha Alto..*
*Anitha..*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
*BABI NA TAKWAS*
Zuwa wannan lokacin komai ya gama daidaita a tsakanin Tahir da Fareeda basu da
matsalar komai yanzu, Fareeda ta natsu ta bar duk abun da take yi ta daina fita
ko'ina kullum tana gida tana baiwa mijinta da 'ya'yanta kulawar data dace, wanda
sauyin wannan hali nata ya yiwa kowa daɗi a cikinsu gidan ya zama cikakken gidan
ma'aurata masu tsananin so da ƙaunar juna haɗe da tarairaya. Kullum cikin farin
ciki da ɗoki 'ya'yanta suke, yanzu babu abunda ke damunsu saboda suna samun kulawar
mahaifiyarsu kuma tana jansu a jikinta bata kyararsu komai suke so tana yi musu,
Mufeeda da Iya suma abun yayi matuƙar yi musu daɗi gidan ya zama happy family babu
damuwa ko matsalar komai a gabansu sai farin ciki.
Suna zaune dukansu a falo gidan suna kallo a makeken talabijin ɗin dake manne a
bangon falon Naila na kan cinyar Mufeeda tana bata madararta yayinda Basma da
Bassam ke gefe zaune a kan kafet suna yin Homework ɗinsu kasancewar gobe Monday
akwai makaranta Iya ta fito daga ɗakinta da sauri tana share hawayen dake zubo mata
ta nufo Tahir ɗa Fareeda dake zaune a saman kujera suna magana ƙasa ƙasa wanda su
kaɗai suka san abinda suke faɗawa junansu dan babu mai jinsu ta ɗan rusuna a gaban
Tahir tana goge ƙwallah tace "Sannunku da hutawa Alhaji." A hankali Tahir ya ɗago
da kansa yana kallonta kafin ya gyara zama sosai yace "Yauwa Iya sannu da fitowa...
amma lafiya kuwa na ganki haka?"
Tana ƙara duƙar da kai tace "Yanzu ne aka yo min waya daga can gida Allah ya yiwa
Yayana Malam Danladi rasuwa..." Ta ƙarashe maganar ƙwallah na ziraro mata ta kwanto
haɓar zaninta ta share wasu na ƙara zubo mata, salati Tahir da Fareeda suka yi
yayinda Fareeda ta miƙe ta kamo Iya ta miƙar da ita tsaye tana kallonta tace "Sannu
Iya, Allah ya jiƙansa ya gafarta masa Allah yasa ya huta." Da Ameen ita da Tahir
suka amsa kafin ya tashi tsaye shima yayi mata gaisuwa cike da alhini kana ya fice
waje ya kira Garzali yace ya shirya ya fito da mota zai kai Iya Kano ba ɓata lokaci
ya dawo ciki yace da Iya taje ta shirya su wuce Garzali ya kaita, sannan ya haura
sama zuwa ɗakinsa ya ɗebo kuɗi masu yawa yazo ya bata ta duƙa tasa hannu biyu ta
amsa tana masa godiya ta koma ɗakinta ta ɗauko 'yar jakar gana most go ɗinta ta
fito Mufeeda dasu Basma da Bassam harma da Fareeda suka rakata har bakin mota ta
shiga Garzali yaja suka fice daga gidan, su kuma suka koma cikin gida cike da
kewarta da tayata alhinin rasa ɗan'uwanta da tayi.
Washegari da sassafe wayar Umman Fareeda ta tashesu daga barcinsu mai daɗi da
sukeyi rungume da juna, da magagi ta lalubo wayar ta ɗauka ta kara a kunnenta nan
take faɗa mata Abbanta ba lafiya ciwon sugansa ya tashi an kwantar dashi a asibiti.
A gigice ta tashi ta sauka daga gadon tana tashin Tahir shima ya tashi ta faɗa masa
abunda Ummanta tace cikin tashin hankali tashi zaune ya ziro ƙafafuwansa ƙasa ya
sauka daga gadon ya riƙe hannunta suka shiga toilet agurguje sukayo wanka suka fito
suka shirya Fareeda ta ɗebi kayanta kala biyu ta zuba a ƙaramar jakarta suka fice
zuwa falo.
Ɗakin Mufeeda ta nufa ta samu har tayi wanka ta yiwa Naila itama tana shiryata ta
shiga ta ɗauki Naila tace Mufeeda ta ɗauko hijabinta ta fito, da mamaki Mufeeda ta
ɗauki hijabinta ta saka ta biyo bayanta suna fitowa falo taga Basma da Bassam a
shirye cikin kayan gida saɓanin na makaranta da tayi tsammanin zata gansu dashi,
duƙawa tayi zata gaida Tahir dake tsaye yana kallonta, ɗaga mata hannu yayi yana
faɗin "Lafiya Alhamdulillahi Mufeeda... Ku muje lokaci na ƙurewa." Ya ƙarasa faɗa
yana karɓar Naila dake hannun Fareeda ya saɓata a kafaɗarsa ya fice suna biye dashi
a baya. Garzali na ganinsu ya taso da sauri ya nufosu ya buɗe masa mota ya shiga
gaba ya zauna sannan ya buɗewa Fareeda ta shiga baya Mufeeda ta shiga kusa da ita
ta zauna sannan Basma da Bassam suma suka shiga ya rufe ya zagaya da sauri ya shiga
ya tada motar maigadi ya buɗe musu gate suka fice sai daya hau titi sannan Tahir ya
faɗa masa inda suka nufa, nan ya taka mota suka ɗauki hanyar Kano.
Ƙarfe 12pm. Dai-dai suka shiga garin Kano direct asibitin da aka kwantar dashi suka
nufa international Hospital kasancewar Fareeda tasan asibitin saboda anan ake
dubasa duk lokacin da jikinsa ya motsa irin haka.
Lokacin da suka shiga room ɗin da aka kwantar dashi yana barci sai Umman Fareeda ce
kaɗai suka samu wacce ke zaune a kujerar dake gaban gadon ta zuba masa idanu tana
kallonsa, da gudu Basma da Bassam suka nufeta haɗe da faɗawa jikinta suka rungumeta
tsam suna tambayarta meya samu Baban Mummynsu cike da so da ƙaunar jikokin nata ta
rungumesu tana basu amsa da baida lafiya ne, a hankali Tahir ya ƙarasa gabanta ya
durƙusa cike da ladabi ya gaisheta tare da tambayarta mai jiki? Da sakin fuska ta
amsa masa da "Alhamdulillahi jiki da sauƙi, barci yake tayi tun ɗazu da akayi masa
allura bai tashi ba har yanzu." Yana jinjina kai ya miƙe ya dafa ƙarfen gadon yana
faɗin "Allah ya ƙara sauƙi yasa kaffarane.." da "Ameen." Duk suka amsa kafin
Fareeda ta zauna bakin gadon da Abban nata yake a kwance tana kallon fuskarsa cike
da damuwa kafin ta ɗauke kanta tana kallon Ummanta cikin sanyin murya ta gaisheta
haɗe da tambayarta mai jikin itama, cike da kulawa ta amsa mata da faɗin "Ai da
alamun yaji sauƙin jikin sosai, dan kwana biyu ko barcin kwata-kwata baya iya samu,
yanzu kuwa kinga tunda likita yay masa allura bai tashi ba sai barcinsa yake yi."
Gyaɗa kanta Fareeda tayi fuskarta cike da tausayin mahaifinta tace "Allah ya ƙaro
sauƙi ya bashi lafiya." Bayan sun amsa Mufeeda itama ta matso tana ɗauke da Naila
ta duƙa a gaban Umman Fareeda ta gaisheta haɗe da tambayarta mai jiki, tana
murmushi ta amsa mata tare da miƙa hannu ta ɗauki Naila dake riƙe a hannunta tana
kallonta ta fara mata wasa tana ɓangala mata dariya, juyawa Tahir yayi zai fita
daga room ɗin da sauri Fareeda ta kallesa "Abban Basma ina kuma zaka je?" Ɗan
juyowa yayi ya kalleta yace "Zanje inga likitan ne, yanzu zan dawo." Gyaɗa masa kai
tayi ba tare da tace komai ba ya juya ya fice.
Koda Tahir yaje yaga Likita Hankalinsa ya Kwanta Tunda Likitan ya Nunamai ba Mtsala
ba kamar yadda Suke Tunani bane,wajen 2pm na Rana Abba ya Farka ba laifin Jikin
Nashi da Sauki nan yaji Dadi ganin Farida da Tahir din Hade da Jikokinsa,ganin
Hakane yasa Karfe 5 na yamma yayi Shirin Komawa Kaduna Shida Su bassam saboda
Mkranta ammh Farida Zata Zauna anan Tataya Umma Zama,Da Zasu Tafi Naila Ta makalema
Mufeeda sai Farida tace su Tafi da Ita,Umma ce ta Hana Tace Maza Farida Ta karbi
Naila Ta Zauna A Wajenta ai ba yayeta Tayi ba,Bude bakin Farida Sai Tace Ai Ta
yayeta,Wata Uwar Harara Umma ta sakarmata kafin ta Karbi Nailan Dake Hannun
Mufeedan Tana basu Umurnin Suyi Tafiyarsu Tahir yaji Dadin Haka Har saida Fuskarsa
Ta Nuna Farida ko Ta Bata Rai ita Dole An Takura mata,nan dai Suka musu sallama
Suka Juyo Zuwa kaduna.
Washehari Duka yaran Suka Tafi Mkranta Shima Tahir yatafi Office Gidan ba
Kowa,shiyasa bayan garzali ya Daukosu Daga Mkranta ya biya Dasu Restaurant ya Siya
musu Takeaway din Abinci kamar yadda Tahir ya Umarceshi Shi sukaci bayan Sun Dawo
kafin Suyi Shirin zuwa Islamiya,Sai yammah Suka Dawo Karfe 7 Tahir ya Dawo
Gidan,Shi ya Shigo musu Takeaway din Abinci Wanda ya biya Siyomusu kafin ya dawo
Gidan Tunda Iya bata nan,kuma bayason Su basma na Shiga Kichen sai Sun kara girma
Mufeeda kuma dama ba Aikinta bane.
Haka Suka Dinga Rayuwar Har Tsawon Kwana Biyu,Farida bata Dawo ba Tana kano,Ammh An
sallami Abba ya dawo gida,Washegari Tahir ya Koma kanon Shida Hakimi da Goggo Abu
da Innaro,Suka Iske Jikin Abba ya Warware kamar bashi ba,Basu jima ba suka Tafi
inda Dama su Tahir din Suka biya Danbatta Suka Taho Dasu,kuma su suka maidasu
gida,Da Tahir zai Tafi ya Kira Farida gefe yace yakamata tadawo gida Hakanan,bude
bakin Farida sai Cewa Tayi yanzuma Jinyar Uban nata sai ya Nuna bayaso,Kokarin Nuna
mata mtsalarshi yake ammh Farida Taki Fahimta basu Rabu ba Sai da duka Rayuwakansu
ya baci Har Tahir ya Dawo kaduna Ransa na bace da Faridar.
***********
Satin Farida Daya da Tafiya Kano,Har yanzu bata Dawo ba,iya ma Tana gidan Rasuwa
bata Dawo ba,kullum Sai dai in sun Dawo mkranta garzali ya Siyo musu Abinci Shi
kuma in Zai Dawo Gida da yamma ya Siyo musu Wanda Zasu Dinner Da Daddare,da Safe
Kuwa Shi yake Shiga Kichen ya Dafa musu Ruwan Tea ya Soya musu Kwai,Har Mufeeda
Taso ya Dinga barinta tanayi Tunda ta iya Don Ita da basma indai Suna gida Toh Suna
Nanike da Iya A Kichen Suna Koyon Girki,Ammh ya hanasu Shi gani yake Yara ne babu
Abunda Sukayi.
Yau ma Hakan Ta kasance Duk yau Din yatashi bayajin Dadi Ciwon mara kamar Zai mutu
Tun Daran Jiya sai da yasha Kanwa kana Abun ya lafamai,Ammh Haka yayi musu Abun
karyawa bayan Sun Dawo sallar Asuba,Bassam ne ke Kichen Din yana kallon Mahaifinsu
Cike da Tsantsan Kauna da Tsausayawa yana Tunanin Duk Duniya ba Wanda yafi son Su
da Kula Dasu bayanshi,Har Suka Tafi Mkranta bai iya Fita Aiki ba Zuwa Chan ya
Shirya ya Tafi Kuma bai kai yammah ba Wajen Biyar na yammah ya Dawo gidan Su basma
ma Sun Dawo Islamiyane Suka Tarar Dashi Takeaway dinsu na Dinner ma Garzali ya Fita
ya Siyo musu,Sun Damu Da Halin da Daddynsu ke Ciki Domin Dakyar ya iya Zuwa Sallar
Mangariba Ko Isha"i bai Tsaya anyi ba kamar yadda ya saba Ya Riko Hannun Bassam
Suka Dawo Gida.
Duka yaran sai sukayi Wani Iri Dasu Harda Mufeeda Wacce Itama Taji Ciwon Tahir Har
Aranta,Zaune Sukae aFalo Sun Zabga Tagumi Gashi gobe Friday Suna da mkranta,Shine
ya Fito ya gansu Sunyi Zugum Zumgum ya Sauko yace Kowannensu ya Shiga Dakinsa yayi
Shirin Kwanciya,Toh ganin kamar ya samu Sauki ne yasa Suka mai sallama Kowanne ya
Shige Dakinsa ya Kwanta Shi Kuma ya Koma sama yana Mukurkusu.
********
Karfe 1:50am na Dare ya Farka da Wani Azababben Ciwon Mara,Dafe Cikinsa yayi yana
Salati tare da Kiran Sunan Allah Abu kamar Wasa karamar Mgana Ta zama babba,Domin
Tun yana iya Mikewa Har yazo Yaji ya gagara,Jikinsa ba Inda baya Rawa,Saboda Tsabar
Sha'awa da Muradi,wani irin Murda Cikinsa keyi kamar mai Naguda Dakyar ya iya Bude
Kofar Bedroom dinshi ya Fito yana Dafe Dafen Bango yana Sanye da Dogon Wando ne
baki Jikinsa ba Riga,Haka ya Dinga Dafa Karfen Steps din matattakalan Benen,yana
Cize baki Acikin Ranshi Yana Tunanin Lalle Dole ya Nemar ma kanshi Mafita kafin Ya
Kashe kansa da kansa Domin Farida bata da Asara.
Da Dafe Dafen nan ya Karisa Shiga Kichen yafara Neman Kanwa Daidai Lokacin Kuma
Mufeeda Ta Shigo Kichen Din Tana Sanye Da Karamar Rigar Barcinta Wacce Cikin Wanda
Farida ke Siya musu ne ita da Basma Rigar iyakarta Cinyarta gata Karamin Hannu
gareta Tana da Budadden Gaba,Ga Ta Sharara ,komai na Jikinta ana gani Harda Yan
Nonuwanta da Suka Fara Tasawa Ta Cikin Rigarta.
Kishi ne ya Fito da Ita Tazo Frigde din Kichen Din Daukan Ruwa,kichen din Didim ne
Sakamakon bai Kunna Wutar Kichen din ba,Kuma bata ji motsi ba Don Azaba yasa ya
Sulale Anan Tsakar Kichen din Rike da Ciki yana Mukurkusu,Hannu ta Sanya ta Kunna
Wutar Kichen din Haske ya Gauraye Ko"ina Da Farko Bata ganshi ba Sai da Taji Ta
Shuru kafar kamar na Mutum yasa taja baya tana Zaro Ido Jikinta yafara Rawa Cike da
Tsoro Bata gane Tahir bane Kokarin Juyawa Take ta Fita da Gado,Ya Dago kanshi Cikin
Wani yanayi yana kiran Sunanta.."Mufeeda....."Yafada Cikin Muryan Ciwo da
galabaita.
.
Cak ta tsaya kafin ta Waigo Tana kallonshi,Zabura Tayi ta Isa gareshi da Sauri
Tunda ta Fahimci Daddy ne,Durkushewa Tayi batare da Tunanin Komai ba Ta Rikoshi
Tana Fadin"Innalillahi Daddy,Ciwon ne ya Tashi...?"Take Fada Cike Da Tashin Hankali
Tana Rikoshi ACikin jikinta,Shiko Tahir Wani Shock ne ya Bi Ilarahin Jikinsa
Lokacin da Mufeeda TaRikoshi Tana Kokarin Sanyashi Ajikinta Mahood dinsa ta Kara
Mikewa kamar Zata Fito Fili,Jikinsa ne yakama Rawa yana Cije baki ya sauka daga
Jikin Mufeeda yana Fadin"Dubamin kanwa Mufeeda plz..."Yafada yana Tamke Baki kamar
mai Nakuda.
Da Hanzari ta Mike Jikinta na Rawa Ta Bude Drower da Kanwar Take tana Dubamai
Ammh sai taga yakara Kwanciya akasar Tayels din Kichen din yana Rike da Ciki,sai ta
bar Dubawan Ta kara Nufoshi,Ja da baya yake da Jikinsa Ammh bata Fahimta ba Tana
Zuwa Ta Dago kansa ta Aza bisa Cinyarta Ta Fashe da Kuka tana Fadin"Daddy meya
sameka...? Cikinka ne ke Ciwo na Kira maka garzali yazo yakai ka Asibiti..? tafada
Tana kallonshi Runtse Ido Yayi yana Girgiza mata kai Kokarin Tashi yake Ta kara
Rikoshi Tana Fadin'Nan ne ke Maka Ciwo Daddy..? Tafada tana Dora lallausan Hannunta
Bisa Cikinsa Wani Yam,Yaji har saida ya Dauke Numfashi kafin ya Dawo Dashi baisamu
Zarafin mgana ba Ta Fara Dannamai Cikin ,tana Fadin"Sannu Daddy zai bari yanzu Haka
Innata keman in ina Ciwon Ciki.."Tafada Hawaye na Zubomata na Tsausayinshi Kokarin
Ture Hannunta yake Ammh Ita bata Fahimta,Saboda Yadda Jikinsa Ke Rawa Zuciyarsa na
Kokarin Sakashi Aikata Abunda zai yi Nadama Har karshen Rayuwarsa.
Kokarin mikewa yayi ganin Mufeda Zata Rabashi da Numfashi Saboda Hannunta Dake
kan Cikinsa Bakaramin Wani yanayi ya sanyashi ba,Rikosa Tayi ganin yana Neman
Faduwa Kallonta yayi kafin ya Runtse Ido ganin Duka Kirjinta yana Waje ne Rigar
Barcin Ta yi gefe Kuma bata da Bra,Runtse ido yayi da Sauri Cikin Wani yanayi
Yafara Tafiya Sai kawai yayi Luu zai Fadi da Hanzari Ta Rikoshi Tana mai Sannu
ganin Haka yasa Tace"Daddy Daki zaka koma..? Muje na Taimaka maka kaga bazaka iya
ba.."Tafada Cikin Wani yanayin Tsausayi Bai mata gardama ba ta Rikoshi Har Zuwa
Sama Cikin Bedroom Dinshi Tana mai Sannu Sun Kariso Zuwa Gefen gadonshi yana
Kokarin Kwanciya Kawai Sukayi Luu Suka Zube bisa gadon Ta Fado kanshi Tunda Jikinsa
ba Karfi Tana Fadowa Jikinsa Komai ya Rikice mai,itako kamkameshi Tayi Cike da
Tsoro Azatonta Kasa Zata Fadi,Sanda Nonowanta Duka Daki Kirjinsa sai da ya Dauke
Wuta na Wasu Mintina,tuni ya Fita Daga Hayyacinsa ya Mika Duka Hannayensa ya Zagaye
Kugun Mufeeda Dashi Wacce Ke Kokarin Tashi Ganin ya kamkameta ne ya Matseta yana
Sauke Numfashi Da Sauri Da Sauri ya Tsorata ta ga Wani Abu Dataji mai kama da Iccen
Daga kasanta yana Tunkuri ta sai Tsoro ya kamata ta Fara Kokarin Kwace Jikinta Ammh
Ina Tahir yagama Fita Daga Hayyacinsa Domin Alokacin ya Manta da Mufeeda ce Abun
Kawai Shedan da Kwakwalsar ke Nunamai Farida ce
Shiyasa Cikin Zafin Nama ya maidashi kasanta,Zaro Ido Mufeeda Tayi Ta Bude Baki
Cike Da Tsoro Zatayi mgana ganin yadda Tahir ke Tusa kanshi Cikin Wuyanta yana
Sumbatarta Cikin Fitar Hayyaci Kalmar.."Dadd....'Bata gama Fita Daga Bakinta,taji
ya Hade bakinsu Waje Daya yana Sumbatarta Cikin Fitan Hayyaci Hawaye Suka Barkema
Mufeeda Domin Duk da kananan Shekarunta ta Fahimci Kudurin Tahir Akanta Ammh Duk
iya Motsin Motsinta bata Tsiraba Haka Tahir ke Sarrafa Sassan Jikinta Cike da
Kwarewa da Kuma Fitar Hayyaci Kukan Datake da Shuren Shuren Kafa Su suka kara mai
kaimin,cikin Azama ya Zare Wandon Jikinsa Hade da Boxers Rigar Barcin Jikin Mufeeda
ko Tuni ya Cireta yayi Wurgi da Ita,tana ji ya Bude Kafarta da karfin Tsiya ya Fara
Turamata Abun nan Cikin karamin Gabanta Wani Azaba Taji da Radadi tana Kokarin Ihu
Ammh Kuma ya Tare mata baki Danashi Shiko bai Cikin Hayyacinshi ganin ya Tura taki
Shiga yasa yakoma da baya yakara Speed ya Danna kai,ya Shiga da karfin Tsiya Wanda
Sai Mufeeda Tayi Suman Mintina Numfashinta ya Dauke kafin ya Dawo Kuka Take da
Hawaye na Azaban Datakeji Wanda bata taba Jiba,Shiko Shiganshi ya kara Taimakamai
Wajen Sake Fita Daga Hayyacinsa Wani Dumi yaji Lokacin daya Shiga sai ya kankameta
yakara Tura kai yana Fadin"Ya illahi..."Riketa yayi gam yafara Driving dinta Cikin
Wani yanayi na Fitar Hayyaci Lokaci Daya Dadin Daya Ziyarceshi Ya Nemi Zautashi
baisan Sadda ya Saki Bakinta ba yafara Sambatu yana Fadin"Farida...Wayyo Allah na
Karki Kasheni Kin kara Dadi...Na bani ni Tahir...Zan Mutu wayooo...Allahna..! Yake
Fada Cikin Wani yanayi Lokaci Daya yana Cigaba da Hakarta da Zafi Zafi kamar ya
samu babbar Mace.
*Aisha Alto..*
*Anitha...*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
```Littafin NANNY... Bana kudi bane,Free Novel ne Daga Farkonshi har zuwa
karshe,Duk Wanda yace Muku na Kudi ne Dan Damfara ne,Nanny Free Novel ne,ga
Masoyanmu Wad'anda Suka Siya Littafanmu,MALIKA MALIK,ZAMAN GIDANMU,da INDO
AISHA...SON SO FISABILLAH```
*BABI NA TARA*
Tsawon Mintina Talatin ya kwashe yana Abu Ɗaya, Ni'imar Mufeeda Da Kuma Wani garɗin
Daɗin Budurci shi ya ƙara Rikita Tahir ya Dinga Haƙarta baisani ba Samabatu kuwa,
baisan iyakar Abunda bakinsa ya Faɗi ba.
Itako Mufeeda Tun Lokacin Daya samu Kofar Shiga yadinga Turamata da ƙarfi
Numfashinta yanemi Ɗaukewa, Kuka shaɓe shaɓe da Majina lokaci Ɗaya Taji Duhu ya
mamaye Idanuwanta Tun Tana iya Jin meke Faruwa Har Jinta da ganinta ya Ɗauke ba
tare Da Tahir ya ankare ba gaba ɗaya Jikinta ya saki bata Numfashi.
Lokacin da yazo gangara ne ya ƙanƙameta Tsab Kamar Zai Tsaga Ƙirjinsa ya maidata,
Nan da nan ya Shiga mata Ɓarin Madara, kafin ya saketa ta koma yaraf bisa gado
Shikuma ya Bita Shima ya Faɗa Bisa kanta Bayan ya sakar mata Nauyinshi Yana Sauke
Tawagayen Ajiyar Zuciya kamar Wanda yayi gudun Tsere .
Ji yayi maranshi Sakyau ta saki Farin ciki ya Cikashi Domin Ji yayi kamar yana yawo
Agajimare Saboda Daɗi Amma Sai me ƙwaƙwalwarsa ne ta Shiga Tunano masa Abunda ya
Wakana da Wani Uban Razana da Ɓarin Jiki da gaggawa ya Miƙe Daga Jikin Mufeeda
Jikinsa da Zuciyarsa na Rawa Lokaci Ɗaya, Dama already Ɗakin Hasken Dum light ne,
Cikin Fitan Hayyaci ya Saka Hannu, ya kunna Wutar Ɗakin Lokaci Ɗaya Haske ya
Gauraye Bedroom Ɗin.
Baya Tahir yaja Cikin Bugawar Zuciya, lokacin Daya ci Tozali Da Mufeeda kwance Akan
gadonshi ba yarda take da alama bata Numfashi, Hannu ya Ɗora Akai kamar Zuciyarsa
zata Fito Waje ya ƙarisa bakin gadon yana kallonta Idanuwansa na Rufewa Saboda
Ruɗewa Hannunta guda Ɗaya ya Riƙo kafin ya sakeshi sai yaga ya Tafi Luu ya Faɗi,
Cikin Ruɗewa yabi Zanin gadon da kallo da Wajen kafafun Mufeeda Yaga yadda Jini ya
ɓata Wajen kamar an yanka Wata karamar Akuya, Gata Tsirara Domin ga Rigar Barcinta
nan,ayashe a ƙasa ko bai Tambayi kanshi ba ya Riga ya sani Cewa Mufeeda ce yama
Wannan Aika Aikan.
Baya Tahir ya Dinga ja Jikinsa na Rawa kamar Wanda yaga Abun Tsoro Kansa ya Dafe
Duk Sanyin Dake Ɗakin na Ac Zufa ke Keto mai, Hannu ya Ɗora bisa kai yana Fadin
"Innalillahi Wa'inna Illaihirraju'un..Me na Aikata ni Tahir...? Wani Irin Abu ne ya
Shiga kaina na Haikema yarinyar Dana ke kallonta Tamkar 'Yata Basma, itama take
kallona Amatsayin Mahaifinta, Kaico na...! Kaico na...Ni Tahir na cuci kaina Wayyo
Allah na! ..."
Ya faɗa yana Zubewa A ƙasa Kan Gwiwoyinsa Yana Riƙe kansa Yana girgizawa Lokaci
Ɗaya Cikin Wani Tashin Hankali, Wata Zuciya Ce Take Tunasar Dashi Tahir zama bai
ganka ba Kada yazo ka kashe yar Mutane, Tuna Haka yasa Yayi Zumbur ya miƙe, sai
lokacin ya Lura Tsirara yake, Da Hanzari ya Ɗauki Wandonsa Wanda ya gani nan yashe
A ƙasa, da Hanzari ya Isa ga Mufeeda yana Jijjigata Idanuwansa Sun sauya kala Sunyi
Jajir Amma ko Motsi Mufeeda bata yi Zuciyar Tahir Ta Sake Tsinkewa Hankali Tashe ya
juya ya Faɗa Bathroom d'in Dake Cikin Ɗakin ya Tara Ruwan Zafi A bath ko'ina na
Jikinsa na Rawa Aguje ya Fito kamar Zai kifa bai tsaya Shawara da kowa ba ya saka
Hannu ya Cicciɓi Mufeedan, Ya Shiga Toilet da Ita Da Hanzari, bai direta ko'ina ba
sai cikin Jacuzzi inda ya Tara Ruwan, bayan ya Toshe Rariyan.
Lokacin Data jita Cikin Ruwan Zafi sai Ajiyar Zuciya ya Ƙwace mata amma bata buɗe
ido ba Sai Mutsu mutsu Take alaman Dai Tanajin ba Daɗi, ruwan ya ɗiba ya Shafa mata
afuska yana Kiran Sunanta A ruɗe, Da Kuka ta Buɗe Ido Lokaci Ɗaya Tana Neman Zabura
Saboda yadda Wani Azaba da Raɗaɗi Suka Ziyarceta Jin Ruwan Zafi na Ratsata, Hannu
yasa Cike da Nadamar kanshi ya maida ita Cikin Ruwan yana kallon Fuskarta, cikin
Azaba da Raɗaɗi Mufeeda ta fara Buɗe Kumburarrun Idanuwanta ta Saukesu kan Tahir,
ƙuri tayi mai kafin Abunda ya Faru ya fara Dawo mata Daki Daki.
Wani Baƙin ciki ne Mai Haɗe da Wani Kuka ya Tasoma Mufeeda Da Hanzari Ta Runtse ido
Bata son ganin Fuskar Tahir, Fuskar Data Ɗauke Ta mai Daraja mai kima, mai kamala
da Dattako, fuskar Datake kallonta amatsayin Mahaifinta yau Shine ya Keta mata
Rigar Mutumci yaci Zarafinta ya kafa mata Tarihin da Har Abada bazata Manta ba,
idonta na Runtse Tana Tsiyayan Hawayen Baƙin Ciki da Azaba mai Tsanani, Shiko Tahir
na gefe yana kallonta ganin Ta Runtse Ido yasa Zuciyarsa Ta Tsinke Shima Sunkuyar
Dakai yayi yana Kiran Sunan Allah.
Kan gadon ya maidata bayan ya yaye Zanin Gadon, ƙasa ta Sulale Tana Kuka idonta
Akulle gam bata Ƙaunar ta Buɗe Idonta ma, Shima Tahir Durƙushewan yayi yana
kallonta Zuciyarsa kamar Zata Fashe ya fara magana Cikin Raunin murya.."
Mufeeda..." Ya kira Sunanta Cikin Bugun Numfashi Cak Ta Tsayar da Kukanta amma Bata
Ɗago Ta kalleshi ba.
Ganin Haka ne yasa ya saki Ajiyar Zuciya kafin ya cigaba Da Faɗin "Ki yafemin
Mufeeda, Ba laifi na bane..Bansan yadda Akayi ba..Bansan yaushe Haka ta Faru ba...
Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un..wallahi yau nayi Nadamar Zuwa na Duniya, bansan
dawa Ni ido zan kalli Mutanen Duniya in Sanar dasu nayi ma yarinyar Dana Riƙeta
Tamkar yata Fyaɗe ba..kaicona Ni Tahir nayi Nadamar Rayuwata Farida ta Cuceni ta
cuci kanta da Zuri'armu Gaba ɗaya Duk Halin Dana Tsinci kaina Aciki wallahi Itace
Sila Itace Sila..." Ya faɗa kawai yanajin Kuka ya Ƙwace mai Jin yana Kuka yasa
Mufeeda ta Buɗe Kumburarun Idanuwanta Ta Bishi da kallo Lokaci Ɗaya Kuma Taji
Tausayinshi ya kamata ganin yana Kuka Duk da Halin Dayake Ciki Sai da tace
"Ka..ka...Da.daina Kuka Daddy...bazan Faɗama Kowa ba.." Ta faɗa Itama tana Sakin
Nata marayan Kukan.
Jin Abunda Tace ne yasa ya Ɗago da Sauri ya Riƙo Hannunta yana Faɗin "Da gaske kike
Mufeeda bazaki Fadama kowa ba...?" Ganin yadda Yake Rawan Jiki ga Hawaye na bin
Fuskarshi yasa Ta ɗaga mai kai kafin tace "Ka..kaini Wajen Innata..Wajenta zani.."
Iska ya Furzar kafin yace "Zan kaiki ki kwantar da Hankalinki kibar Wannan Kukan
kada gobe su Basma su Fahimci Wani Abu ya Faru, yanzu bari na Shiga nayi Wanka na
Fito Hau gado ki Kwanta naji Jikin ki Temperature yayi yawa Kinji ki jirani na
Fito.." Ganin yadda ya Ruɗe ne yasa Ta Ɗaga mai kai da Hanzari ya saki Hannunta ya
rarumin Zanin gadon daya baci da Jini ya Faɗa Toilet yana jin Tsanar kanshi, da
kallo Ta bishi Sai da ta Tabbatar ya Shiga kana ta fara Rarrafe ta jawo Rigarta ta
sanya, tana Neman Hanyar Fita Lokaci Ɗaya tana Zubar Ƙwallah Saboda Azaban Dake
cinta ta Tsakiyarta kamar Wacce Aka Tusa mata Wani Katon Abu ya Tokareta...
Da Rarrafe ta Fito Daga bedroom Ɗin ta Kuma gangaro Steps d'in Benen Tanayi tana
Kuka Har Ɗakinta, Allah ya Taimaketa Basma ko Bassam ba Wanda ya Fito, Da Rarrafen
ta Ƙarisa Cikin banɗakin Dake Ɗakinta ta Haɗa Ruwa Mai Zafi Ta Shiga Ciki Tana
Cigaba da Kuka mai Cin Rai Tana Sane Cewa Wannan Abun Tahir yayi Toh sai fa sai
tayi Wankan Tsarki Domin A makarantar islamiya an Sanar Dasu Duk Ranar da Namiji ya
kwanta Dake sai kinyi Wankan Janaba kuma ko ba Haka ba Lantana Ta Sanar da ita
Ranar Daren Farkonta Haka Mijinta yayi mata, Amma ita yau gashi ba Miji ba Saurayi
ba Daddy Shi ya Keta mata Budurcinta yau ya maida Ita mace..
Tana Kuka da Komai tayi Wankar Tsarki ta Fito Tana Dafe bango, Lokacin Zazzaɓi ya
Rufeta tana Rawan Sanyi, Da Hanzari ta Faɗa kan gado taja bargo Ta Rufe Jikinta
tana Rawan Sanyi, Shiko Tahir Wanke Zanin Gadon yayi ya Shanyashi Acikin Bedroom
d'in kafin yayi Wankan Tsarki ya Fito sai dai yana Fitowa yaga Wayam ba Mufeeda
Hankalinsa Tashe ya Zura Wata baƙar Jallabiya ya Nufo Ɗakinta Ajiyar Zuciya ya
Sauke sanda ya ganta Lulluɓe Cikin bargo baya yaja Cike da Damuwa kafin ya koma
sama Yana mai Nadama.
Darduma ya Shimfida ya kabarta sallah dama already ya Ɗauro Alwala, Sallah yayi
Raka'a goma Sha uku Haɗe da Shafa'i da Wutiri, Kafin ya Ɗaga Hannuwanshi Sama yana
Roƙon Gafaran Allah, Yana yi yana Kuka kamar ƙaramin yaro baƙin ciki da Nadama
Sunga ma Lulluɓe Tahir, Bayan ya idar karatun Qur'ani ya dasa gabatowar Asuba, kana
ya Tashi Daga kan Sallayar ya Sauko Ƙasa Idanuwansa Sun Masa Nauyi, Ɗakin Mufeeda
ya Leƙa yarda ya Isketa sai gabansa ya Faɗi Tana Kwance Cikin Bargo Tana Rawan
Sanyi Cikin Hanzari ya ƙarisa gareta bayan ya yaye Bargon ya Taɓa Goshinta yaji
Zafi Sosai Ruɗewa yayi Cikin Fitan Hayyaci ya koma Ɗaki ya Ɓallo mata Paracetamol
da Kuma Pain Killer yazo ya tada Ita tana Rawan Sanyi gefe Ɗaya Kuma Tana Tsiyayan
Hawaye, ya bata Tasha Ta Koma ta Kwanta.
Ranar dai Barci baiga idon Tahir ba Shi ya Tashi Bassam Suka Tafi masallaci Koda
Suka Dawo Sai da ya leka Dakin Mufeeda ganin Ta samu barci ne yasa Hankalinsa yadan
Kwanta sakamakon baya Cikin Natsuwarsa yasa breakfast ɗinsu ma Garzali ya aika yayi
musu Takeaway Koda Basma Ta Fito Cikin Shirin kayan makaranta ita da Bassam, Tahir
bai bari Sun Tambayi Mufeeda ba yace musu yau bazataje Sch ba batajin Daɗi, Ransu
baiyi Daɗi ba Suka Juya Zasu Shiga Ɗakinta Tahir ya hanasu Cikin Wani yanayi nan
yace su bari Su Dawo ya bata Magani ta samu barci Inda Ace Zasu lura da Sunga yadda
yake Rawan Jiki kamar baya Cikin Hayyacinsa.
Basu kawo komai Aransu ba Suka Fita Zuwa Haraban gidan bayan Sun karya da takeAway
d'in Da Garzali yayi musu, ƙarfe 7:30am Garzali ya kwashesu Zuwa Makaranta
Shikanshi Da baiga Mufeeda ba sai da ya Tambayesu Suka ce mai batajin Daɗi Fatan
Samun Lafiya yayi mata kafin ya kaisu Makaranta ya Ijiyesu ya Kamo Hanyar Gida yana
Tunanin Zai kai Tahir Office.
Shi ko baida Cikakkiyar Natsuwa Hankalinsa A tashe yake na Abunda ya Faru kada Kuma
Wani ya ɗau sanau, Ganin Jikin Mufeeda Har da Safen Arikice yasa bai Fita Office ba
koda Ishaq yajisa Shuru ya kirasa Awaya nan yake Shaida mishi bazai Samu Fitowa ba
baya jin Daɗi, Sannu yamai kafin Suyi Sallama, Tahir Wuni yayi Tashin Hankali Domin
Zazzaɓi yaƙi barin Mufeeda ko Abincin da Garzali yasiyo ta kasa Ci Komai ya bata
sai ta kauda kai Tana Kuka Tana Kiran Sunan Innarta ya rasa yadda Zaiyi Tsoronshi
Ɗaya kada Farida Ta Dawo ta Fahimci Abunda ya Faru Domin Ko makaho Ya Shafa yasan
Cewa Mufeeda ta Illata ganin ko iya Tafiya ma batayi Tana Kuka Tahir nayin na Zucci
Suna Cikin Wannan Halin ne yaji sallamar su Basma sun Dawo Daga Makaranta Koda yayi
Wuf ya Fito Daga Ɗakin Mufeedan Sai Suka ci karo da Su, Ganinshi Hankalinshi Tashe
sai su ka Tura kai Ɗakin Azatonsu Jikin Mufeedan ne ya Tashi Shiko kasa Komawa
Cikin Dakin yayi ya Tsaya anan Yana Kiran Sunan Allah yana Fatan Kada Su basma Su
Fahimci Wani Abu.
Toh dai basu Fahimci komai ba, Illah Sun Tausayama Mufeedan Ganin yadda Take kuka
Tana Kiran Sunan Innarta, Basma kamar ta mata Ƙwallah Ta Fito Daga Ɗakin Tana Faɗin
"Daddy Akai Aunty Mufeeda Asibiti Jikinta kamar Wuta.." Ajiyar Zuciya ya Sauke
kafin yace "Za'a kaita Basma ku Shiga ɗaki ku cire Uniform ɗinku ga Takeaway chan
Garzali yayo muku kunji.." Gyaɗa kai suka yi kafin Kowanne ya Nufi Ɗakinsa
zuciyarsu ba Daɗi Domin Sun Shaƙu da Mufeedan Sosai.
Suna gama cin Abinci Sukayi sallah Da Farko Basma taso Ta Zauna da Mufeeda amma
Tahir yace maza Ta Shirya ta tafi makaranta Dole Hakanan ta Shirya Ita da Bassam
Garzali ya Kwashesu Zuwa Islamiya, Har Suka Taso Daga makaranta Tahir baisamu
mafita ba, Sun Shigo Kenan sai ga Iya Ta Dawo Wanda ya Faɗarma da Tahir gaba, Basma
da Bassam Suka Rungumeta suna Murna Itama Cikin Farin cikin Ganinsu Take Amsa
gaisuwansu kafin Su Dakata ta Rankwafa Tana gaida Tahir ya amsa Cikin Wani yanayi
na karaya, yana Ƙara yi mata gaisuwa.
Mufeeda Ta fara Tambaya kafin Farida nan Basma tace Tana Ɗaki Tun Jiya bata da
lafiya, Ai kafin Tahir yasamu Mafita Iya da Basma Sun Nufi Ɗakin Mufeeda Zuciyarsa
ce ta karye ya Nemi Kujera ya Zauna yana Dafe kai Bassam ne ya katseshi da Faɗin ya
Tashi Su Tafi masallaci Shidai Har Aka idar da sallar mangariba baya Cikin
Natsuwarsa Saboda Zullumi bai jira Sun Sallaci Issha'i ba kamar yadda Suka saba Ya
Riƙo Hannun Bassam Suka Dawo Gida Zuciyarsa na Bugawa Saboda Fargaban kada iya
tagano Abunda ya Faru Ta Matsama Mufeeda Har Sai ta gaya mata Abunda ya Faru,
Bassam ko tausayin Daddynsa yakeji ganinsa Haka Kamar Wanda ƙwai ya Fashema aciki
sai ya yi Tunanin ƙila Jikin Nashi ne Har yanzu.
Suna Shigowa Falon Suka Ci Karo da Iya ta Fito Daga Ɗakin Mufeeda Ɗauke da Ƙaramin
Kofi Ahannunta tana ganinsu Tace "Yauwa gama Alhajin nan..." Faɗin Haka da Iya Tayi
sai da gaban Tahir ya Tsinke Zufa ta fara Ketomai Tsura mata Ido yayi yana kallonta
Domin miyan bakinsa ya ƙafe, bata Lura da Yanayinsa ba tace "Alhaji gaskiya ya
kamata Akai Mufeeda Asibiti Zazzaɓin Jikinta yayi Zafi Sosai Inajin Maleria ce Ta
Shigeta.." Ɓoyayyiyar Ajiyar Zuciya ya Sauke kafin yace "Eh dama Dawowar Danayi
kenan, Ta fito muje Adubata yanzu..." Ya faɗa Cikin Sanyin Murya Kai Iya ta kaɗa
kafin tace "Yadai kamata Alhaji.." Ta faɗa Tana Komawa Ɗakin Mufeedan.
Iya ta Umarci Basma Data Ɗaukoma Mufeeda Hijabinta ita Kuma tana Ƙoƙarin Miƙar Da
Ita Noƙewa Mufeeda Tayi Tana Rawan Jiki Tace "Bazan iya Tashi ba Iya ki barni
Akwance Don Allah..." Fuskarta Iya Ta kallah Tana Faɗin "Sannu Daurewa zaki yi
Alhaji ne zai kai Ki Asibiti Adubaki Mufeda.." Jin Abunda Tace ne yasa Ta ƙara
Ruɗewa, Bata da Kwanar Amin Iya ta Tsayar da Ita da ƙafarta tana Cema Basma ta Bata
Hijabin Hannunta, Mufeeda Ji Tayi Ƙafarta na Rawa Saboda Wani Hucin Azaba Dake bin
Tsakiyar Kafarta Tana Ƙoƙarin Sulalewa Basma da Iya Suka Riƙota Iya ta Sanya mata
Hijabi saman Doguwar Rigar Jikinta, Suna mata sannu Duk da Suna Riƙe da Ita amma
yanayin Takunta yadda Take Gwale ƙafa sai da ya bama iya mamaki ta kalleta tana
Faɗin "Mufeeda meya sameki ne ga kafarki ba Daidai ba Kina Tafiya Wani Iri..?"
Iya ta Faɗa Tana kallonta Cike da Mamaki daidai Lokacin Da Suka Fito Falon, kuma
maganar a kunnan Tahir, wanda Yaji jiri ya Ɗaukesa ya Ɗago yana kallon Mufeeda
Zuciyarsa na Harbawa da Sauri Sauri Mufeeda Wacce Iya ta sakama ido, kafin Ta Waiga
Tana kallon Tahir yadda ya Sauya cikin Kwana Ɗaya yasa bakinta na Rawa Tace "Ba..ba
komai.. ɗazu ne nazo Fitowa Daga banɗaki Shi..shine Santsi ya ɗebeni na Faɗi na
Buge ƙafana.." Ta faɗa Tana Runtse Ido Hawaye na Zubo mata, ajiyar Zuciya Daga
Tahir har Iya suka Sauke Iya ce tace "Ashha Sannu.. ƙila Targaɗe Kikayi.." Ta faɗa
Tana ƙara Riƙota su suka Fita Da Ita Har Haraban Gidan Saboda Tashin Hankali ko
Ɗaki Tahir bai koma ba Da Jallabiyan Jikinsa ya Shiga Mota Daidai Lokacin da Iya da
Basma Suka Shiga Motar, Gabansa ne ya Faɗi, amma sai ya Danne ya juya yana Ce musu
Su bari yanzu zasu dawo su Zauna Su kula da gidan, ba yadda Suka iya Suka Fito Daga
Motar Suna ji Suna gani Garzali yaja Motar Suka Fice Daga Haraban gidan..
.
Iyali Hospital iyalanshi Keda Fayel Amma gudun tonon Asirinshi yasa Suka Nufi
Garkuwa Hospital, Suna Zuwa Aka karɓeta suka kuma yi sa'a Dr Hadiza ce kan Duty
Ranar Haka ta Fito tana Faɗa Lokacin data ci karo Da Mufeeda Office Ɗinta ta Kira
Tahir tana Tambayanshi Suwaye suka ketama yarinya ƙarama Mutumci Suka mata Wannan
Illar, Fada Take Sosai, Zuciyar Tahir tashi ga Rawa Da ƙyar ya iya Faɗa mata ba'a
san ko Suwaye ba, Nan dai Tace Zasu Riƙesu Domin Mufedan Tana buƙatar Kulawa Saboda
An Jimata Rauni Sosai So Zasu Riƙeta Har Zuwa nan da Sati Ɗaya Sugani, Tahir yaji
Daɗin Haka Sosai ko banza Asirinshi Zai Rufu, bai bar Asibitin ba Sai Wajen 10pm na
Dare Har Mufeeda ta samu barci bayan ansaka mata Drip da Wasu Allurai, gida Suka
Dawo Shi da Garzali Wanda baisan Abunda Ke Faruwa ba, inda Allah ya Taimakeshi
Asibitin basu bukatar masu jinya, koda Ya Dawo su Basma basu Kwanta ba Suna Jiran
Dawowarsu nan yake sanar dasu an bata gado, sun janjanta Sosai yace Suje su Kwanta
gobe da Safe sai Suje Su Dubata, Iya ma sai Fatan Allah yabama Mufeedan Lafiya Take
har Tashiga Ɗakinta.
Tahir ko bedroom ɗinsa ya Shiga Kafin ya Faɗa Toilet ya sakarma kanshi Shower yana
kuka zucci jikinsa na Rawa inya Tuna kalaman Dr Hadiza inda Take mai Faɗa bayan
yace Shi mariƙin Mufeeda ne, Da Har yayi Sakaci aka keta mata Mutumci Haka..? Yaya
zataji in Taji labarin Shine Da Kanshi ya Aikata mata Haka..? Tun yana Kukan Zucci
Har ya Fito Sarari, Dakyar yayi Wanka ya Ɗauro Alwala ya Fito ya Saka kayan
barcinsa Riga da Wando, Ya Shimfiɗa Darduma ya Tada Sallah, Issha'i yayi kafin yayi
Shafa'i da Wuturi ƙaramin Alqur'aninsa ya ɗauko ya Tankwashe ƙafa ya fara karatu
Cikin Rawan Murya yanayi yana Kuka, kukan Nadama Da Kaico da Rayuwarsa.
*Anitha*
*Aisha Alto..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
*BABI NA GOMA*
Ranar barci ko ɓarawo bai Sace Tahir ba, kuka kuwa yayishi kamar Ranshi Zai Fita
Daga ƙarshe ya Haƙura ya Fauwalama Allah komai ya kuma Ɗaukeshi A Matsayin
Ƙaddararshi, Amma yasan Duk Abunda ya Faru Dashi Farida ce Sila kana Goggo Abu
Da'ace Sunyi Duba da Lalurarsa da Irin Halittarsa, Da Duk Haka Bata Faru ba Amma
yana Ta Neman gafaran Allah, sai dai Kunya da Nauyi Sun Cikamai Ƙirji Sun Hanashi
Sukuni.
Shi yazo ya tashi Bassam Suka Tafi masallaci Sallar Asuba basu Dawo ba sai Wajen
Bakwai Saura Koda suka Shigo Iya ta gyara Ko'ina Tana Kichen Tana Musu Abun Karyawa
Bedroom ɗinsa ya shige ya Zauna Kawai ya Zabga Tagumin Makomar Rayuwarsa yadda ya
Cuci Rayuwar Yarinya kamar Mufeeda.
Su Iya ko tana gama Abun karyawa Ta ɗorama Mufeeda Abunda Zata Tafin mata Dashi
Asibiti Tunda Tahir yace in Sun karya Garzali zai Tafi Dasu, Shiko yana Cikin ɗaki
yama kasa Fitowa Bawai bayajin Yunwa bane A'a yanaji Domin Rabonshi da Abinci Tun
Jiya da Dare, Amma Cikinsa ne A Chushe bayajin Akwai Abunda Zai samu Wajen Zama ga
bakinsa ba Tes Kwata kwata Ɗaci ɗaci ma yakeji Shikanshi Damuwa ta Saukar mai Da
Zazzaɓi mai Zafi kan gado ya Kwanta ya Lulluɓa da bargo Haka Basma da Bassam Suka
zo Suka iskeshi ya Dunƙule yana Hawaye, yanajin Muryansu Suna Kiranshi yayi Saurin
Share Kwallah ya Fito da kanshi yana Ƙoƙarin Daidaita kansa.
Basma ce Ta ƙarasa Tana Zama Gefen gadon Lokaci Ɗaya Take faɗin "Daddy jikin
ne...? Ta faɗa Cike da Tausayawa, Kai ya girgiza musu kafin yace "No ba sosai bane
Basma, nasha magani da nayi barci zan Warware, kun Shirya ne..." Bassam ne ya Ɗaga
mai kai yana Zama Shima gefen Basma Fuskarshi ta bayyana Damuwar Dayake Ciki, Cikin
Raunin Murya ya Furta..." Daddy What Wrong With you ne? bama jin Daɗin Ganinka A
haka in Momy bata sonka Why not ka samo mana Wata Second Mom ko Basma...?" Ya faɗa
yana kallonta, Saurin Kuka ne da Ita sai ga Hawaye Shar ta gyaɗa kai tana Faɗin "Eh
mana Daddy, Momy tana Barinka kana Wahala bamai kula dakai ka ƙaro Aure plz kasamu
Wacce Zata Dinga Zama dakai kullum muma Mu samu Mommy Wacce Zataso mu sosai Fiye da
Momy.." Ta faɗa Kuka na Ƙwace mata ta Kifa kanta Jikin Tahir tanayi, Hannu ya saka
yana Shafa kanta Dake Cikin Hijabin yanajin Ƙaunar 'ya'yansa Har Cikin Ranshi Duk
da ƙananan Shekarunsu Sun Fahimci Damuwar nashi Acikin Ranshi Faɗi yake dama dama
ace bai Aikata Abunda ya Aikata ba, Amma yanzu da Wani ido Zai kalli 'ya'yansa yace
Shine ya Ketama Mufeeda Mutumci.
Cikin Sigan Lallashi yake Faɗin "Shiii..Is Ok karku damu Kunji na samu Sauƙi
Sosai Ku Tashi Ku Tafi Garzali zai kaiku Room 9 Take kunji.." Gyaɗa kai Basma Tayi
kafin Ta mike Tana Share Kwallah Hannunta Bassam ya Riƙo Kafin su Duka Dukkansu Su
Sakarma Tahir kiss a Goshi, Lumshe ido yayi Idanuwansa Sun Cika da Kwallah Cikin
Raunin Murya yace "Take care..." Suka Fice Suna Ɗaga mai Hannu Suka Fita Wani Kuka
yazo mai ya Shige Cikin Bargo yanayi kamar ya Shiɗe Saboda Takaichi So yake ya Buɗe
Ido yaga Duk Abunda ya Faru mafarki ne Amma Ina bakin Alƙalami ya Riga Daya bushe,
Abunda yasa Ma ya bari su iya suka Tafi Asibitin bashi da mafita ne don ya cigaba
da Hanasu Zuwa Zasu Zargi Wani Abu, shiyasa yakira Dr Hadiza da Safen nan, dayake
sun karɓi Numbarn Juna, ya Roƙeta Akan Don Allah mahaifiyar Mufeeda Zatazo Dubata
koda Wasa Kada Ta mata Narrated din Abunda ya Faru da Mufeeda baya son Hankalinta
ya tashi Sai daga baya zai sanar da ita, jin Haka yasa Dr Hadiza ta Amince da
Roƙonsa suka Rabu Akan sai Anjima zai Shigo Asibitin.
Su Basma Sun Iske Jikin Mufeeda da Sauƙi Tana ta Barci ga Nurses nata kula da Ita
sai Wajen 1 ta Farka taji Daɗin ganinsu Iya dasu Basma Ta dinga Murmushi, ta daina
Kukan yanzu, Tunda Ta fara jin Sauƙi Gasata Suke bana Wasa ba ga mgaunguna gashi
tana samun Hutu Dr Hadiza Da Tazo da Safe Haka ta Dinga Tambyar Mufeeda ko Zata
Tuna Fuskar Wanda yayi mata Wannan Aiki Ko Zata Taimakesu Su Nemar mata Hakki,
Acikin Ranta Kuka Take Har Asarari, Saboda Bazata iya Buɗe baki ta Furta Wanda ya
Inganta Rayuwarta ne ya Aikata mata haka Bazata iya karya Alƙawarin da tayima Daddy
ba Koza'a Kasheta Akaro na Farko Zata saka mai da Abunda yayi mata Arayuwa, tana
kuka take Cemata bata sani ba Dole ta kyaleta.
Sun Daɗe sai Wajen Uku Suka Tafi bayan Iya Ta Zuba mata Faten Waken Data Zo mata
Dashi Abakinsu ma Takejin Wai Daddy baida lafiya, Tana Shan Faten Waken Tana Sharan
Kwallah Na Tausayin kanta Dana Daddy Domin Dukkansu Sun Faɗa Cikin Wata Jarabawa,
koda suka koma gida Tahir na Kwance Ba yadda yake Ishaq ne da yayi ta Kiran Wayarsa
bai samu ba yazo gidan nan ya iskeshi Kwance Zazzaɓi ya Rufeshi Batare da Tunanin
Komai ba ya Taimaka mai ya Fito Suka Tafi Asibiti.
Iyali Hospital Ishaq ya kaisa Suna Zuwa Suka Riƙeshi Saboda Jikinsa ba ƙwari ga
Jininsa ya Hau Gado Suka bashi bayan Sun Sakamai Drip, Ishaq kamar yama Tahir Kuka
yana Tunanin Duk Damuwar Farida ce Sai da Aka gama Komai aka kawoshi Ɗakin Hutu
kana ya samu Sararin Kiran Farida yana Sanar da Ita Tahir bashi da lafiya gashi
Anyi Addmiting Ɗinsu, Taji ba Daɗi Sosai Ta Dingama Ishaq din kame kamen batama san
Bashi da lafiya ba, Nan tace Insha Allah gobe Zata Dawo Daga Haka Suka Rabu, kafin
ya kira Zahra yana Sanar da Ita ta Turo Direba da Abinci yana Asibiti Zai Kwana da
Tahir, Su Basma kuwa Jin Shuru basu Dawo ba yasa Suka saka Garzali ya Kawosu
Asibitin nan Suka Iske Daddynsu Kwance Kuka Sukayi Tayi Ishaq na lallashinsu bai
Tashi ba Har Suka Koma gida, Iya Tayi Tagumi Tana Jimamin Wannan lamarin Gefe Ɗaya
tana Tir da Halayyar Farida.
Sai Wajen yamma Farida Ta Dawo, Tun Agida ta samu labarin Itama Mufeeda na Asibiti
ga Tahir Abu Lokaci Ɗaya sai ta Fara Zuwa Asibitin Inda Tahir yake Ta Dubashi, taji
Tsoro Ganin yadda Tahir ya Faɗa yayi Wani Sukuku Dashi nan ta Iske Ishaq da
matarshi da 'ya'yansu, Alokacin ne yake Shaida mata Likita yace Damuwace Tayi mai
yawa Sosai Shine ta galabaitar dashi gashi bayason Cin Abinci, Tagumi Farida Tayi
Tana kallon Tahir Cike da Tausayi, Yau ne Rana Ta Farko Dataji bata kyauta ba,
Shiko Tahir bayama son ganin Fuskar Farida Saboda Duk Itace Silan Shiga Wannan
Halin Shiyasa ya Kulle ido Yayi mata barcin karya, Da Farko Ta karɓi Ishaq Jinyar
Shi ya Koma gida Amma Sai Tahir ya Hana yace Ta Koma gida Saboda Mufeeda Shi Ishaq
ɗin ya cigaba da Zama Dashi bata da yarda Zatayi Hakan ta Haƙura suka Fito da Aliya
Kowa ya Shiga Motarshi Zuwa Gida.
Bata samu Zuwa gaida Mufeeda ba sai Washegari dasu Innaro Suka zo Da Ashe da Hakimi
Sun Zo Duba Tahir bayan sun Dubashi ne Farida Ta ƙarasa Dasu Suka Duba Mufeeda
wacce Ta samu Sauƙi Sosai, Koda Suka Haɗu In Farida zata Lura Mufeeda bata iya
kallonta Saboda gani Take kamar Zata Fahimci Abunda ya Faru, Amma ita Farida ba
Wannan bane agabanta Damuwarta yadda Tahir bayason kallonta balle yimata mgana sai
ya zama Dole.
Washegari ne Umma Tazo Daga Kano, itama Ta Jinjina Ramar da Tahir yayi da Zata
Tafi, tayi tama Farida Faɗa lokacin Data Zo Rakata, Akan ta kula da Mijinta Taga
dai Halin Dayake Ciki Haƙuri Farida tabama Umma Inda Tamata Alƙawarin gyara
Kuskurenta, itama bata Wuce ba sai da ta biya ta Duba Mufeeda, kana Direba ya Wuce
Da Ita Kano.
Tahir Kwana Huɗu yayi A Asibiti kafin asallameshi ya Dawo Gida, Mufeeda ko Sai da
ta Kwana Takwas Cur ta Warke kamar babu Abunda ya Faru kana Dr Hadiza Tayi
Discharging Ɗinsu Tahir da kanshi yaje ya Taho Da Ita Shida Farida Wacce yanzu ke
Wani Rawan Jiki Dashi Shi kuwa kallonta kawai yake Acikin Ranshi yana Faɗin Lokaci
ya Ƙure miki Farida, Baya son ma Haɗa Ido da Mufeeda Amma itako Tana ta Satar
kallonshi ganin yadda ya rame yayi ƙasumba kamar ba Daddy Ɗan Gayu ba, ita kaɗai
Tayi ta Sharɓan Kwallah Acikin Ranta Tana Faɗin Ta yafema Daddy Duniya da lahira
kuma Har Abada ba Wanda Zaiji Labarin Abunda ya Faru.
Gida yayi Daɗi da Dawowar Mufeeda mussaman ma Basma da Bassam da Iya, Tahir ko
yanzu kwata kwata ya daina Sakewa kamar da ko ya'yanshi Sun Fahimci Haka dama kuma
baida yawan magana Amma yanzu Abun nashi yayi yawa Tun balle Farida Data zage tana
Kula Dashi Amma Sai dai ya Bita da Ido Abun ya Fara bata mamaki da Tsoro ko Ta
Tambayeshi sai yace mata ba komai ta bashi Haƙuri Kuma yace ba komai amma ya kasa
Sakin Jiki Da Ita Babban Abunda ya bata mamaki Shine bai Nemeta ko Sau Ɗaya ba, Shi
ko Gaba ɗaya Sha'awarshi bata Zuwamai Saboda baya Cikin Natsuwarsa, Abunda ma ya
ɗan Lafamai Shine ganin Mufeeda ta samu lafiya ta Dawo Walwalwarta Har Ta koma
School Shi kaɗai sai ya Riƙa Fita Ta Ƙofar baya Daga sama yana Hangensu in Zasu
makaranta ganin Ta Saki Jikinta yasa Hankalinsa ya fara Kwanciya.
Sati biyu ya kwashe Agida yana Hutu kana ya koma Office Wanda ko Alokacin Sai
Ahankali Ishaq yasha Kamashi yashiga Zurfin Tunani Akwai Ranar daya ganshi yana
Kuka Abun yabashi Tsoro, yayi kuma Tambayar Duniyar nan Amma Tahir yaki Sanar dashi
sai ma Murmushin Kuka Dayayi mai yana Faɗin karyayi Fatan Jin Abunda ya Aikata
Domin Har shima in yaji Sai ya Tsaneshi, Abun yabashi Tsoro Sosai Sai ya Dinga
Fatan Allah ya yayema Tahir Duk Abunda Ke Damunshi Tunda yaƙi Sanar dashi koma
menene.
Ita kuma Farida takasa gane kan Tahir yadaina Fitowa Dining Cin Abinci sai dai
takai mai Ɗaki, shima bawani ci yake Sosai ba, koda yaushe ya dawo yana Ɗakinsa
yana karatun Qur'ani ko Kuma ka ganshi Zaune yayi Tagumi duk ya Chanza kamar ba
Tahir ba, bashi da Wata Walwala Komai na Duniya ya Fita kanshi gani yake Watarana
Za'a gane Komai yana ji Ajikinsa Asirinsa bai Rufeba Wata rana Komai Zai Fito
Sarari, kowa kuma Zaiji yazaiji Da Kunyar mutane Dawani Ido Zai kalli iyayansa yace
Shine da kanshi ya Aikata Wannan Aiki, Abun yana Ranshi ya Hanashi Sukuni.
*****
Yau ɗin Takama Weekend ne Sunday, Tun safe Farida ke Lura da Tahir yayi Zurfi Cikin
Tunani Ko Ruwan Wanka Data Hadamai bai Shiga yayi ba, Tana Lura Dashi yayi Zaune
Kawai yayi Shuru agefen Gado ya zabga Tagumi da Hannu Bibbiyu.
Shigowarta Bedroom d'in yasa Ta Bishi da kallo kafin ta ƙarasa Kusa Dashi Zama
tayi Gefenshi Kafin ta sanya Hannu Ta dafa Kafaɗarshi Tana Faɗin "Abban Basma..."
Ta faɗa Lokaci Ɗaya Tana Girgiza Kafaɗarshi, Ɗagowa yayi yana kallonta Kafin ya
saki Ajiyar Zuciya, yana Lumshe ido Lokaci Ɗaya yana Furzar da Iskar bakinshi,
narai narai Tayi da Ido kafin tace "Meke damunka ne..? Tunda Kadawo Daga Asibiti Ka
Chanza kadaina Walwala kamar baya baka sakin Jiki da Kowa, Baka da Aiki sai yawan
Zama Shuru da Tunani, kuma kasan Cewa Likita yace kadaina yawan Zama Cikin Tunani
Saboda Jinin Ka yayi Sama.." Ta faɗa Cike da Tausayawa.
Ƙura mata ido Yayi kafin ya saki Ajiyar Zuciya, Kawai ya Miƙe bai ce mata komai ba,
sai da ya Nufi Hanyar Toilet kana ya Waigo yana Faɗin "Bafa komai Tun Ranar Nake
Faɗa miki karki Damu.." Ya faɗa yana Tura Ƙofar Toilet d'in ya Shiga Da kallo Ta
bishi Jikinta Duk yayi Sanyi A iya Tunaninta ta kasa gano Abunda ke Damun Tahir Ta
tambayeshi ko Itace Amma yace karta damu Bakomai Amma Koda yaushe Abun nashi ƙara
gaba yake ba Wani Chanji, tana nan Zaune ya Fito Wanka Ɗaure da Towel a ƙugunsa
yazo ta gabanta Zai Wuce Da Hanzari Ta Miƙe ta faɗa Jikinsa Ta Rungumesa ta baya ta
Fashe mai da Kuka Tana Faɗin "Nidai don Allah ka sanar dani Abunda ke Damunka..? In
nice na maka laifi Tunda na Dawo nake baka Haƙuri Bai ci ka Haƙura ba? Don Allah
kadaina Wannan Tunanin.." Ta faɗa tana zagayo da Hannuwanta Ta Cikinshi Runtse Ido
yayi Jikinsa Duk yayi Sanyi kafin ya Buɗe ya Juyo da Farida Suna Fuskartar juna,
Hannu ya sanya yana Share mata Hawaye kafin yajata Jikinsa yana Faɗin "Shiiii..Nace
miki ba komai ko? Ki daina Damuwa..." Ya faɗa yana Shafa bayanta Har Zuwa Tudun
Hips Ɗinta, ganin Haka ne yasa ta ƙara Narke mai ajiki kafin Ta Ɗago kanta Ta Haɗa
Bakinsu Waje Ɗaya Gefe Ɗaya Kuma Hannunta na saman Faffaɗan Ƙirjinsa Tana Shafawa.
Tahir bai da Wata Natsuwa Biye mata kaɗai yayi Saboda Kada Allah ya kamashi da
laifin Danne ma Farida Hakki Har Suka Dangana da gadonsu sai gashi yau Abun mamaki
Farida bata gaji da Tahir ɗin ba Amma Shi Round ɗaya Sukayi ya Zame Jiki ya Shiga
Toilet ya sakarma kanshi Shower, yana Jin kamar ya kurma Ihu, yau shine bayan ya
Sadu da Mufeeda kuma ya koma ya Sadu da Farida Abun yamai baƙin ciki Sosai Wanda
yasa ya kasa Sakin Jikinsa yayi komai kamar yadda ya saba, Har yayi Wanka ya Fito
Farida na Kwance Tana Binshi da kallon Mamaki Aranta tana Faɗin Tabbas Tahir bashi
da lafiya don A Tarihin Aurensu bai Taɓa mata Ci Ɗaya Alokaci ɗaya ba sai yau.
********
Bayan Sati Uku da Faruwar Haka Abubuwa Suka Fara Sauki, Domin Mufeeda ta Saki
Jikinta Sosai ta Koma kamar da, rainon Naila ya Dawo Hanmunta kamar da, kuma Tana
Cigaba da Harkarta sai dai Abun na Cikin Ranta Tayi ta Kuka Ita Kaɗai Acikin ɗaki,
Sai Abu na Biyu Daya Dameta ganin yadda Daddy yake Ta Rama Atsaye Duk da bata cika
ganinshi bane, Shiko Tun bayan Faruwar Haka Mufeeda Ta Zauna Aranshi Komai yake sai
ta Faɗo mai tausayi Take bashi yarinya Ƙarama Ta Zama Abun Tausayi, Da ganga yake
gujema Haɗuwarsa da Mufeeda Da Zarar Sun Haɗu Abunda ya Faru ke Dawo mai Duk da
yanzu Ya fara Maida Natsuwarsa Amma bawai Don Abun yabar Zuciyarsa ba Kwata
Kwata...
*Aisha Alto...*
*Shakira...*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
Rayuwa Tana ta ganganrawa Da Daɗi ba Daɗi, Har yanzu Tahir bai manta da Abunda ya
Faru ba, Amma ya ɗan Saki ba kamar Farkon Abun ba, Amma Tausayin Mufeeda yayi Zaune
ɗam Acikin Ranshi Tun bayan Faruwar Abun baya iya Runtse Ido bai tuna ta ba, gashi
bai cika yarda Suna Haɗuwa ba Saboda gani yake Tamkar Za'a iya Fahimtar Abunda ya
Faru.
Ita ko Mufeeda duk da yarinta na Ɗawainiya da ita Zan iya Cewa Tama Fara Manta
Abunda ya Faru Tsakaninta da Tahir Tunda gani Take ta warke Komai ya Riga ya Wuce,
babu Wanda zai gane Kuma ba Wanda zai sani bata taba Tunanin nan gaba Wani Abu Zai
iya Faruwa ba.
Ɓangarenshi da Farida Kuwa ba laifi yayi ƙoƙarin ɓoye Damuwarshi Saboda Iyayenshi
Da Sauran 'yan'uwanshi da Kuma 'ya'yanshi da Hakkin Farida Dake kanshi Amma zancen
gaskiya Tun bayan Abunda ya Shiga Tsakaninsa da Mufeeda bai ƙara yin Sex cikin
Daɗin Rai ba, sam sam Sha'awar Hakan ya Fita a kanshi ita kanta Farida Tana mamakin
Wasu Sauye Sauye Daga Hallayar Tahir kamar An Ɗauke Tahir ɗin baya An kawo musu New
One ne.
Ko awajen Aiki Koda yaushe Cikin Danne Damuwarshi yake kada Wasu Su Fahimta, bayan
Ishaq baisan Ko kowa kallonshi yake ba Domin Duk Wanda yasan Tahir Abaya in ya
ganshi yanzu sai ya Tambayi kanshi Cewa Yaushe Tahir ɗin ya koma Haka...? Ishaq ko
Daga baya Daya Gaji Da Tambayar Tahir meke Damunsa yaƙi Sanar Dashi, Sai kawai ya
kawo Ido ya Saka mai Gefe Ɗaya yana Tayashi Addu'ar Allah ya warware mai duk Abunda
ke Damunshi.
Duk da ƙoƙarinsa na Danne Damuwarsa in ya keɓe kanshi na Wasu Mintina sai Abun ya
Faɗo mai nan da nan zai Rasa Natsuwarsa Har idanuwansa Su kama Zubar da Kwallah
Wanda ya rasa Dalili Haka Kurum ya keji Acikin Ranshi Komai bai ƙare ba Akwai Wani
Babban Lamari da Zai Faru nan gaba.
***********
Yau tun 8 yake Cikin Office ya kasa Aiwatar da Komai ya faɗa Kogin Tunani Hannunsa
Dafe da Duka Kuncinsa Zuciyarsa na Harbawa Lokaci Ɗaya, Koda da Rana Ɗaya Abun bai
Taɓa Shafe mai Acikin Kwakwalwa ba gani yake Tamkar Akwai Wani Babban Al'amarin da
Zai bayyana Komai yana Ji Ajikinsa Asirin sa bai Rufu ba, kuma Koda ya Rufu ina Zai
kai Hakkin Marainiyar Allah?
Wannan Tunanin Shike Sanyashi Shiga Wani Hali har ya fara Zubar da Kwallah bai sani
ba, Tsawon Lokaci ya Ɗauka yana Shessheƙan kuka Abunda bai sani ba Tunda ya fara
Wannan Koken nashi Ishaq ya Shigo Office d'in Bai sani ba Wanda ya Shiga Tashin
Hankali ganin Tahir na Kuka Lokaci Ɗaya yana Faɗin Allah na tuba ka yafemin, Abun
ya bashi Tsoro matuƙa Shiyasa yayi Tsaye ƙiƙam ya kasa magana yana Ɗauke da Wasu
Fayel ne Wanda ya kawoma Tahir ɗin ya Duba sai ya Tarar Dashi Cikin Wannan Halin.
Da ƙyar ya iya ƙarasawa Ga Kujeran da Tahir ke kai ya saka Hannu ya Dafa Kafaɗarshi
yana Faɗin "Subhanallahi Tahir mezan Gani Haka...? Kuka fa kake yi Don Allah ka
Daure ka sanar dani Abunda Ke Damunka Don Allah...?" Ya faɗa Cikin Alamun Damuwa
lokaci Ɗaya yana binsa da kallo, Firfigit Tahir yayi ya ɗago yana kallon Ishaq dake
Tsaye kanshi, Saurin Saka Hannu yayi yana Share Kwallarsa kafin ya ƙaƙaro murmushin
Dole yana Faɗin "Haba Friend Sau nawa Zan Sanar dakai babu Abunda Ke Damuna meyasa
kaƙi yarda dani ne...?"
Wani kallo Ishaq yabishi Dashi kafin yace "Eh Naga alama, na yarda kana da damuwa
amma bankai matsayin Dazaka sanar Dani ba..." Ya faɗa kai Tsaye yana Kafeshi da
ido, Cikin Fitan Hayyaci Tahir yace "Toh mene ne Damuwar nafada maka bakomai
Allah..."
Tsaki Ishaq yaja yana Faɗin "Toh in ba kana Cikin Damuwa ba Uban Me zai Zaunar
Dakai kana Kuka kana Faɗin Allah ka Tuba ya yafe maka? Haba Tahir ban zaci Akwai
Abunda Zaka iya ɓoye min ba. Amma ba komai Insha Allahu bazan Ƙara Ƙoƙarin naji
Abunda Ke Damunka ba Zan Ta Maka Addu'an Koma Menene Allah ya yayemaka Shi.."
Ya fada kafin ya ajiye mishi Fayels Ɗin Agabanshi ya juya zai Fita Daga Office d'in
kamar Daga Sama Yaji Muryan Tahir Yana Faɗin "Ba Abun Kirki bane Ishaq zaka Sha
mamaki in nace maka Fyaɗe Na Aikatama yarinyar Datake Daukana Tamkar
Mahaifinta...." Tahir ya Faɗa Idanuwansa suna Zubar da Kwallah, Cak Ishaq ya Tsaya
kafin ya Waigo yana Faɗin "Fyaɗe...? Wani Irin magana ne Haka, Shikenan Kuma Don ba
kasan Faɗa min Damuwarka sai kayi ma kanka Irin Wannan Mugun Bakin..? Ya faɗa yana
kallonsa Cike da damuwa.
Cikin ƙarfin Hali Tahir ya miƙe ya isa ga Windown office d'in Yana Share Hawayensa
Cikin Raunin Murya ya furta..."Dama Nasan bazaka yarda ba Ishaq Ina Jin Kunyar
kaina Da Kaina In na Tuna Abunda na Aikata, Ba karya bane Duk Damuwar Daka ga Ina
Shiga Saboda Hakane Mufeeda fa nayi ma Fyaɗe Ishaq..." Ya faɗa yana Dafe Kanshi,
Zaro Ido Ishaq yayi kafin yace "Mufeeda Nanny dai Ta Gidanka mai Renon Naila Wacce
Kuka Ɗaukota Daga Ƙauye..." Ya faɗa Cikin Fitan Hayyaci.
Gyaɗa kai Tahir yayi yana Hawayen Takaichi Da Nadama yana Faɗin "Ita fa Ishaq, ita
nayima Fyaɗe Cikin Rashin Hayyaci Amma Duk da Haka na Ɗauki Hakan A Matsayin
ƙaddarata..." Nan ya Shiga labarta mai Duk Abunda ya Faru Daga Farko Har ƙarshe, ya
ƙara da Faɗin "Ya zanyi Ishaq..? Abun yaƙi barin Raina ina ganin kamar na Cuci 'yar
mutane, ina ganin kamar Asirina bai Rufu ba, Kamar Akwai Wani Babban Al'amari da
Zai Faru nan gaba, Da Wani ido zan kalli mahaifiyar yarinyar nan...? Da wani ido
zan kalli iyayena da 'yan'uwana da kuma 'ya'yana...? Ishaq ka Faɗa min Da Wani Ido
Zan Kalli Mutanen Dasuke gani na Da Mutumci da Kima...?" Ya faɗa Ya kasa Control
Ɗin kanshi kawai sai ya Rufe Fuskarshi da Tafin Hannunshi ya Saki Wani Marayan
Kuka.
Jikin Ishaq ya gama yin Sanyi da labarin da Tahir ya bashi Jikinsa A matuƙar
Sanyaye ya ƙarasa ga Tahir ya Dafa Kafaɗarshi yana Faɗin "Ba laifinka bane
Tahir...Duk Abunda ya Faru Rubutacce ne Daga Rabbil Izzati, amma babu Shakka Farida
da Goggo Abu sune Silan Fadawarka Wannan Halin Ko Nace Wannan Kaddarar..." Da Sauri
Tahir ya Ɗago Idanuwansa Jajir yana Faɗin "Sune Sila Wallahi Ishaq Sune Sila da'ace
Farida Tana Kula da Duka Hakkina Da Haka bata Faru ba, da kuma Ace Goggo Abu ta
karɓi Uzurina ta barni na ƙara Aure Da Haka bai Faru Dani Ba Ishaq, kaicona na Cuci
Rayuwata Na Kuma Cuci Rayuwar baiwar Allah..." Ya faɗa Lokaci Ɗaya yana Faɗawa
Jikin Ishaq Shi kuma ya Rungumesa yana Bubbuga Bayansa Alamun Lallashi Tausayin
Tahir ya Cika mai Ciki Sosai.
Sun Daɗe A haka kafin Ishaq ya Ɗago Tahir ya kuma sanya Hannu yana Share mai Hawaye
Lokaci Ɗaya yana Faɗin "Ba girmanka bane ka Dinga Kuka Haka Friend na Tabbata koda
labarin nan ya Fita kowa zai bada Sheda Akanka kai Mutumin Kirki ne Kawai ƙaddara
ne ta Faɗa maka Wanda baka isa ka Tsallaketa ba..." Ƙura mishi Ido Tahir yayi kafin
yace "Hakane Ishaq Amma kai kaɗai ne zaka Fahimci Hakan Sauran Mutane bazasu gane
Haka ba..."
Hannunshi Ishaq ya Riƙo Suka Zauna Bisa Doguwar Kujeran Dake Cikin Office d'in,
Ƙaramin Fridge d'in dake Office d'in ya Buɗe ya Ɗauko mai Roban Ruwa da Kofi ya
Tsiyaya mai Ruwa ya bashi, karɓa yayi yasha Kafin ya miƙa mai, shima Tsiyayawa yayi
yasha kafin ya maida Kofin Da Goran Ruwan Saman Fridge d'in, Ya koma ya Zauna kusa
da Tahir ɗin yana Faɗin "Suma zasu gane Friend, Karka damu Nidai Roƙona ka Cire
Komai Acikin Ranka Tunda Itama yarinyar Ta manta komai, Kuma Tana da Hankali Tunda
Har yanzu Bata Sanar Da kowa ba.." Ajiyar Zuciya Tahir ya saki kafin yace "Hakane
Tausayin Yarinyar ne yaƙi barina Ishaq, ina Tausayinta yadda na Cuci Rayuwarta
Marainiya ce fa bata da Kowa sai ni sai Allah.." Ya faɗa cikin Damuwa...
Kafaɗarsa ya Bubbuga yana Faɗin "Cool Down karka Damu Insha Allahu Komai zai Wuce
Kuma Allah naganin Zuciyarka, Ai tana Karkashinka ne Kuma Kana Ƙoƙarin Kyautata
mata, na Tabbata nan gaba Zata inganta Rayuwarta.." Jinjina kai Tahir yayi kafin
yace "Insha Allahu" Nan Ishaq ya zauna yana Ta bama Tahir baki Sai da ya Tabbatar
da Tahir ya saki Jiki kafin Su gangara maganar Aikin, Tahir ya natsu ya Na Duba
Fayels din da Ishaq ya kawo mai, nan Ya barshi Shi kuma ya Tafi Office ɗinshi Cikin
Damuwar Halin da Tahir ke Ciki.
******
*After 2 Month...*
Gidan na Tahir A cike yake da 'yan Hutu Domin Satin Daya Gabata 'Ya'yan na Ashe
Suka Diro Sun Zo Hutu, Laila da Muda Sakamakon Dogon Hutun da yan Makaranta Suka
Samu na Third Tearm Duka yaran na gida Hatta Dasu Bassam Waɗanda Sukaji Daɗin
Zuwansu Laila d'in.
Misalin Ƙarfe 4:50pm na Ranar Asabar Iya ta Shiga Ɗakin Mufeeda Da Niyyar Ɗeboma
Naila madararta A cikin Wani ƙaramin Kofin Da'ake Dama mata Har ta Ɗiba Madaran
Tana Shirin Fitowa Daga Ɗakin Idonta ya Hango mata Mufeeda Kwance Gefen Gadonta
tana Sharar barcinta Jikinta Dogon Hijabin Islamiyansu ne, Daga ƙasa Kuma Ƙaramar
Jakar Makarantan nata ne yashe A ƙasa Daga Ganin yadda Ta Kwanta Zaka Fahimci
Barcin ya Kwasheta ne ba tare Data Shirya ba.
Baki Iya ta Riƙe Cike da mamakin Mufeeda A yan Kwanakin nan, Bata da Aiki sai barci
Wuni Take barci bata gajiya Alhalin Kuma Ada ba Haka Take ba,Da Hanzari Ta Isa
gareta ta Hau Tabata Tana Kiran Sunanta.. "Ke Mufeeda..Mufeeda..." Buɗe Ido Tayi
Cike da barci da kasala Tana kallon Iya, wacce ke Tsaye Tana kallonta Cikin
Mamakinta tace "Tashi Meye Haka Islamiyan Kenan, Su Basma sun Tsufa A Makaranta
Ashe Ke Kina nan Kina Shegen barcinki na Fama..." Ta faɗa Tana Binta da kallo.
Miƙa Mufeeda Tayi Tana Banƙaro Ƙirjinta kafin Ta Miƙe Zaune Tana Kwaɓe Hijabin
Jikinta, Baƙar Doguwar Rigar Dake Jikinta na kamfanin Armani ta bayyana, Wacce Ta
Fito da Ainihin Cikar da Mufeedan Tayi Tunda ga Kugunta Har Zuwa Nonuwanta, Cike da
Kasala ta Ɗaga Ido Tana kallon Iya Kafin Tace "Wallahi Iya bansan Barci ya Kwasheni
ba na Idar da sallar kenan Basma ta Shigo Ita da Laila Tace na Fito Mu Tafi, nidai
na san na Ɗauko Jaka na saka Hijabin Daganan Kuma Ban ƙara Sanin Inda kai na yake
ba.." Ta faɗa Tana Hamma.
Tsam da Ido Iya Tayi Tana Ƙarema Mufeeda Kallo Tun daga kan Fuskarta yadda Ta Cika
Tayi Wani Fari da kyau ga Jikinta Duk ya Chanza Ta kara Cika Kamar ba Mufeeda mara
Jiki ba, Gabanta na Faɗuwa Tace "Mufeeda meke Damunki ne, Na lura Dake a yan
Kwanakin nan, Baki cin Abinci sai Kayan Kwalama Kullum Sai kin Soya Wainar Fulawa,
kin kuma yi Ɗanwake ga yawan Barci Da kasala kamar kasa, Anya Mufeeda Zuciyata fa
Tana Rayamin Wani Abu...?"
Ta faɗa Tana Kurenta da Ido Mufeeda bata bama Tambayar Iya Muhimmanci ba Ta Miƙe
Tana Miƙa Tace "Bansani ba Iya Haka Kurum na Tsinci kaina, In ina Sha'awar Abu in
banci ba kamar Zan Mutu kuma yawan Barci Kila Don Hutun Da Muka samu ne, Nima Wani
Lokacin ina mamakin kaina, na rasa Meke Damuna..." Ta faɗa tana Yamutsa Fuska.
Cike da Faɗuwar gaba Iya ke Bin Ƙugun Mufeeda da kallo yadda ya Cika Sosai Ta Juya
Zata Shiga Toilet, Baki Ta kama kafin Ta Fice gabanta na Faɗuwa Zuciyarta na
Tsinkewa Ita ba yarinya ba ce, Ta san Alamomin Ciki Sosai da Munafiki da
Fallasasshe, Bata son Abunda Take Zargi Kan Mufeeda Ya Tabbata, Bayan Ta gama bama
Naila Madaran Ta Goyata tayi Barci sai ta Nufo Babban Falon Gidan Inda Farida ke
Zaune Tana Waya da Umma.
Gefenta Iya ta Zauna saman Cafet, Har sai da Ta kammalah Wayar, Ɗagowa Tayi Tana
kallon Iya kafin Tace "Hajiya Iya Naila ce Tasha goyo Haka..?" Yake Iya Tayi Kafin
Tace "Eh Hajiya..." Daga Haka Ta Sunkuyar Dakai, Ganin Haka yasa Farida tace
"Lafiya Iya da Wani Abu ne..?" Kai Ta Ɗago Tana Faɗin "Eh Hajiya nazo Miki da Wata
Magana ne Allah yasa Zaki Fahimceni..."
Zama Farida ta gyara kafin ta ajiye Wayarta Tana Faɗin "Karki Damu Iya Ina Jinki"
Cikin Muryan Dattako Iya Tace "A gaskiya Hajiya ya kamata Ki saka Likita ya Binciki
Mufeeda, domin ina Wani Zargi Akanta Duba da Wasu Alamomi Dana ga Sun bayyana
Muraratan Tare Da Ita.." Cike da mamaki Farida Tace "Likita ya Binciki Mufeeda Kuma
Iya bata da lafiya ne Ko meye Dalili..?
Iya ta Ɗan Yi Shuru kafin Tace "Maganar Gaskiya Hajiya Ina Zargin Ciki Mufeeda Ke
dashi, Amma Ita kanta bata Fahimci Haka ba, ko kuma Tsabar Bariki ne bansani ba..."
Zabura Farida Tayi Ta Miƙe Hannunta Dafe A ƙirjinta Tana Faɗin "Ciki Kuma Iya...?
Wata magana Kike faɗi Haka? Wazai ma Mufeeda Ciki yarinyar Da bata Fita Daga
Makaranta sai gida..?" Iya ta gyaɗa kai kafin Tace "Ƙwarai Kuwa Hajiya Nima Abunda
ya Dauremin kai kenan" Nan Ta Shiga gayama Farida Duk Abunda Tagani game da
Mufeedan da Alamun Ciki Ta ƙara da Sanar da Ita Halin Data Tarar da Ita yanzu
Haka..."
Cikin Farida ya bada Wani Sautin Tashin Hankali, jikinta na Rawa Tace "Na Shiga
goma ni Farida Ya Zanyi Iya.? In ya Tabbata yarinyar nan Ciki Tayi Wani Amsa zan
bama su Goggo Abu da Mahaifiyar yarinyar nan...? Mezan Cema Abban Basma Iya...?" Ta
faɗa Cikin Tashin Hankali, Miƙewa Iya Tayi Tana Faɗin "Hajiya kafin Mu Fara yanke
mata Hukunci Ya kamata Likita ya Duba Ta Tukunnah..." jinjina kai Farida Tayi Kafin
Tace "Shiga ki Sanar da Ita ta sako Hijabi ko Keke Napep mu Tara ya kaimu Asibiti
Tunda Inaga Daga Makarantarsu Basma Garzali ya Wuce Company ne, Hanzarta Iya.." Ta
fada tana Ɗaukan Wayarta Ta Nufi Upstairs Da Hanzari Nombar Tahir Take Nema Amma
kuma bata Sameshi ba, Ɗakinta ta Shiga Ta Ɗauko Mayafi Tunda Motarta ta samu
Matsala tana Wajen gyara, Koda ta Sauko Ƙasa Har Mufeeda Ta Fito Idanuwanta Sun
Shige Ciki Saboda barci, don Kwance Iya ta Tarar da ita.
Farida sai Lokacin Take ƙarema Mufeedan kallo gabanta na Faɗuwa Na Irin Kyau da
Cikar da Mufeedan Tayi basu Tsaya ba Farida Da Iya Wacce ke goye da Naila Suka Tasa
ta Gaba Suka Fice Daga Falon, a haraban Gidan Farida ce ta barma Megadi sallahu
Koda Tahir ya Dawo ko yara ya sanar dasu Sun Shiga Asibiti yanzu Zasu Dawo Da Toh
ya amsa musu yana Musu Fatan Dawowa Lafiya.
Keke Napep Suka Tara Sai iyali Hospital, Ƙuruciya da Yarinta ke Damun Mufeeda
Shiyasa Taji Daɗi Tunda Iya tace Za'a Dubata ne Don Itama Ta Gaji da yawan Barcin
Datake Fama Dashi Da Kasala, Suna Zuwa Farida da Mufeeda Suka Shiga Ciki Ganin Dr,
saboda Daman Nan Suke da Fayel, ganin Farko yayi mata sai ya Fara Jeho mata
Tambayan Yaushe Rabon Data ga Al'adanta tace "Wata Uku kenan." Gaban Farida sai ya
ƙara Tsinkewa nan Likitan keta Tambayanta Tana bashi Amsa, nan da nan ya kira Waya
sai ga Wata Nurse Tazo Yace Suje da Mufeeda Ta Ɗibi Jininta ta kai lab Agwadashi
yanzu yana Jiranta Fita Sukayi Ta tafi da Mufeeda lab D'in Ta Ɗibi Jininta, Office
d'in Mufeeda ta Dawo Ta Zauna Farida ko na Zaune Tana Fama da Faɗuwar gaba Tsawon
Minti 30 sai ga Sakamako ya Fito An kawoma Likita yana karɓan Takardan Ya Buɗe ya
karanta kafin ya kalli Farida yana Faɗin "Wai kun ma yaranku Aure ne ba labari..?
Da yake Likitan Asibitin ne ya sansu Fiye da Shekaru Huɗu So Duk yasan Mufeedan
Dasu Basma.
Farida Taji miyau mai Kauri ya Tsaya mata da ƙyar tace "A'a Dr meka gani.? Ta faɗa
tana Kafeshi Da Ido. Cikin mamaki yace "Ah...Garin ya haka..? Gashi Result Ɗinta ya
Nuna Tana Ɗauke da Ciki Har na Tsawon Wata Uku..." Ƙirji Farida ta Dafe Hannunta
Akai Suka maimaita kalmar "Ciki.....?" Ita da Mufeeda Wacce Ta Zabura Ta Miƙe bayan
Taji Kalmar Kamar Saukar Aradu Akunnenta.
*Janafty...*
*Aisha Alto..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
Suna Fitowa Iya Ta Miƙe ko bata Tambaya ba ganin Yadda Idanuwan Farida Suka kaɗa
Sukayi Jajir, ga Mufeeda na Kuka Wurjanjan Ta samu Amsarta Shiyasa bata Tsaya
Tambaya ba Sai ma bin bayan Farida Datayi Wacce Ta Saki Hannun Mufeeda Tayi gaba
Zuciyarta na Ta fasa da Fargaban Wani bayani Zatama goggo Abu..? Mezatace da
Mahaifiyar Mufeeda..? Uwa uba Kuma Tahir Wanda Amanar Mufeeda Ya Damƙashi Ahannunta
ya kuma ce Ta Kula da Ita Tamkar yadda Zata Kula dasu Basma..? Abunda yafi Ɗaure
mata kai da bata mamaki Wayayi ma Mufeeda Ciki..? Yarinyar da babu Inda Take Zuwa
Daga Makaranta sai makaranta kuma Makarantan ma Akaisu Adawo Dasu..? Kai Wannan
Al'amari Akwai Ɗaure kai.
Ko Acikin Adaidaita Mufeeda Keta Gunjin Kuka Farida da Iya Kuwa Suka mata banza
Kowa na Saka Abubuwan Mamaki Acikin Zuciyarsa Ita Farida Baƙin Ciki ne da Kuma
Kunyar Wani bayani Zatama Su Goggo Abu Akan Wannan Baƙin Labarin, ita kuma Mufeeda
Kuka take Wanda Ta rasa Dalilinshi Sai Da Akace Tana da Ciki Ta Tuna Malamin
Islamiyansu ya sanar Dasu Duk macen Data Fara Jinin Al'ada Akayi Abunda Tahir Daddy
yayi Da Ita To Zata iya Samun Ciki, ƙananun Shekarunta bai bata Damar Fahimtar Cewa
Akwai Rana mai kama Data yau ba, Kuka Take na Baƙin ciki Bakinta bazai iya Taɓa
Furta Wanda ya Aikata haka gareta ba Domin Tayi Alkawarin Ko Za'a Kasheta sai ta
Rufama Daddy Asiri Domin Shima ya Rufa mata Asiri Lokacin Da bata da Kowa.
Ita ko iya Cikin Ranta Salati kawai Take, Tana Kuma Hasashe da Tunanin Waye yayi
ma Mufeeda Ciki, ita bata ma kai da Nisa ba Tunani Take ko Garzali ne..? Ko maigadi
ne..? Domin Iya saninta Gidan Tahir gida ne na Tsaro da Tsantsar Tarbiya, Amma Kuma
Taya Hakan Ta kasance..? A iya saninta bata san Mufeeda da Wani Halin banza ba,
bata da Saurayi ko Wata Ƙawar Banza Wanda Zai Nuna Alamun Hakan Zai iya Faruwa..?
Kai Wannan Abu da Ban Mamaki yake.
Suna gab da Isowa gida Wayar Farida ta fara ƙara Tana Dubawa Taga Tahir ne sai
taƙi Ɗaga Kiran Don bata da Abunda Zata iya Sanar Dashi Adaidai Wannan Lokacin
Zuciyarta bata da Ƙwarin Gwiwa, suna Dawowa gidan Suka Iske Su Basma Sun Dawo Daga
Islamiya Nan Suke Shaidama Farida Daddy ya Dawo Megadi ke sanar Dasu Sun Tafi
Asibiti Shine yayi Ta Kiranta bata Ɗaga ba Sun Tafi masallaci Shida Muda da Bassam,
Farida batayi magana ba Illah Hayewa Sama Datayi, Ranta Duk ba Daɗi Itama Iya
Ɗakinta ta Shiga Tana Sauke Naila Data Farka Mufeeda ko Tana Kuka ta Nufi Ɗakinta
Laila da Basma Suka bita Suna Tambayanta Ko lafiya Da ƙyar Ta Iya Cemusu batajin
Daɗi ne, Basma tace "Oh dama ke Momy Taje kaiwa Asibiti? Sannu Allah ya baki
lafiya" Nan Laila Itama ta mata Sannu Daga nan Suka Fice Daga Ɗakin Suna masu
Tausaya mata ganin Kukan Datake Su Azatonsu Ko Ciwon nata yayi Zafi Shiyasa Take
Kuka.
Farida ko Da ƙyar ta iya Shiga Toilet ɗinta ta Ɗauro Alwala tazo ta kabarta sallar
Magriba ta Idar Kenan Tana Zaune Ta Ƙurama Saitin Makeken Gadonta Ido zuciyarta ba
Daɗi Kamar mai Nazarin Wani Abu Amma Azahirin Gaskiya Tunanin Mafita Takeyi, Bata
ji Shigowar Tahir ba sai da Taji Tattausan Hannunshi Akan Fuskarta yana Shafa
Kumatunta Firgigit ta Dawo Cikin hayyacinta, Ta Ɗago Tana kallonshi Shima kallonta
yake Cikin Mamaki yace "Lafiya..? Meyake Faruwa Ki kai nisan Tunani Haka.? Waye ba
lafiya mun Dawo Kuna Asibiti..?"
Miyau Farida Ta Haɗiye mai Ɗaci Kafin Ta Tattaro Murmushin Yaƙe Tace
"Amh..Umh...ba komai..." Ta faɗa Muryanta na Rawa Kamar zata Fashe da Kuka Tana
Tunanin In Tahir yaji labari Ita Zai Ɗorama laifi yace Duk da Laifinta bata Son
Zaman Gida Balle ta Fahimci Wani Hali yaran Ke Ciki.
Wani kallo ya mata kafin yace "Ban gane ba komai ba Farida? kinga idonki kuwa..?
Kuka kikayi ko menene..? Kuma baki bani Amsa ba Waye ba lafiya Kuka Tafi ganin
Likita..?" Ajiyar Zuciya Ta Sauke Kafin Ta Yunƙura Ta Miƙe Tana Zame Hannunta dake
Cikin na Tahir Hijabin Jikinta ta Cire Tana Ƙoƙarin Isa gaban Makeken Wardrope
Ɗinta Take Faɗin "Mufeeda ce take Fama da Zazzaɓi Tun Jiya Shine mukaje da Ita Taga
Likita."
Lokacin da Farida Ta Ambaci Mufeeda sai da gaban Tahir ya faɗi, Haka yake Fama Da
Faɗuwar Gaba Kwanan nan Duk Sanda Zaiga Mufeeda Ko Kuma yaji Muryanta ko Wani ya
Ambaci Sunanta, Toh Hakan sai ya faru yanzu ma Tunaninsa bai taɓa bashi Ciki
Mufeeda ke dashi ba Shiyace yace "Tun Jiya kuma..? Shine sai yau zata ganin
Likita..?" Ya faɗa Cike da Nuna Kulawa, Farida na Maida Hijabinta Cikin Durowarta
Tace "Kasanta da Nuƙu Nuƙu bata Sanar ma Kowa ba Nima Ɗazu ne Iya ke Sanar Dani Ko
Islamiya ta kasa Zuwa.."
Numfashi ya Sauke kafin yace "Naji yanzu me Likitan yace..? Ya jikin Nata..?"
Kamar tayi Ihu Da Tambayoyin Tahir Amma Sai ta kanne Cikin Sanyin Murya tace "Taji
Sauƙi Zazzaɓi ne ya Dubata ya bata magunguna.." Kai Tsaye yace mata "Wani Dr Kuka
gani..?" Gabanta na Faɗi bata juyo ba Saboda Kada ya Fahimci Halin Datake Ciki Tace
"Dr Salis ne..." Miƙewa yayi yana Faɗin "Ok yayi kyau Zan kirasa Zamu yi magana."
Ya faɗa yana Ƙoƙarin Ficewa Daga Ɗakin.
Bayan Fitarshi Falon Ƙasa ya sauko yaso ya Shiga Ɗakin Mufeeda, Yaga Jikinta Amma
Sai ya samu Wayar Ishaq akan yana Haraban Gidanshi ya Fito Su Tattauna nan ya fice
Suna magana kan Wasu Sabbin Motoci ne da zasu zo Daga Kwatono gobe Sun Ɗauki Lokaci
mai Tsawo kafin Su Rabu Wanda yayi Ya Shiga Su gaisa da Farida Amma yaƙi yace Dare
yayi Dole ya Ƙyaleshi Suka Rabu Akan Sai gobe in Sun Haɗu A office, koda ya Shigo
Falon ba Kowa Su Basma da Bassam Har Sunyi Dinner ɗinsu Sun Shige Ɗakunansu, Kan
Teburin ya Nufa yaja Kujera ya Zauna yana Murmushi Shi kaɗai ganin Tuwon Shinkafa
miyar Kuɓewa Ce Ɗanya Yana Son Abincin Sosai bai Damu da Cin Abincin dasu Basma
Sukayi ba Tunda Shi ya Saka Dokar Daga yanzu Adaina Jiransa Sai yazo Kana Ayi
Dinner, nan ya Zauna yaci Tuwon Sosai bayan ya gama ganin Dare Yayi sai ya Haƙura
da Shiga Wajen Mufeeda ya barshi Sai da Safe, alokacin Kuma Daya Shiga Zai Isketa
ne Tana Kuka.
Farida Kuwa Lokacin da Tahir ya Fita ta Daɗe Zaune Tana Tunanin Mafita, kafin Ta
Janyo Waya Ta Kira Goggo Abu bayan Goggo Abu Ta Ɗauka Sun gaisa Kawai sai Farida ta
Fashe Mata Da Kuka Nan Hankalin Goggo Abu ya Tashi nan da nan Ta Shiga Tambayanta A
ruɗe Akan Abunda ke Faruwa, cikin Kuka Farida ke Zayyanama Goggo Abu komai game da
Abunda Likita yace na Mufeeda Nada ciki, Wani Razana Goggo Abu Tayi Tana Kan
Gadonta ne sai da ta Wuntsulo Ƙasa Saboda Razana da Maganar Farida Innalillahi
Kawai Take Maimatawa kafin Ta samu Zarafin Magana Farida ta kwaso Rantsuwan basu
san Wanda ya Aikatama Mufeedan Haka ba, Goggo Abu na Share Zufa tace "Farida Ita
Mufeeda bata Faɗi Wanda ya yi mata Cikin ba? Na shiga Uku ni Zainabu Abu Mezan cema
Uwar yarinyar nan..? Ta faɗa Tana Sharɓe Kwallah.
Farida tace "Ban Tambayeta ba Goggo Na shiga Ruɗani bana So Tahir ya Fahimci komai
goggo laifina Zai gani.." Goggo Abu Tace "Wannan ba Hujja bane Farida Ya zama Dole
Tahir ya sani, Babu yadda zamuyi Farida Dole maganar nan Zata Shiga Kunnan Waɗanda
ya kamata, yanzu zan Shiga Wajen Hakimi mu Tattauna gobe in Allah ya Kawomu zan ma
Tahir Waya ya Turo Direbansa ya Ɗauko mu Nida Hakimi da Ita Fulera ɗin sai Asan
Abun yi..." Farida ta saka Kuka Tana Faɗin "Wayyo Goggo nasan Laifina za'a gani
Amma ko Shegiyar yarinyar nan Ta Cucemu.." Goggo Abu Tace "Ba kaɗan ba Farida bar
Kuka Gobe in Allah ya kaimu zatayi bayani Don Ubanta.." Daga Haka Suka Rabu bayan
Goggo Ta Jaddada mata Gobe Suna Tafe.
Daga nan Zuciyarta taƙi NaTsuwa, Sai kawai ta Latso Nombar Umma Kano Ta Ɗauka
Kenan Kafin Tayi magana Farida ta Sanya mata kuka Hankalinta Tashe Take Tambayanta
lafiya...? Farida ta Buɗe baki Zatayi mgana sai Wayarta ta Ɗauke Ɗif ba Chaji Taji
Haushi Sosai taso ta sanarma Umma Halin Da'ake Ciki, Da hanzari ta tashi ta Jona
Chaji sai ta Sha'afa bata Kunna Wayar ba Ita Kuma Umma Daga chan ɓangaren Tayi Ta
Neman Farida bata samu ba, Ta maida Akalan Kiranta kan Tahir Shima kamar Haɗin baki
bata Sameshi ba Ashe ya sanya Wayarsa A Fligt mode bai sani ba, Hankalinta a tashe
ta samu Abba Tana gaya mai Shima Ya shiga Ruɗu Amma sai ya lallashi Umma da cewa
Gobe in Allah ya yarda sai Su Tafi Kadunan Tare Shima Dama Zai je Saboda Zuwan
Sabbin Motocin nan, Da Haka Umma ta Ɗan Saki Amma Ranta ba Daɗi Jin Kukan Farida
Tana Fatan Allah yasa Lafiya.
Shiko Tahir Daga nan Ɗakin Farida ya Nufa, Farida na Zaune gefen Gado Sanye da
kayan Barci masu Taushi Tana Jin Motsin Tahir ta Sulale Bisa Gado Taja Bargo Ta
Rufe Jikinta Lokaci Ɗaya Tana Kulle Idanuwanta, yana Shigowa ya Ƙaraso bakin gadon
yana Kallonta ganin kamar Tana barci ne sai bai Tasheta ba Illah Ranƙwafawa Dayayi
ya Sumbaci Goshinta Kafin ya ƙara gyara mata Blanket d'in Wutar Ɗakin ya Rage ya
Kunna mata Dum light, Kafin ya Fice Daga Ɗakin ya Rufo mata Ƙofa ya Nufi Bedroom
ɗinsa, yana Fita ta Buɗe Ido tana Sauke Numfashi kafin Taji Kwalla Ta Cika mata
Ido, Farida Nadama ta Shigeta Alokacin da Komai ya Riga ya gama Kwaɓe mata.
********
Washegari Tun Safe Tahir ya Fita Office, Saboda Bakin Da zasu zo yau ɗin Kuma Sunyi
Waya da Abba Tun jiya Dama yasan Da Zuwanshi Bai Dade Da Isa Company ba Wayar Goggo
Abu Ta Iskeshi Inda Tace ya Turo musu Direba Zasu Zo Ita da Hakimi da Fulera
Mahaifiyar Mufeeda Abun ya bama Tahir mamaki Sosai ya Shiga Tambayan Goggo Abu Wani
Abu ya Faru ne...? Amma Sai tace Kar ya Damu In Suka Zo Zaiji Komai, Abun ya bashi
mamaki barin Ma Datace Harda Hakimi, wanda Hakimi baya Zuwa Kaduna sai da
Ƙwaƙƙwaran Dalili Mai karfi Amma Ko Ɗaya Zuciyarsa da Tunaninsa basu kawo masa Wani
Abu mara Daɗi ya Faru ba, Ya mafi karkata Alaƙan Zuwan nasu ƙila ko Farida ce Takai
Ƙararshi Toh Amma Ai yanzu basu da Wata Matsala, Haka dai ya gama Duk Tunaninsa Bai
Hango Dalili ba Duk da gabansa na Faɗi bai Ɗauki Abun Nada Nasaba da Haka ba.
Ita ko Goggo Abu Tun Adaren Jiya Ta Isa Turakar Hakimi ta Zayyana mai komai Salati
da Sallallami Hakimi ya Shigayi Cikin Ruɗani da Tashin Hankali Sun Daɗe Suna
Jajanta lamarin, har Innaro Tazo ta Samessu Itama Taji Ɗimuwa Dataji Wannan Lamarin
Daya Faru Haka Suka Zauna Jugum Jugum Abun Duniya ya Ishesu, Hakimi Shi ya yanke
Hukunci Kada Asanar da Fulera Abunda Ke Faruwa sai Sun Isa Kaduna Allah barshi Sai
Lokacin Taji Komai, Da haka Suka Rabu Innaro Ta Koma Shashenta Ta Kwanta Cike da
Mamakin Faruwar Wannan Al'amarin Hakimi da Goggo Abu Kuwa basu Runtsa ba Suna
zullumi da Tunanin Yadda Mutane zasu Ɗora musu Laifin Duk Abunda ya Faru.
Garzali ya bama Umarnin ya tafi Ɗanbatta ya ɗauko su Goggo, Ya koma Office Kenan
Sai ga Abba ya iso, nan yake Shaida ma Tahir Cewa Tare da Umma Suke sun ajiyeta
Gidanshi Abun sai ya Ƙara Ɗaurema Tahir kai barin ma Da Abba ya Shiga Tambayanshi
Duk Gidan Lafiya ba Abunda ya Faru..? Yace mai ba komai, jin Haka sai suka Watsar
da Zencen Suka Cigaba da Tattauna Batun Motocin nasu da zasu iso yanzu ba da Daɗewa
ba.
Umma kuwa Tana Isowa Farida na Cikin Ɗakinta bayan Su Basma Sun gama mata Oyoyo
Suka gaisa da Iya, Ta Haura sama Wajen Farida Wacce Ke Kwance Tana Tunanin Mafita,
Sai kawai Taji Sallamar Umma Lokaci Ɗaya Tana Kiranta Zumbur Ta Miƙe Ta Isa gareta
ta Rungumeta Lokaci Ɗaya Ta Fashe da Kuka Umma Ta Fara Lallashinta Ta hanyar
Bubbuga Bayanta Sai da Farida Tayi Kuka mai Isarta kana Ta Sanar da Umma Abunda Ke
Faruwa.
Ƙirji Umma Ta kama Tana Salati Lokaci Ɗaya Idanuwanta Duk A Bude Tana Tsaye ne Sai
Da Ta Zauna Hannunta Duka biyu Bisa kai Tana Tambayan Farida garin ya Haka ta
Faru..? Farida na Kuka Take Faɗin bata sani ba Wallahi...? Nan Take Shaida mata
Abunda goggo Abu Tace Suna Tafe Yau Tagumi Umma Ta Buga Ta fara ma Farida Faɗan
Rashin Kula da Sakaci Metake Tunani in Itama Basma Ta faɗa irin Wannan Halin..?
Tunda Da Mufeedan Da Basma duk Tare Suke Ita dai Farida Kuka Kawai Take Tana Jin
Kunyar yadda Duka kowa zai Bata laifi Amma Maganar Gaskiya Mufeeda Ta Cuceta
Wallahi.
Wajen 12pm na Rana Su Hakimi Suka Iso gidan Tahir Farida Ta karɓesu Hannu
bibbiyu Amma Da Faɗuwar Gaba Nan Suka Iske Umma, basu yadda Sun Tada maganar ba
saboda Inna Fulera Wacce Tana Zuwa 'yarta ta Fara Nema,Wacce ke Ɗaki Dunƙule Tana
Kuka Lokacin Data Ci karo da Fuskar Inna Fulera sai Rauni da Kunya Suka Zomata ta
ƙanƙame Innar ta ta Tana Kuka Ganin Haka sai Jikin Inna Yayi Sanyi ta Zaunar Da Ita
gefen Gado Tana Tambayanta Lafiya meya ke Faruwa..?" Don Goggo Abu bata mata Wani
bayani ba, ta dai ce Ta Shirya Suzo Kaduna Jin Haka Yasa Jikin Mufeeda ya fara Rawa
Kamar Mazari Idonta ya fara Zubar da Kwalla, Tana Tunanin Ya Zatayi in Aka Turketa
sai Ta faɗi Wanda yayi mata Cikin..? Uwa uba ga Innarta Wani Hali Zata Shiga Intaji
labari..? Ƙanƙameta Innar Tayi Ita Kuma Mufeeda tana Faɗin "Inna Kiyafemin Ba
Laifina bane, Jin Haka sai gaban Innar ya faɗi Ta fara Tunanin Allah yasa Ba Wani
Laifi Mufeeda ta Aikata Musu mara Daɗi ba, Gashi Kuma Mufeedan Taƙi magana sam
balle Taji Abunda ya Faru.
Motocin Sunzo ba Daɗewa sai ga Kiran Goggo Abu Tace maza maza Tahir yazo gida yanzu
nan, Sun Iso sai Lokacin ya ƙara jin Mutuwar Jiki Sosai da Faɗuwar Gaba, jin Haka
yasa Abba Shima Direba ya Wuce Dashi Shi Kuma Ishaq ya Ɗaukosa Zuwa gida Suna Tafe
Suna Fatan Allah yasa Lafiya.
Lokacin da Suka iso gidan Ishaq yaso ya koma Company Sai Tahir ya Matsa mai ya
Shiga Ya gaisa dasu Hakimi Suna Dumfaran Falon Suka Fara Jin Shessheƙan Kuka da
Koke koke Da Hanzari Tahir ya Fara Shiga Falon Ishaq na Binsa Abaya Idanuwansa
Sukayi Tozali da Mufeeda, Wacce ke Durƙushe Tsakiyar Falon Tana Gunjin Kuka ga Inna
Fulera gefenta Itama Tana Kukan ga Farida Zaune A ƙasa Kusa da Goggo Abu sai Hakimi
dake Zaune kan Ɗaya Daga Cikin Kujerun Falon Shida Abba, Sai iya Dake Zaune chan
gefe Kowa ka kallah Fuskarsa ba Annuri.
Lokaci Ɗaya gaban Tahir ya yanke ya Faɗi Yaji Jiri na Neman Kadashi, sai da Ishaq
dake bayansa ya Riƙonsa, Idanuwansa Sun Fito Waje yake bin Kowa da Kallo Kafin ya
maida kallonsa kan Farida Cikin Sarkewar murya ya Furta.." Fa...Farida...Meya Ke
Faruwa...?" Ya faɗa suna ƙarasowa Cikin Falon, Jin muryansa yasa Duka Ido ya koma
kanshi Cikin Damuwa goggo Abu Tace "Yauwa Attahiru Dama kai muke Jira kazo ka
Tambayi Mufeeda Wanda yayi mata Cikin Jikinta Tunda Dukkanmu Taƙi Sanar damu
komai..."
Ba Tahir kaɗai ba Hatta Ishaq Sai da Yaji Wani Abu ya Tsirga mai Daga
Kwakwalwarsa, Shiko Tahir Kwalalo Ido yayi kamar Idonshi zai Fito Waje, Mufeeda
Data Ɗago Kanta Tana Kuka Idanuwanta Suka Kumbura Suka Haɗa Ido da Tahir Wanda
Jikinsa Ke Rawa Zuciyarsa na Gudu Naman Jikinsa na Cida Zufa na Keto mai Cikin Wani
yanayi ya Saluɓe Hannunsa ana Ishaq ya Sulale A ƙasa yana Maimata kalmar
"Innalillahi Wa'inna Ilaihirraju'un"un..." Sai ga Hawaye Suna Fitowa Daga Cikin
Kwarmin Idanuwansa.
Ba Wanda yayi mamakin Halin Da Tahir ya Shiga Sanin Halinsa Mai Ƙoƙarin Kyautatama
Kowa, Inna Fulera tana Kuka Take Faɗin "Mufeeda Meyasa Kika min Haka..? Zuciyata ta
kasa yarda da Wannan maganar ki ƙaryata ko kuma ki sanar damu Wanda Kika bama kanki
yayi miki ciki.." Ta faɗa Tana Kuka Girgiza kai Mufeeda Ta Hauyi Tana Kuka Take
Faɗin "Kiyi Haƙuri Inna Ba Laifina bane, Amma bazan iya Faɗar Wanda yamin Wannan
Cikin ba Ko zaku Kasheni.." Ta faɗa tana kallon Tahir Wanda Ya Ɗago yana kallonta,
Jin Haka yasa Inna Fulera ta Taso da Hanzari ta Isa ga Mufeeda ta Fara Dukanta ta
Ko'ina Tana Faɗin "Allah ya isa Tsakanina Dake Mufeeda zan ko kasheki kowa ya Huta
da Na Dinga Kallonki kina sakani Baƙin ciki da Takaichi..."
Kuka Mufeeda Keyi Inna Fulera nayi Tana dukanta Farida ma Kukan Take Kafin Wani
yayi magana Tahir ya Miƙe ya isa Ga Inna Fulera ya Duƙa agabanta bayan ya Shiga
Tsakaninta da Mufeeda ya kalleta yana Zubar da Hawaye, Bakinsa na Rawa zai Fara
Magana Ishaq yace "Don Allah Tahir kar kace Komai na Roƙeka..." Tahir ya Runtse ido
kafin yace "Kabarni na Faɗa Ishaq Gwara Kunyar Duniya Data Kiyama..." Ya faɗa
Hawaye na Kwararo mai.
Gaba ɗaya Falon kallo ya Koma kan Tahir Cike da Mamaki, barin ma Farida wacce
Kukan Tahir ya fara Tsorata ta, Babu Zato kawai Sukaji Tahir na Faɗin "Bazata Taɓa
Faɗa muku Wanda yayi mata...don Ba kowa bane Face Ni...ni...na mata Cikin
Jikinta...." Ya faɗa yana Rushewa da Kuka Numfashisa na Sama Sama, Gaba ɗaya Falon
Kowa ya Kwalolo Ido, Matan Gaba ɗaya Suka Miƙe Farida Wacce Ta Ɗora Hannu Akai ta
Zaro Ido Tana Faɗin "What....? Kace kai kayi mata Cikin...?"
*Aisha Alto...*
*Shakira...*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
Gyaɗa kansa yayi hawaye masu zafi da raɗaɗi na zuba daga cikin idanunsa ya duƙar da
kai ƙasa yace "Tabbas nine nayi mata ciki...cikin jikin Mufeeda nawa ne bana wani
ba..." Yana faɗa ya sake rushewa da wani irin kuka mai taɓa zuciya da ban tausayi.
Itama Mufeeda ƙara sautin kukanta tayi da ƙarfi zuciyarta cike da tausayin Daddy ta
tsura masa ido tana ji a ranta dama wannan ranar bata zo musu ba.
Gaba ɗaya falon salati suka ɗauka kowa faɗi yake "Innalillahi wa'inna
ilaihirraji'un...." Yayinda ita ko Farida ta ƙara gigicewa ta ruɗe da jin kalaman
da Tahir yake faɗa, lokaci ɗaya komai ya tsaya mata cak, sai aikin nunashi take da
yatsa tana girgiza kai ta kasa magana, kafin ta koma da baya ta faɗa saman kujera
daɓas ta zauna a ruɗe tana faɗin "A'a Abban Basma don Allah kar kace haka...wannan
nasan ba gaskiya kake faɗa ba...nasan ba halinka bane a ko'ina kuma zan iya yin
shaidarka akan haka...kuma nasan kowa ma zai yi shaidarka indai akan haka ne, nasan
ko akan wata bazaka taɓa iya aikata haka ba, balle akan Mufeeda 'yar damuka raina
muka ɗauketa tamkar 'yar da muka haifa da cikinmu...plz Abban Basma karka sakamu
cikin wani yanayi plz kace ƙarya ne abinda ka faɗa ba gaskiya bane...don Allah kace
ƙarya ne Abban Basma.." Ta faɗa tana ji a zuciyarta dama a tasheta ace mafarki take
ba gaskiya bane abinda kunnuwanta suke jiye mata ba.
Yana kallonta da idanuwansa da suka rine sukayi jajir suna tsiyayar ruwan hawaye
yace "Tabbas Farida abinda na faɗa gaskiya ne, kunnuwanki sun jiye miki dai-
dai...cikin dake jikin Mufeeda nawa ne...nine na yiwa Mufeeda ciki..cikina
ne...amma a bisa ƙaddara data faɗa min ba'a son raina ba..." Salati duka falon suka
ƙara ɗauka, kafin Inna Fulera ta fashe da kuka mai sauti ta miƙe ta cakumi Mufeeda
ta fizgota ta rufeta da duka baji ba gani tana yi tana kuka take faɗin "Kin cuceni
kin cuci kanki Mufeeda, kin wulaƙanta rayuwarki kin tozarta kanki...Allah ya isa
tsakanina dake..ki rasa sakayyar da zakiyi min sai ta abun kunya...kina marainiya
kin zubarwa kanki kima da mutunci...Allah ya gani iya tarbiyya na baki ita dai-dai
gwargwado ban san kuma meya shiga kanki ba har kika iya watsar da mutuncinki a titi
ba..." Ta faɗa tana ƙara shurinta da ƙafa tana kuka, Mufeeda ma kukan take tana
jujjuya kanta amma ta kasa tashi ta ƙwaci kanta, da sauri Tahir ya matso ganin Inna
Fulera ta ɗaga ƙafa zata taka cikin Mufeeda tana faɗin gwara na kasheki da inci
gaba da ganinki ina jin baƙin cikinki a raina, da hanzari ya riƙeta yana girgiza
kai a hankali yace "Laifina ne Inna, ita da niyyar taimakona tazo, dukkanmu bada
niyya mukayi ba...ƙaddara ce ta afka mana..." A fusace Farida ta miƙe tana faɗin
"Babu ruwan ƙaddara Malam, dama can kana da niyyar aikatawa shine zaka fake da
ƙaddara..." Ta faɗa tana fashewa da kukan takaici da baƙin ciki tana faɗin "Amma
Tahir ka cuce ni ka cuci zuri'arka ka wulaƙantamu, yanzu da wani irin idanu kakeso
a kalli 'ya'yanka? Ka ɓata mana sunan zuri'a, ka haikewa 'yar da take ɗaukarka a
matsayin uba...tirr da kai da irin halinka, wallahi bazan iya ci gaba da zama da
kai ba, ni ba fasiƙa bace don haka bazan zauna da fasiƙi ba...sai dai ka zauna da
ita da shegen cikinku..." Ta faɗa tana ƙara fashewa da kukan baƙin ciki da takaici
tana kallon Mufeeda dake kukan itama tana ji kamar ta tashi ta shaƙeta har sai taga
bata numfashi.
Wani murmushin dayafi kuka ciwo Tahir yayi yana kallon Goggo yace "Komai da ya faru
bada son raina bane kawai na ɗauki hakan ne a matsayin ƙaddarata kuma na karɓeta
hannu biyu, Allah ya bani ikon cin jarabawata... Nan take ya shiga bada labarin duk
abubuwan da suka faru, kafin yana kuka ya ɗago yana faɗin "Duk da wannan abun daya
faru dani ba kowa bane sanadin shigata wannan halin sai Farida dake Goggo, domin ke
kika hanani na sanarwa Baba Hakimi wannan matsalar dake faruwa dani kuma kika
hanani maganar ƙara aure, alhalin baki taɓa tambayata dalilin da yasa na nace inaso
na ƙara auren ba, sai dai a kullum idan naje miki da maganar irin abubuwan da
Farida take yi min sai kice inyi haƙuri zaki mata magana, zata gyara, baki taɓa
nuna damuwarki akan halin da nake ciki ko ki tambayeni abinda yake faruwa ba, sai
dai dana fara sai ki katseni kice bakyason ayi abunda zumunci zai lalace...Goggo ni
ɗanki ne amma baki taɓa damuwa da matsalata ba, domin baki taɓa bani damar nuna
miki damuwata ba, sai dai ma kiyi ƙoƙarin hanani faɗawa mahaifina halin da nake
ciki, to yau ga abinda kika jawo min nan..." Ya faɗa tare da juyawa yana kallon
Farida data daskare a zaune ta kasa ko ƙwaƙƙwaran motsi hawaye sai zubowa suke a
idanunta, Girgiza kansa kawai yayi yana faɗin "Kuka ai yanzu kika fara yinshi
Farida, domin tun asali abunda na dinga gujewa faruwarsa kenan a tsakanina
dake...Nayi haƙuri har na kai maƙura amma Farida baki canza halinki ba, nayi
ƙoƙarin gyaraki amma baki gyaru ba...kin ɗauke ni tamkar ba mijinki ba, baki
maidani a bakin komai ba, baki san ki sauke hakkina dake kanki ba, baki san ki kula
da 'ya'yan da Allah ya baki ba...sai dai kullum kina yawon bin gidan bikin ƙawaye,
baki san ki tambayeni fita ba, sai dai duk lokacin da kikaso kiyi fitarki kuma ki
dawo duk lokacin da kika so ba abunda ya dameki, na nuna miki nima fa mai lafiya ne
ba dutse bane kuma dole ne in nemi hakkina a gurinki, amma yawon zuwa gurin biki ya
hana ki zauna ki kula dani da 'ya'yanki...kullum baki nan baki nan, kuma kinsan ban
ajiye wacce zata kula dani bayan ke ba, tunda ke kaɗai gareni baki damu da wane
irin hali zan shiga ba, kedai kawai abunda ya shafeki kuma ya dameki shi kikeyi,
'ya'yan da kika haifa kin barwa masu raino baki damu da tarbiyyarsu ba, baki damu
da halin da zasu shiga ba, kedai kawai ki tafi biki..sai kibar gidanki da mijinki
da 'ya'yanki babu abunda ya dameki, babu ruwanki da duk irin halin da zamu shiga,
Saboda Haka Dukkan abunda ya Faru Tsakanina da Mufeeda Keda Goggo kuna da Alhaki
akai..."
Ya faɗa yana Matse Ƙwallah, gaba ɗaya Falon ya Ɗauki Shuru banda Kukan Mufeeda dana
Farida sai Inna Fulera sai na Goggo Abu Dake Tashi ƙasa ƙasa, wani mugun kallo Baba
Hakimi ke Jifan Goggo Abu Dashi Lokaci Ɗaya Zuciyarsa na Lulluɓewa da Ɓacin Rai
kukan Tahir Tamkar Saukar Dalma ne Cikin Ranshi Cikin Tsawa yace "Kukan me kike
Zainabu...? Ai bai kamata kiyi Kuka ba Tashi zakiyi ki Taka Rawa kiyi Murna Kin Yi
Sanadiyar Lalata Rayuwar Ɗanki Wanda Kika Haifa da Cikinki. Tir Dake Abu Wallahi
Yawonki Da Girmanki Amatsayinki na Uwa bai amfaneki da Komai ba sai Sakarci Yanzu
ace Ɗanki yazo ya Sameki da Irin Wannan maganar ki kasa gayamin Abun baƙin ciki
kuma kin Hanashi ya Sanar dani..? Ke Har Kin isa ki gyara Abunda Allah bai gyara ba
Wato kin Hanashi ƙara Aure Amma baki Taɓa Tunanin ina zai kai Lalurarsa ba kanki
kaɗai kika sani Sai Wani Dalilinki mara Tushe Ballantana Makama, Wallahi Tallahi
ina so ki Sani Duk Zunubin dake Kan Tahir Akan laifin Zina Dake da Farida za'a
Rabawa Domin kune kuke da alhakin Duka Abunda ya Faru..Babu Abunda Zance miki sai
godiya kin kuma kyauta.." Ya ƙarashe Faɗa yana Share ƙaramar kwallarsa Data Zubo
mai Cikin Tashin Hankali.
Su Basma da Bassam da Muda da Laila Dake laɓe A koridon Ɗakin Basma Kuwa kuka Suke
Ka Shirɓan na Tausayin Kukan da Daddynsu yake Duk Abunda aka faɗa kaf Acikin
kunnuwansu Lokaci Ɗaya Sukaji Sun Tsane Farida da Komai nata ganin Itace Silan
Shigan Daddynsu Wani Hali Hartana Sanyashi kuka dama ba Tun yanzu ba Rashin Kula
Dasu da batayi yana Tsaye Acikin Ransu kuma Suna jin Haushin hakan gashi Dalilin
Sakacinta Ta saka Daddynsu Cikin wani Hali, Basma Da Laila Suka haɗa kai Suna kuka
yayinda Muda da Bassam Suma Suka Ɗora kai Agwiwa suma Suna ta kukan Tausayin
Daddynsu.
Goggo Abu ko Kuka Take ba Bakin magana Maganganun Hakimi Sun Shigeta Sosai Tahir
Kaɗai Take kallo Tana Jin Ta zama Sakaryar Uwa Mara Damuwa da damuwar ɗanta Data
Haifa da Cikinta Innaro ko Tana gefe Itama tana Sharan Ƙwallah Tausayin Tahir na
Jarabawar da Allah ya masa, Domin Wanna Jarabawa ce Domin Ajaraba Imaninsa Abba ko
Wani Kallo yake Wurgama Farida Dake Jikin Umma Tana Kuka Ita kanta Umma Kukan Take
Sharewa Lokaci Ɗaya Tana Faɗin "Muma muna da laifi ba Goggo Abu da Farida bane
keda alhaki Akan Wannan Abun ba Harda mu kanmu iyayen Farida bamu Taɓa Lura da Irin
Ƙararta da Tahir yake kawo mana ba, ko yazo ya Faɗama bama Nuna mata batayi Dai dai
ba sai ma Mu kama lallashinta Cikin Soyayya musamman ni dana kasance Uwa agareta
Wacce Nafi kusanci da Ita, Gatan da Muka Nunawa Farida Shiya Sangarta ta bata iya
zama Gidan Mijinta ta bashi Dukkan kulawa, Muma muna da Laifi Muna Dashi muma.." Ta
ƙarashe Faɗa Tana Sharɓan Kuka.
Abba yace "Haƙiƙa maganarki gaskiya ne Aliya muna da laifi Wajen Rashin Nuna ma
Farida Muhimmancin Mijinta Hakika bamu kyauta ba..kuma bamu kyautama Tahir ba Domin
Yayi Haƙuri da Ita Tun bayan Auresu, Dukkanmu bamu Taru mu Duba Halin da Tahir zai
Shiga ba..Duka laifin namu Ne sai dai muyi fatan Allah ya ya yafe mana Gaba
ɗaya..." Baba Hakimi ya amsa da Ameen Ishaq na gefen Tahir yana Ɗagoshi Amma yaƙi
ɗago kansa Saboda Hawayensa Sun kasa Daina zubo mata Baba Hakimi ya Kalli Inna
Fulera yana Faɗin "Fulera ki Daina Ma Mufeeda mugun baki kinji da Kunnenki Duka ba
laifinsu bane, Ki saka mata albarka ki kuma kalleta kice kin yafe mata Babu kyau
bawa ya Nuna Butulci ga Allah lokacin Daya Jarabceka da Wata Jarabawa Godiya zaki
ma Allah, kar in sake jin kin aibata 'yarki.." Ya faɗa cikin Sanyin Murya gyaɗa kai
Inna Fulera Tayi tana Kuka Lokaci Ɗaya Jikinta yayi sanyi Ta kalli Mufeeda Dake
Durƙushe Tana Kuka Lokaci Ɗaya tace "Na..yafe miki Mufeeda...Allah ya bamu ikon Cin
Jarabawarsa Haƙiƙa na Shaida ke yarinya ce mai Tarbiya Hakama Alhaji na yarda da
Ƙaddara ne ta Faɗa muku Domin Dattakonsa Data iyayensa Shike Riƙe damu Har yanzu...
Amma Ina Roƙon ku don Allah kada ku Zubar da Cikin ku barma Mufeeda Shi ƙila Wata
rana Shi zaiji kanta ko kuma ƙila Shi kaɗai ne ƙwanta a nan Duniya.." Farida dake
Jikin Umma ta ɗago Tana Faɗin "Wallahi sai yabi Rariya Uban Wa zata Haifa ma
Shege..? Ba anan gidan ba Wallahi sai an Zubar Dashi..."
Ta faɗa Cikin ƙaraji Da Kuka Abba ne ya mata Daƙuwa yana Faɗin "Kinci Ubanki,
Farida In na Sake jin bakinki Anan Wajen Wallahi sai naci Mutumcinki mutuniyar
Banza da Wofi.." Ya faɗa yana Hararanta Umma dai ƙwallah Take Sharewa Duk Jikinta
yayi Sanyi Su Goggo Abu kuwa An Shiga ƙwaryar Nadama.
Baba Hakimi ne yace "Dama waya ce miki za'a Zubar..? Haba kamar ba masu Hankali ba
kenan bamu yarda da Ƙaddara ba, taya zamu aikata Wani Zunubin kan Wani Zunubin
kuma..? Mufeeda zata Cigaba da Rainan Cikinta kuma ta Haifeshi da Ikon Allah Acikin
gidan nan Saboda Lura, Ɗanbatta ƙauye ne In Muka Tafi da Ita labarin zai yi Tambari
Gwara abarta anan Ɗin Harta Haihu muga Abunda Allah zaiyi..."
Zabura Farida Tayi Tana Faɗin "Awani gidan..? Wallahi ba a nan gidan ba..? Bata isa
ta haifamin Ɗan Shege a gida ba.." Tahir Dake Duƙe ya Ɗago da Jajayen idanuwansa
yace "Toh sai dai ke ki bar gidan, Amma Babu fashi kamar Yadda Hakimi yace Mufeeda
zata Haihu anan gidan Insha Allahu..." Ya faɗa yana mata wani kallon Tsana Baba
Hakimi ya saki Murmushin Takaici Amma ƙasan Ransa yaji Daɗin Amsan da Tahir yabama
Farida.
Kuka ta ƙara sakawa kafin tace "Haka kace..? Toh Wallahi sai dai na bar gidan ni
ban zauna ba...Bazan zauna gida Ɗaya da karuwarka wacce kama Ciki ba.." Umma ce ta
Make mata baki Tana Faɗin "Rufema mutane baki Mara Kunya Gaban iyayenshi kike gaya
mai magana Haka Irin Tarbiyar da muka baki kenan..?"
Ta faɗa Tana kallonta Cikin ɓacin Rai Durƙushewa Farida Tayi Tana Cigaba da Gunjin
kuka, Abba yace "Saurareni Da kyau Farida kinga matuƙar naji labarin kinbar gidan
Mijinki Wallahi sai na Saɓa miki Sakarya mara Hankali Wacce iliminta da shekarunta
basu amfana mata komai ba..Wallahi in baki Shiga Taitayinki ba Naji labarin kinyi
ma Tahir ko ita yarinyar Wani Abu sai nazo Har gida nan gaban 'ya'yanki na barki
Kwance ja'ira kawai.." Ya faɗa Cikin Fushi da Sauri Farida Ta Miƙe ta Haura sama
Tana Gunjin kuka gaba ɗaya Aka bita da kallo kafin Baba Hakimi ya kaɗa kai yana
Faɗin "Ayyah Ibrahim ga Wacce Girmanta da Shekarunta basu mata amfanin komai ba nan
Zainabu..ai ko banza ta Haifi Farida Tsakani ga Allah bata Fita Hankali ba..?" Ya
faɗa Cike da Takaici Goggo Abu Dake kuka ta Buɗe baki zatayi magana Baba Hakimi ya
ɗaga mata hannu yana Faɗin "Karma ki ɓata bakinki...Yanzu Maganarki banda ɓata min
rai Babu Abunda Zatayi Gwara ma ki rufe bakinki zai fi alheri agaremu Gabaki
Ɗaya.." Goggo Abu Tayi ƙasa Dakai Hawaye na Zubar mata tace "Attahiru ka
yafemin...Mufeeda kema ki yafemin.." Daga Haka ta miƙe ta Fita Zuwa Haraban Gidan
Tana Kuka.
Baba Hakimi ne yace "Fulera kama Ɗiyarki ku Shiga Ciki ki ƙara lallashinta kinji
itama ba laifinta bane.." Jiki ba ƙwari Inna ta Miƙe ta Kama Mufeeda Da ƙyar Dake
kuka Suka Nufi Ɗakinta Iya Dake gefe sai Lokacin itama ta Miƙe tana Sharan Ƙwallah
na Tausayin Waɗannan Ahalin Innaro Ta miƙe Ta Bita tana Faɗin "Kai ni Ɗakinki Iya
na kama Ruwa nayi sallah.." Da Toh Iya ta karɓa kafin su Nufi Ɗakinta Kowa
Zuciyarsa ba Daɗi.
Umma ma Miƙewa Tayi tana Faɗin "Bari naga Farida.." Kai Abba ya gyaɗa mata kafin Ta
Haura sama tabar Baba Hakimi da Abba da Tahir da Ishaq Suna ƙara Jajanta lamarin.
Umma Kwance Taga Farida na Kuka, gefenta ta Zauna Tana Faɗin "Farida...Bai kamata
kiyi kuka ba kamata yayi ki zauna kima kanki karatun ta Natsu ki gyara Kuskuranki,
ki kama Allah ki kuma Roƙi gafaran Mijinki ki Rungumi 'ya'yanki kinga Abunda ya
Faru..? Izina ne gareki da Kuma mata masu irin Halinki Daga ƙarshe ina Ja miki
kunne da ki Natsu In ba Haka ba Wallahi Dagani Har Abbanki zamu Ɗauki mummanan
mataki Akanki.."
Daga Haka ta miƙe ta Fice Daga Ɗakin Tana Fitowa su Baba Hakimi na Miƙewa, nan Suka
ce kowa ya Fito zasu Wuce Inna Fulera Data kai Mufeeda Ɗaki ta saka Gefen Hijabinta
tana Share mata ƙwallah Mufeeda na kallon Inna Fulera Take Fadin "Inna ki
yafemin...Ba laifina bane.." Murmushi Inna Fulera ta mata kafin tace "Na yafe miki
'Yata..Allah yayi miki albarka ya kuma Saukeki lafiya.." Jin Haka yasa Mufeeda Ta
Rungume Inna Fulera Suka Fashe da Kuka Lokaci Ɗaya, Iya Data leƙo kiran Inna Fulera
itama sai dai taji ƙwallar Sun kawo mata, muryan Iya ce ta saka suka saki juna Nan
take sanar da ita ta Fito zasu Koma.
Kumatun Mufeeda ta Shafa kafim tace "Ki kula da kanki kinji ko Mufeeda..? Allah na
Tare Dake..." Daga Haka ta saki Hannunta ta Fice Daga Ɗakin Tana Sharan ƙwallah kan
gado Mufeeda ta zame tana kuka mai Cin Rai tana jin kamar Bazata ƙara ganin Innar
ta ta ba kenan.
A waje Suka samu Goggo Abu bayan Dukkansu Sun Fito Innaro ce kaɗai ta samu yin
Sallah Sauran Baba Hakimi yace in Sun Isa gida kowa sai yayi..Abinci kuwa Da Iya Ta
jera ba Wanda ya kalleshi Motar Su Abba da Umma ce Ta fara Fita Daga gidan sai ta
Baba Hakimi Wanda Garzali zai Maidasu bayan Baba Hakimi yaja Tahir gefe ya ƙara mai
Nasiha sosai ya kuma Nusar dashi ya barma Allah komai Da Haka Suka rabu Bayan Motar
Ta Fice Daga Haraban Gidan
Ishaq ma bai koma gidan ba, Daga nan Sukayi sallama da Tahir ya Shiga Motarshi ya
Fice Daga gidan Bayan shima ya ƙara bama Tahir ɗin baki sosai...Ya Daɗe Tsaye yana
Sauke Tagwayen Ajiyar Zuciya Lokaci Ɗaya yana Goge Siririyar ƙwallar data Siraro
mai ya Juya ya tunkari Cikin Falon gidan.
*Anitha..*
*Aisha Alto..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty*💕
_*Muna Mika sakon godiya bisa ga masoyanmu na nesa Dana kusa,Bisa ga yadda suka yi
ta aikomana da sakon gaisuwa kama daga Masoyanmu na Whattapp da kuma Wattpad munga
tarin sakonninku na Ta"aziya muna godiya Sosai Allah ya bar zumunci Muna Fatan
Allah ya Sa Dukkanmu Fatima Binafa tazama mai Cetonmu Ranar gobe Kiyama Ameen..*_🤲
*BABI NA GOMA SHA HUDU*
""""Cikin Sanyin Jiki Da Takun Jarumta ya Shigo Falon,Babu Kowa ya Tsayawa yayi
Shuru yana Bin Dakin Mufeeda da kallo Wani Zuciya yana Tambayanshi Ko Wani Hali
Take Ciki..? Ganin bashi da Amsa ne ya sanya ya Kada kai ya Fara Kokarin Haura
Steps yaji Muryan Basma Tana Fadin"Daddy... "..
Da Sauri ya Juyo yana Kallonsu Ita da Bassam da Laila da Madu Sun Kuramai Ido
Fuskokinsu Cikin Damuwa da alamun ma Basma Tayi Kuka ne,Gabansa ne ya Fadi Kunya Ta
kamashi Yama manta Sam da yaran Da wani Ido Zai kallesu bayan Sunji Abunda ya
Aikata..? Cikin Karfin Hali ya Furta.."Basma Wht hpped....? Yafada Cikin karfin
Hali.
Kuka ne ya Kwace mata Da Gudu Ta Isa gareshi Ta Fada Jikinsa Ta kara Sakin Kuka
Kamar Wacce Aka Daka,Hakama Bassam Ya Rugo Shima ya Fada bayan Basma Shima yana
Kuka Tahir ya Rutse Ido kafin ya Dora Duka Hannuwansa bayan Yaran Nashi yana
Bubbugawa alaman Lallashi Idanuwansa ya Bude da Suka kara kadawa Sukayi Jajir ya
Sauke kan Muda da Laila Dake Tsaye Suma Suna Share Kwallar..
Hannu ya Mika Musu Alaman Su Taho Suma Da Gudu Suka Taho Suka Fada Jikinshi
Yahadasu ya Rumgume Cikin Kuka Basma Ke Fadin"We Relly Srry Daddy.,Momy Ta Cuceka
Daddy Mun yadda Muna Son Cikin Mufeeda Ta Haifama kani.."Take Fada kamar Wata Babba
Wani Yam Tahir Yaji Cikin karfi Hali ya Sakesu yana kallon Cikin Idanuwan Basma ya
Dafa kanta yana Fadin"Nothing To be Worry My Dota,Stop craying and Kar nakara Jin
Sunan Momy ku Abakinki balle kice ta Cuceni koma Menene She is my Wife Ku ma,Kuma
Mahaifiyarku ce So Stop All dis Kinji ko..?.
Gyada kai Tayi Tana Share Kwallarta Kafin ya Saki Kanta yana kallonsu Dukkansu
Cikin Karfin Hali yace"And All Dis..Don't let Anyone Know abount It kunji Ko
Amkaranta Karku Sake Kuyi Zencen da Wani Kuma Laila Koda Kun Koma Gida ko Mamanku
karku Fadamwa Kunji.."Kai Suka gyada Kafin Su Hada baki Suka ce"Insha Allahu Daddy
We are going To Hide Dis Secret.."
Mirmishin Dayafi Kuka Ciwo ya Hadiye kafin yace"Ok..Muda da Bassam Kuje kuyo
Alwala naji Ana Kiran Sallar Mangarib,ku kuma Ku Koma Daki Kiyi Taku sai Mun
Dawo ."Da kai Suka amsa kafin Kowannensu Ya Juya Basma da Laila Suka Nufi Dakin
Basma Hakama Bassam da Muda Suka Nufi Dakin Bassam Din Ko bakomai Zuciyarsu Ta
Warware ba kamar Dazu ba....
Sai da Suka bacemai kana ya Kada kai ya Fara Taka Steps Cikin Sanyi Jiki,ya Dade
Tsaye Kofar Bedroom Din Farida yana Nazarin Wani Abu kafin ya Cije Lebe ya karisa
Cikin Bedroom Dinshi Tiolet ya Fada agurguje yayi Wanka yazo ya saka Wata bakaer
Jallabiya da Hula ya Dau Carbinsa ya Fito,Afalo Suka Hadu dasu Muda Suma Sun Fito
nan da Nan ya Rike Hannayensu Suka Fita Zuwa Masallaci.
***
Mufeeda Kuwa Bayan Fitan Inna Fulera Kan Gadonta Ta Fada Tana Gunjin Kuka Wani
Tsausayin Kanta Dana Tahir na Kara Kamata Zuciyarta Tana mata Rawa In Ta Runtse Ido
Ta Tuno Sanda yake Mgana yana Zubar Hawaye bazata Jura ganin Hawayen Tahir ba Tana
Jin Abun Acikin Ranta Bata da yarda Da Zatayi ne.
Tana Cikin Wannan Halin ne Iyya Tazo ta Sameta,Zama Tayi Gefen Gado kafin Ta Dagota
Tana Fadin"Mufeeda...Mufeeda..."Tafada Tana Dago Fuskarta Wacce Tayi Faca Faca Da
Hawaye Sosai Cikin Mutuwar Jiki da Tsausaya Iyya Ta Fara Fadin"Mufeeda,Kibar Wannan
Kukan Kinji ko..? Bashi da Wani Amfani Tunda Mai Afkuwa ta Afkuwa...'Tafada Tana
Share mata Hawaye Da Hannunta Duka Biyu.
Kuka ya kara Ciyo Mufeeda Sai ta Sulale kan Cinyar Iyya Tana Yi Tana Fadin"Ya zanyi
iya..? Na batama Kowa Rai Ba laifina ba..Bansan Haka zata Faru ba Kuma Shima Daddy
ba Laifinshi bane Iyya,Momy zata Kasheni ina Jin Tsoro.."Idon Iyya ya Kawo Kwallah
Cikin Lallashi Take"Ayyah Bar Fadin Haka Mufeeda Babu Abunda Hajiya Zata Miki
Alhaji bazai barta Kibar Kuka babu Abunda zai Faru Kinji ko.."
Tafada Tana Dago Kan Mufeeda Lokaci Daya Tana Share mata Kwallah Mirmishin Yake
Mufeeda Tayi kafin tace"Nagode Iyya Akullum Ina kallonki Tamkar Inna tace..Nagode
Sosai.."Kumatunta Iyya Ta Shafa kafin Tace"karki Damu Mufeeda duk Abunda Ke Damunki
karki Boyemin ki Sanar dani Kinga yanzu bake kadai bane Kina da Yaronki Ciki Toh
yakamata Ki Kula da kanki kinji ko.."Kai Ta gyada mata Tana Mirmishi kafin
Tace"Insha Allahu.."
.
Mikewa Iyya Tayi Tana Fadin"Maza Ki Tashi Kiyi Sallah Nima bari naje nayi
alwala,Kafin Na Idar da Sallah Abincin ya Karisa.."Mufeeda Ta Mike Tana Fadin"Toh
Iyyah..."Har Iyya Ta Juya Zata Fita Mufeeda Tace"ahm Iyyah.."Iyyah Ta Waigo Tana
Fadin"Na"am Kina mgana ne Mufeeda..? Kai ta gyada mata kafin Tace"Eh nace Ina Naila
Take ne banganta ba..?
Iyyah Tayi Mirmishi Tace"Tayi barci Ammh Itama Tayi Ragimar Rashinki Tana Dakina In
Kin Idar da Sallah Kije ki Dauki Yarki "Tafada Tana Dariya Kafin Ta Fice,Mufeeda
Dake Tsaye ta Murmusa kafin ta Saki Ajiyan Zuciya Ta Shige Tiolet Din Dake Dakinta
Domin Dauro Alwala.
****
Farida Kwance Take Ruf da Ciki Tana Rafzan Kuka Ji Take kamar Zuciyarta zai Fashe
da Bakinciki Da Kishi Sun Taru Sun Mata Yawa Tana Ji kamar Tatashi Taje ta Shake
Mufeeda Ta Mutu Daga Ita Har Abunda Ke Cikinta.
In Ta Tuna Wai Tahir ya Hada Shimfida da Mufeeda Sai Taji Tafita Hayyacinta
babban Abunda Ke Kara Ruguza mata Zuciya Sai Cewan Datayi Mufeeda ta bar Gidan Ammh
Ko Kunya Tahir ya bude baki yace Bazata Tafi ba Kenan awannan Gidan Zata Reni
Ciikin Kuma Ta Haifeshi Tana Gani Ina Hakan Bazai Taba Yuyuwa ba Wlh bazata Iya
zama da Mufeeda Acikin gidan nan ba Duk Abunda Zai Faru Sai dai ya Faru
Hawayen Idonta ta Share Kafin Ta Sauko Daga Kan gadon Wayarta Dake Gefe Ta Dau
Tsuwa,Jawota Tayi Ta Duba Taga Daya Daga Cikin Kawayensu Tasan Kan mganar Bikin
kanin Bilkisu ne,Tsaki Taja ta Kife Wayar Acikin Ranta Tana Fadin Bata da Lokacin
Wannan Bala"in daya Tunkarota ya Isheta Tiolet Ta Fada Domin Dauro Alwala Tanayi
Tana Kuka Kamar Wata Karamar yarinya.
Gabadaya Ranar gidan Babu Sukuni Su Basma ne kadai Sukayi Dinner,Tahir Coffea Kadai
Yasha ya Koma Dakinsa,Mufeeeda ko Takasa Fitowa Falo Iyyah ce Ta Dauki Abincin Ta
kaimata Dakyar Ta Lallasheta Ta Iya ci Ta Kwanta Tana Ajiyar Zuciya,Ita ko Farida
Kofarta ma Arufe ne Kuma ba Wanda yama yabi Ta Kanta Duka Zukatan Haka Suka Kwana
Zuciyoyi ba Dadi,Hatta da Umma da Abba Suma Haka Suka Kwana Cikin Zullumi balle
Goggo Abu Wacce Tunda Suka Dawo Hakimi bai kara mata Mgana ba Domin yanaganin Duk
Itace Silan Faruwan Komai....
Bangaren Inna Fulera Kuwa Kwana Tayi Kuka Cikin Damuwa Gefe Daya na Zuciyarta na
Tsausayin Yarta yarinya karama Ta Shiga Cikin Jarabawar Rayuwa,Haka Tatashi ta
Dauro Alwala Tana ta kaima Allah Kukanta Kamar yadda Tahir ya Kwana Salloli yana
Neman Gafaran Allah kafin Safe yaji Zuciyarsa Tamai Sanyi Duk Nauyin Dadade Tanayi
Tun bayan Faruwar Lamarin Yaji ya Washr ko banza ya Rage kaso 74 daga Cikin
Damuwarsa.
***
Washegari Tun Karfe 8 na Safe Tahir ya Fita ko Breafsat bai Tsaya Yi ba,Domin baki
na Jiransu Ishaq Tun 7 ya Isa Shima ya Tadashi Daga barcin Daya Kwasheshi bayan Sun
dawo Daga Sallar Asuba Shida su Bassam da Muda.
Farida najin Fitar Tahir Tayi Zumbur Ta Mike Daga Kwancen Datake Domin Tana Ta
saman Steps Din Ta Hangeshi suna gaisawa da Iyya kafin ya Fice Da Sassarfa,Tana
ganin Haka ta Fara Saukowa Daga Steps Din Benen Tana Hada Hanya Bibbiyu Sanye Take
da Riga da Sikat Din Atamfa Tun na Daran Jiya,sai Wani Hijabinta Red Colour Wanda
Tayi Sallar Asuba Dashi,Iyyah na Kichen Tana kokarin Soya Kwan da Za"ayi Breafsat
Dashi Taga Wucewar Farida Da Sauri Kamar Ta Kifa Zuwa Dakin Mufeeda,Iyya Tayi Tsam
da Sauri kamar Ta Bita sai Wata Zuciyar Tace Bazata saba Mganar Iyayenta ba.
Mufeeda na Kwance Kan Gado Tana barci Gefenta Naila ce Itama barcinta Yadda Naila
ta Riketa Kamar Wasu Uwa da yarta Tsaye Farida Tayi Tana Binsu da Kallo Wani
Takaichi mai Hade da bakin ciki da Kuma Kishi Suka Taru Suka kara Tunzurata Cikin
Fitan Hayyaci Ta Karisa ga Mufeeda Daga Tsayen Ta Saka Hannu Ta Daka mata Duka
Abayanta Cikin Masifa tace"Tashi...Tashi Don Ubanki Yau zaki bar gidan nan Tunda
Bana Ubanki bane.."Take Fada Tana Kara Sakarma ta Duka Abaya
Kamar Amafarki Taji Saukan Dukan Tayi Firgigi Ta Farka Tana gyara zaman Doguwar
Rigar Barcin Dake Jikinta Cikin Fargaba da Faduwan gaba Ta kara Ware Ido ganin
Farida Tsaye Akanta tana Huci kamar Wata Macen Zakayan,Da Sauri Mufeeda ta Sauko
Daga kan Gadon Ko"ina na Jikinta na Rawa Tace"Ina..ina..kwa...kwana
Momy.."Rankwashi Farida ta Sauke mata akanta kafin Tace"Karki kara Kirana Mommy
Domin Ni ba Uwarki bane,Da"ace Kin Dauki ne Amatsayin Uwa da baki Hada Shimfida Da
Mijina ba,Mufeeda Kin Cuceni Mijina fa Kika Sani kuma Har yayi miki Ciki Kuma
Shikenan Don Ina Sakarya sai na barki Ki cigaba da zamamin Agida..? Tafada Tana
Nuna kanta Lokaci Daya Hawaye Duka Wankrmata Fuska.
Mufeeda da Hannunta Guda Daya ke bisa kanta Daya kuma yana Kan Bakinta tana Danne
Kukanta Cikin Wani yanayi da Firgici Take Fadin"Don Allah Mommy Ki..."Bata karisa
ba Farida Ta Wani ,mugun Dauketa da Wani Lafiyayyan mari sai da Ta Kife Bisa gado
Ta Fashe da Kuka wanda Hakan ya Tashi Naila Daga barci ganin Mufeeda na Kuka sai
Itama ta Canyara Kuka.
Iyya na Kichen Tana Kokarin Hada Kayan Karyawan Taji Kuka Daga Dakin Mufeeda Ga
Naila Taji Kukanta Da Hanzari ta bar Abunda Takeyi ta Fito,Da Gudu Zuwa Dakin
Mufeeda Daidai Lokacin Da Farida Takema Mufeeda Watsi da kayanta Dake Cikin
Wardrope Tana Fadin"Tashi..Maza Ki Hada Kayanki Cikin Jakarki yanzu zaki Barmin
Gida Bazaki Haifan Dan Shege Agida ba Kije Cutar da Kikamin Allah ya Sakamin.."Take
Fada Ta kara Watso mata kayanta Wasu Har kan Jikinta,Itako Mufeedan Sai Kuka Take
Kamar Ranta zai Fita tama Kasa Mgana,Naila Kuwa Rarrafowa Tayi Zuwa Wajen Mufeeda
Ta lafe Ajikinta Daukanta Tayi Ta Rumgume Tana lallashinta Tana Kuka.
Iyya Dake Tsaye Taji kwallar Tsausayin Mufeeda Sun Cika mata Ido,domin Farida ba
Abar Tsausayin Bane Duk Abunda ya Faru Tsakanin Alhaji da Mufeeda Itake da Alhakin
Kaso mafi Girma Aciki,Cikin Hanzari Ta Karisa Dakin Tana Fadin"Ashh...Hajiya me
yayi Zafi kuma..? Take Fada Tana Rikota Daga Rikito kayan Mufeedan Datakeyi Daga
Cikin Wardrope.
Cikin Hargagi Farida ta Fizge Jikinta Daga Na Iyya Tana Fadin"Babu Ruwanki Dani,Wlh
kinjima Na Rantse Sai Mufeeda Ta bar gidan yanzu.."Tafada Tana Zaro mata Jajayen
Idanuwanta Jin Haka yasa Iyya Tayi baya tana kallon Ikon Allah Farida tana Juyowa
Ta Saka Hannu Ta Fizge Naila Hannun Mufeeda Tana Fadin"U get me Right ko..? Toh
maza Tashi Tashi ko kuma na Watsaki keda Kayanki Zuwa Waje.."Tafada Tana Rike Naila
Wacce Ke kuka Tana Zille zille Ita Asaketa ta koma Wajen Mufeeda.
Mufeeda na Kuka Tana Tattara kayanta Tana Tusawa Cikin Babban Akwatunta Wanda
Faridan Ta Siya mata,Ita kuka Farida Kuwa Hawaye ke Zubarmata Saboda Fitina Mufeeda
na Zage Akwatin Farida ta Mikama Iyya Naila Tana Fadin"Rikemin Ita Iyyah.."Tafada
Tana Tunkaran Mufeeda Wacce Ke Tsaye Tana Kokarim Sanya Hijabin Dake Hannunta
Fizagar Hannunta Farida Tayi Lokaci Daya da Akwatin Kayan nataTafara Janta Zuwa
Falo Tana Fadin"Fito Muje Mufuka Macuciya Allah ya Isa Tsakani na Dake Mufeeda Wlh
bazan Taba yafemiki ba.."Take Fada Tana Kuka Lokaci Daya Tana Faman Jan Mufeedan
Har Tsakiyar Falon,inda Taci karo dasu Basma da laila da Bassam da Muda dake Tsaye
suna kallon Ikon Allah Domin Hayaniyar Faridan Ya Tadasu Daga barci.
Cikin Mamaki Basma Ta kalli Bassam shima ya kalleta Kafin Su maida Kallonsa kan
Farida Wacce Ke Jaye da Hannun Mufeeda Tana Kuka ga akwatunta,Cikin Siririyar Murya
"Mommy Ina zaki kai Mufeeda..?
Cikin Tsawa da Fada Farida tace"Gidan Ubanta zata Koma basma Ai nan ba gidan su
bane.."
Tafada Tana kara Jan Mufeedan Iyya Dake Biye da Ita Dauke da Naila Dake Kuka Cikin
Ranta Addu"a Take Allah ka Jeho Tahir yanzu Kowani babba Wanda zai iya Dakatar da
Farida Daga Kudurinta,Basma da Abun ya bata Haushi Kawai sai Tasha Gaban Faridan
Tana Fadin"A"a Mommy Kin manta Abunda Su Baba Hakimi Sukace Mufeeda zata Cigaba da
zama tare damu ko Bassam..? tafada Tana kallonshi Da Sauri ya Gyada mata kai ..
Farida Dake binsu da kallo Cikin Mamaki da Fushi Tace"Au..Allah Haka Sukace
kenan..? Tafada Cikin Salon Rainin Hankali Basma Tace"Eh mommy Harda Daddy ma Haka
yace.."Kafin Basma Ta kara Motsi Farida tace"Naji Masu Daddy ban Hanya na Wuce ko
naci Ubanki yanzu nan.."Basma Takura ma Farida Ido,idanuwanta Sun Cika da Kwallah
batasan Sanda Bakinta ya Furta"Haba Mommy meyasa Zaki yi haka..? Duk Abunda ya Faru
da Daddy KE CE SILA,domin da baki banzatar Dashi ba,Kuma baki Banzatar damu da
yanzu Muna Cikin Farincikin mu,Saboda Haka bazan Matsa ba Wlh bazaki Kori Mufeeda
ba.."Ran Farida ya baci Ta Saki Hannun Mufeeda Ta Dauke Basma da Wasu Tawagen
Maruka Tana Fadin"Ni ne zaki Fadama Wannan Mganar Basma.."
Bata Dauke Numfashi ba Taji Itama an Wanketa da Maruka Har Biyu Sai da Tayi Taga
Taga Zata Fadi kafin Ta iya Tsayuwa da Kafafunta Cikin mamaki Take bin Wanda ya
mareta da Kallo Tahir ne Tagani Tsaye Akanta yana Huci Gefe Daya yana Binta da Wani
Matsayin kallo Domin Tun Mganar Basma na Farko yake Tsaye bakin Kofar Shigowa
Falon,Ya Dawo Daukan Wasu Fayels ne Daya manta Dasu yau Bai Fita Dasu Shine yana
Shigowa Falon yaci karo da Abunda Farida Keyi nan da nan Fushinsa ya Dawo Sabo
kusan Mai Hakuri bai iya Fushi ba.
Baya Taja tana Tsiyayan Hawaye Tana kallonshi Cikin Tsoro Domin Batasaba ganin
Tahir Cikin Wannan yanayi ba Cikin Kuka tace"Ni ce nayi Asara Tahir...? Ni Farida
ni ka mara gaban ya"ya da Yan Aiki.."Ya Taso mata yana Fadin"Amm mareki Di n ko
zaki Rama ne..? Bari ki ji na gaya miki na Fada Kuma zan Kara Fada Wlh Baki isa Ki
kori Mufeeda Daga gidan nan ba Sai Dai ke in kin ga bazaki iya ba ga Hanya nan ba
Wanda ya Rikeki Dama Banga Uwar Da kike Tsinana mana ba Dake da babu Ke Zamu Rayu
So in Kin Fita wlh zanfi Kowa Jin Dadin Hakan.."Yafada Duka Jijiyon Kansa na Tashi
Saboda Bacin Rai.
Farida Dake Kuka Jin Kalaman Tahir sai ta kara Volume din kukanta Cikin Firgici
Take kallom Tahir Tana Girgiza kai ko kallonta Baiyi ba yace"Basma Dauki Akwatun
Mufeeda ki kaimata Daki.."yafada Lokaci Daya yana Wucewa Ta gaban Farida ba zato
kawai Mufeeda Taji ya kama Hannunta zuwa Dakinta yana Fadin"Naga Uban da zai sake
yunkurin Koronki Tunda Shima ba Gidan Ubanshi bane Domin Da Gumin Aikin Danikeyi
Aka sakamin Dashi Kinga ko baki da Iko Akanshi.."Yafada yana Rike da Mufeeda Zuwa
Cikin Dakinta Basma na Biye dasu Abaya da Akwatun Mufeedan Tana Mirmishin Jin Dadi.
Farida Dake Binsu da kallo Wani Bakinciki Da Kishi Suka Kusa Kada Ita Cikin Kuka ta
Zura da Gudu Zuwa saman Tana Haura Steps Tana kuka,Har Ta Shige Cikin Dakinta ta
banko Kofa,Bassam da Muda da Laila Suka Bita da kallo Iyya kuma Dake Rumgume da
Naila Wacce Tayi Barcin Wahala Ranta ya mata Dadi ko Banza yau Alhaji ya Burgeta
Sosai,Ta tabbata Farida zata kara Dawowa Cikin Hayyacinta.
*One love*😍
*SHAKIRA..*
*AISHA ALTO*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
Yafada Haka kafin ya kai ya Fice Daga Dakin da Sassarfa,basma Dake Tsaye ta Kariso
Kusa da Ita Tana lallashinta Tahir yana Fita yaci karo da Iya Tsayawa yayi yana
Fadin"Iya don Allah ki kula da Mufeeda..."Iya Ta gyada kai Tana Fadin"Insha Allahu
Alhaji.."
Sama ya haye Cikin Dakinsa ya Shiga Daga ganin yadda yake Komai Cikin Hanzari
zaka Fahinci yana Cikin bacin Rai,Cikin Sauri ya Dauki Duka Fayels din ya Fito
Garzali Dake Waje yana Jiransa ya Shiga Mota Suka koma Campany Wanda Tunda ya Dawo
Ishaq ya lura kamar Ranshi abace yake ba Haka ya Fita ba bai mai mgana ba Sai da
Suka Dawo Masallaci Sun Shigo Office Din Tahir din
Kan Wata Kujera Dake Cikin Office din Ishaq ya zauna yana Fadin"Kai inaga fa zan
Koma gida cikina yana ta Kiran Ciroma.."Tahir Dake zaune kan Kujeran gaban
Tuburansa Ya Dago yana Fadin"Allah Sarki kuda Kukayi Dace kenan Mu ko Mun koma muda
banza Duk Daya While sai ka Dawo ni kila sai la"asar in zan Koma gida na Biya na
Siya Fura ."
Ishaq ya gyara zama yana Fadin"Tahir meya Faru ne..? Dazu Bayan kaje gida Dauko
Wadanan Fayels din ka Dawo Ranka bace.."Ajiyar Zuciyar Tahir ya Sauke kafin ya Mike
yana Fadin"Nida Farida ce Wato Ishaq Farida Muguwar Yar Rainin Hankali ce Ayadda
nakeji yanzu kamar na kamata nayi ta Duka Gabadaya na Doramata kaso mai girma na
Abunda ya Faru Domin Data Kiyaye Hakokina na aure da Duka Haka bata Faru
ba.."Yafada yana Saka Duka Hannuwansa Ciki Aljihun Wandonsa.
Ishaq yace"Me kuma ta Sakeyi..? Tahir ya waigo yana Fadin"Zuwa nayi na tarar da Ita
zata kori Mufeeda Daga gidan.."Ido Ishaq ya zaro yana Fadin"Kabari don Allah...?
Tahir ya kariso Kusa da Ishaq ya zauna yana Fadin"Wlh Allah ina gayamaka tana Kuka
Wai Tana Fadin Ta Cuceta Ishaq can u juz imaging Wai Farida na Kuka saboda ni Tahir
na Ma Mufeeda ciki.."Ishaq ya saki Dariya ahankali yace"Dama tana Sonka Tsabar
Iskanci ne ke Cinta nayi Takaichin Abunda ya Faru Tahir Duk da bawa bai isa ya
Gujema kaddaransa ammh Ta wani Fanni naji Dadi ko banza Lokaci yayi da Farida zata
girbi Abunda ta Shuka.."
Tahir ya kuramai ido yana kallonsa kafin yace"Kamar yafa..? Bangane ba..? Tashi
Ishaq yayi kafin ya Sakala Duka Hannuwansa Akirjinsa kafin ya Fuskanci Tahir yana
Fadin"Eh mana Ai ada Tana ganin baka da Wani amfani Awajenta,Tana ganin ka Daga Ita
sai kai yanzu kuwa Dole zata Shiga damuwa Domin Tana Sonka auren Soyayyah Kukayi
bana Kiyayyah ba So Dole Farida tayi kuka Kishinka Take Tahir.."Shuru Tahir yayi
kafin ya Jinjina kai yace"Hakane..,? Toh ai Ta makara Sai dai komai yagama
lalacewa.."Ishaq yace"Shine ake Jiyemata Tun Farko Kada tayi Nadamar Dole Wacce
bata da Wani Amfani.."
Mikewa Tahir yayi kafin yace"Wannan ya Rage nata Ishaq Abunda na sani Shine Matukar
Farida tace zata matsama Mufeeda Wlh Itama zata Shiga mtsala na Fadamata in batason
ganin Mufeedan agidan zata iya komawa gidansu ban Hanata ba ."Ishaq yace"Ina
bayanka Wlh gwara ka Nuna mata Kuskuranta Tun yanzu.."
Kusa dashi Ishaq yazo Lokaci Daya yana Dafa kafadarsa Cikin Sigan lallashi
yace"Daga goggo Har Farida nasan Haka zata Faru dasu kayi Hakuri zasu Daidaita ammh
kaima kasan Dole Baba Hakimi yayi Fushi mganar Kunya kuma Don Allah ka saki Jikinka
ba Wanda zai san Wannan Mganar bayan mu da muka sani kuma ko Ansani Bafa laifinka
bane Kaddara ne kuma Bawa bai isa ya kaucemata ba.."Ajiyar Zuciya Tahir ya Sauke
kafin yave"Hakane Nagode Sosai Ishaq Da bansamu Amini kamar ka ba Dabansan Wani
Hali zan Shiga ba.."Mirmishi Ishaq yayi kafin yace"Nima Haka da Ban Hadu da Amini
kamar ka da na Tafka Asara.."Atare Suka saka Dariya kafin Ishaq yace"Allah ya Sauki
Mufeeda Lafiya,Ammh sai nake ganin kamar yarinyar tayi kankanta da Haihuwa
fa.."Wani kallo Tahir yayi mai kafin yace"Nima fa ina Mamaki kaduba kagani
yarinyarnan kamar kara ammh Ta iya Daukeni Tsaf.."Ishaq ya Buga Kafadarsa yana
Fadin"Bugu Daya ko Mallam Kasaka Kwallo Araga.."Ture Hannunshi Tahir yayi yana
Fadin"kaifa Dan Iska ne Zahra ta bata ka.."
Ishaq na Dariya yana Fadin"Yan Iska dai Mallam kadinga saka Mun jaye.."Shuru Tahir
yayi kafin yace"Wani Hanzari ba Gudu ba,ya Zan yi da Mufeeda bayan Ta Haihu..?
Ishaq yayi Shuru Shima yana Wani Tunani kafin yace"Mubar Wannan Mganar Fatarmu dai
Allah ya Sauketa lafiya Insha Allahu bazai gagaraba."gyada kai Tahir yayi kafin
Ishaq yace"Bari na Kira Zahra ta saka Direba ya kawoma Abincin nan kawai sai muci
ko..?
Tahir na Shafa Cikinsa yace"Daka Agaza kuwa Domin nafara ganin Hazo hazo.."Dariya
Ishaq ya saka kafin ya fice yana Laluban Zahra ta Waya Shiko Tahir komawa yayi
yazauna yana Auna Mganar Yadda zai yi da Mufeeda bayan Ta Haihu..? Wata Zuciyar
tace In ta yaye Abunda Ta Haifa sai ka mata Aure ka bata jari..,Toh wazai Aureta
bayan Ta Haihu..? Babu Wanda ya chanchanta ya Aureta sai kai Tahir.."Wata Zuciya ta
karantamai da Sauri yace"A"a Bazai Yuyu ba Naso kaina Dayawa bayan na lalata mata
Rayuwa kuma na Tursasamata zama dani Tana karamar yarinya bazan yi Haka ba.."Yafada
Afili Cikin Karayar Zuciya Lokaci Daya Tsausayin Mufeeda na Ratsashi Runtse Ido
yayi Yana Tunanin Wani kariya zai Bata saboda Farida Domin yadda ya Zuciya da
Farida indai Tace zata Takura Ma Mufeeda Zasu samu babban Mtsala.
****
Farida Kuwa Tunda Ta Shiga Daki Tafada Bisa gado Tana Gunjin kuka kamar Zatayi
Hauka Gabadaya ta Birkice Haka take Buga kanta bisa katifa Tana Kuka Hannuwanta
Dafe da kanta bayan Ta Barbaja Gashin kanta Ya Watse kamar Wata Kamun Hauka Cikin
Ranta da Zuciyarta kamar Ta Buga Saboda Kunci Da bakinciki.
Duk bayan Kowacce Dakika sai kalaman Tahir Sun Fado mata arai Wani Jiri take gani
Idanuwanta Sun kode Saboda Kuka Tana ji acikinta Ranta Tahir ya gama da Ita Tuni
Shedan yamata Zugan dama Duk karya ne plan ne Tahir ya Shirya dama Sun Dade Suna
Cin Amanarta Shida Mufeeda munafukar Allah,Ji Takeyi ayanzu Duk Duniya bata da wata
makiyiya kamar Mufeeda Tanajin bazata iya Rayuwa acikin gidan Nan Tana kallon
Mufeeda da Cikin Tahir ba Watarana Bakinciki zasu Sa Zuciyarta ta buga Ta Fadi ta
Mutu .
Cikin Hanzari ta Mike Daga kan Gadon Wajen Jerin Akwatunanta Karamin Ciki Ta Dauko
Ta Budeshi Bisa gado kafin Ta Bude Wardrope dinta Tana Debo kayanta tana Sakawa
Gefe Daya kuma Tanayi Tana Share Kwallah,Sai da Cikata kafin ta maidata ta Rufe
Tana kuka Ta Dauki Wani Hijabin Data Cire Wanda Ke Jikinta Duk gayun Farida Yau
batama Tuna da Wani Abu ba Waishi Wanka balle Kwalliya,ta dauko Akwatin kenan Wata
Zuciya tace"Farida ina zaki..? Kawai Taji bakinta ya Furta Kano lokaci Daya kuma
kalaman Abbanta ya Fado mata Kuka Takara sakawa Kafin Ta koma Bakin gado ta Zauna
Tana Faman Sharan Kwallah Cikin Ranta Tana Tunanin bayan Kano bata inda zataje
kuma,Danbatta..? Kai ina..? Bazai Yuyu ba Ko Naje chan Duk Daya ne Goyon bayan
Dansu zasu yi Toh ina yakamata Naje..? Kai Tsaye Wata Zuciyar Tace"gidan
Bilkisu..."
Tuna Haka yasa Ta saki Mirmishin Karfin Hali kafin Ta mike Har Ta kusa Ficewa Ta
Tuna Da Wayarta tazo Ta Dauka Ta Fice Cikin kunar Rai Take Saukowa Daga Stairs tana
Bin Dakin Mufeeda Dawani kallo har ta kariso Tsakiyar Falon kenan Sai ga Laila da
Basma Sun Fito Daga Kichen Laila na goye da Naila Ita kuma Basma na Dauke da Wani
Jug ahanunta Da alama Lunching Suke Shiryawa bayan su Kuma Iya ne Dauke da Wasu
Manyan Food Flaks kallo Daya Farida Tayi musu Ta Dauke kai bata kara kallonsu ba Ta
Nufi Hanyar Ficewa...
.
Cike da Mamaki Basma ke Fadin"Mommy ina zaki..? Afusace Farida ta Waigo Tana
Watsama Basma Harara kafin Tace"Inda Ubanki Tahir ya aikeni zani Don Kakarki Goggo
Abu.."tafada Idanuwanta Sun kada Sunji Jajir Daga Basma Har laila balle iya baki
Suka Rike Suna salati acikin Ransu Iya ce Tayi Saurin Cewa"Subhanallah...Haba
Hajiya Wannan zagin bai kama..."Dallah Malama ki Rufan baki Tsohuwar
Munafuka.."Farida ta katse Iya Tana Fadin Haka ..
Ido kawai iya ta sakamata batare Datace komai ba,Baya Farida ta Dawo Tana Nuna Iya
da Yatsa Kafin tace"Nasan Duk Abunda Tahir da Mufeeda Suka Taru Suka aikata kina
sane ammh Dayake ke Tsohuwar Munafukace Shine kika munafunceni ko .? Toh kema
kinsan Da sani Karshen Aikin ki yazo Acikin gidan,Zan Tafi na barma Tahir gidan
Tunda Dama Burinku kenan Daga ke Har Mufeedan In Kinji ko kuma In kun Burgeni ku
Maye masa Gurbina da Mufeeda kodon Taimakon Shegun ya"yan dazasuyi Ta
Haifa.."Tafada Tana Watsama Iyan Wani kallo Lokaci Daya da Mufeeda Wacce Taji
Mganar Faridan Ta Fito tana Tsaye Kofar Dakinta tana Kuka..
Wani Mirmishin Kuka Farida Tayi kafin ta Dauki Akwatunta ta Fice da Sauri Su Iya
Suka Marata baya,Basma ce tafara Juyawa Zuwa Saman Dining ta iJiye Abunda Ke
Hannunta da Gudu Ta Nufi Hanyar Dakinta tana Kuka Laila ta marata Baya Cike da
Tsausayi Iya Kuwa Jikinta Asanyaye ta Karisa Jera Kololin Abincin Bisa Dining kafin
Ta Waigo Tana kallon Mufeeda Cikin Kulawa tace"Kidaina yawan Kuka Mufeeda bashi da
Alheri..Kiyi Hakuri Daman Dole zaki Fuskanci Haka Allah ya baki Ikon Karban
Kaddaranki Hannun Bibbiyu.."Daga Haka Ta Shige Kichen Tana Shara Kwallah Aranta
Tana Ji ko Farida bata Koreta ba ita da kanta zata Tafi Tunda Gidan ya Rikice komai
Babu Dadi,Dama Babu Abunda Ta Nema Rasa na Rayuwa Domin Danta ya samu Aiki Ta
Dalilin Tahir Kawai Karamcinene da Mutumcin shi yasa Take Zaune Dasu Haryanzu Ammh
Lokaci Yayi da zata koma gida...
******
_Anguwan SARKI_
Bilkisu Kawar Farida ce Wacce Sukayi Mkranta Tundaga Secondry Har Zuwa Buk,Course
Daya Suka karanta kuma Suka zo Sukayi Aure A kaduna sai dai Ita Bilkisu Ta Riga
Farida Aure da Wajen Shekara Daya da Rabi,Tana Cikin Wadanda Suke Zuga Farida
acikin Kawayensu Duk da ko Ita ba Haka take Tafiyar da Gidanta ba Ko yar Aiki bata
Dashi sai Wata Tsohuwa mai Zuwa tana mata Wanke Wanke da Wanki Shima Sai Mijinta ya
Fita tazo Tagama aikinta ta tafi ya"yanta Hudu yanzu Haka kuma bata Tsaida Haihuwa
ba Ammh Tana Daga Cikin Wanda Suka Zuga Farida kan Ta Tsaida Haihuwa Hakannan Dama
Duk Inda ka zama Sakarai sai Ana nuna maka Hanyar da zaka sake bi ka kara
Sakarcewa.
Farida da Motar Ta Fita Zuwa Gidan Bilkisu Tana Driving Tana Kuka Lokacin Data
Shigo Babban Falon Gidan Bilkisu Tana Zaune kan Kujera Tana Waya da kaninta Wanda
zai yi Aure Sai ga Farida ta Shigo Tana kuka Abun yabata Tsoro da Hanzari ta yanke
Kiran Ta Mike Tana Fadin"Fari Mezan gani Haka..? Mutuwa Akayi..? Farida bata samu
zarafin mgana ba Illa Zubewa datayi jikin Bilkisu Ta saki kukan Datake yinshi
Acikin Zuciya
Riketa Bilkisu Tayi Cikin Tashin Hankali Take Fadin"Na Shiga Uku Fari wai meya
Faru..? Basma ce Ta Rasu ko Shi kanshi Tahir din ne Wani Abu ya sameshi Kaina ya
Kulle Don Allah ki gayamin Abunda Ke Faruwa...? Farida Ta Dago Daga Jikin Bilkisu
Tana Fadin"Billy Tahir ya Cuceni...Tahir ya gama Dani Billy Shida Mufeeda Sunci
Amanata..."Take Fada Hawayenta Suna Kwararowa
Idanuwan Farida na Runtse Hawaye Suka kara Kwaranyomata kafin ta Gyada kai Cikin
Kuka tace"Kwarai Da Gaske..."Nan ta Shiga labartamata Abunda ya Faru Tundaga Farko
Har Karshe Ai sai Bilkisu Ta Mike Tana Fadin"Kutumar Uba..Lalle Tahir Mugun dan
Wasa ne Wato Fyade yayimata baya Cikin Hayyacinsa Kajimin Matsiyacin Mara Mutumci
da Kima Wato Shine Iyayensa Suka Taru Suka Marama Dansu baya Saboda Tacewa Ke kuma
gaki banza Sakarya sai ki zauna Araini Cikin Shege agabanki ko..? Farida na Share
Hanci Tace"Abunda ke sakani Kuka kenan Billy Bansan Iya Adadin Tarayyar da Tahir
yayi da Mufeeda Ba Bilkisu ammh Duk da An batamin ba Wanda yaga laifinshi sai ma
laifina ake gani Daga Karshe Cemin yayi Mufeeda bazata bar Gidan ba Sai dai ni in
nagaji na kara gaba."
Billy tace"Jar Uba..!Lalle Tahir Mugun Dan Iska ne,Haka yace...? Tafada Tana
Girgixa Jiki batai Tunanin Magidanci kamar Tahir Tana Surfamai Zagi,Farida ta gyada
kai kafin tace"Shine Dalilin Dayasa na Taho Tunda Umma da Abba ya mallakesu ko na
Koma Bazasu Taba Saurarana ba Kirufamin Asiri ki barni na zauna Awajenki Har Tahir
yagane Kuskuransa.."
Bikisu Tayi Shuru Cikin Nazari Farida Ta kalleta Tana Share Kwalla tace"Ko da kwai
Mtsala ne..? Ajiyar Zuciya Bilkisu ta Sauke kafin Tace"Ba mtsala in ma Dashi Abban
Su Walida ne,ammh komai ke zanyi mgana Dashi in ya Shigo Tashi na rakaki Dakin da
zaki Sauka bazan bari ki koma gidan Tahir ba Domin Cuta kam an Cuceki Wlh Cikin
Shege Acikin gidanki don Wulakanci ma Mafi kaskanci Mai Renon Yarku Gaskiya Tahir
ya bata Wayonsa Kuma girmansa ya Zube Acikin Idanuwata.."Tafada Tana Daukan Akwatin
Farida Tatashi Suka nufi Wani Korido Suna Tafe Billy na Tsinema Tahir Wanda Har
Azuciyar Farida Tana Jin Zafi ammh bata da yarda zatayi Tunda Ita ta Tona ma kanta
Asiri.
Daki ne Mai Dauke Da gado da Wardrope sai Madubi da Tiolet ba laifi ko"ina Tsab
Tsab nan Bilkisu Ta Fita ta barta Zuwa Kichen Ta Zubomata abinci Domin Duka yaran
nata Suna Islamiya Fargaban Bilkisu Daya Megidanta Wanda yake da Zafi Sosai In Har
yaga Farida tadawo Gidan sai yaji Dalili Kuma Akwai sanayyah Sosai Tsakaninshi Da
Farida Har da Shi kanshi Tahir din Ita kuma bataso ma Tahir yasan Farida na gidanta
sai yagama Wahalan Nemanta tukunna Hardai ta Zuboma Farida Abinci bata samu Mafita
ba Tana ta Dai Tufka tana Warwara Tsoro ya cika Ranta Saboda Tasan Abban Walida bai
da Wasa.
****
Tahir kuwa bai da lbrin Farida bata gidan Domin Bai Dawo Daga Office ba sai bayan
Isha"i Suna Zauna Suna Duba sakon Wasu Sabbin Samfur din Motoci Cikin Laptop din
Tahir din Shida Ishaq basu ma gama ba Suka Rabu Akan Tahir zai karisa Komai kafin
gobe koda ya Dawo ya Biya ya Siyo Furanshi yana Shigowa,kafin ya Shiga Dakinsa ya
Fara Biyawa Dakin Su basma ya Tarar dasu suna kallon Cartoon Oyoyo Sukayimai ya
Rumgumesu yana Tambayansu ko Sunci Abinci Tsaraban Furan Daya Siyo ya basu kulli
Daya kafin yayi musu Saida Safe Daganan ya Shiga Wajen Su bassam ya samesu Shida
Muda Suna buga Game,nan Suma Suka Tashi Suna mai oyoyo Shafa kansu yayi yana
Tambayansu lafiyansu Suma Furan Guda Daya ya basu kafin Daganan ya Fito yaja musu
kofa,Dakin Mufeeda ya kallah har zai Wuce sai kuma ya kasa Cikin Sanyin Jiki yanufi
Dakin Nata yana Tura Kofar yaganta Kwance Kundundune chan Tsakiyar gado Cikin bargo
Tana barci Bai Shigo ba Daga Kofar Dakin ya Tsuramata ido yana kallon Karamar
Fuskarta Cike da Tsausayi Wani Abu na Tasomai Daga Kasan Zuciyarsa Ajiyar Zuciya ya
Sauke kafin ya koma Da baya ya jamata Kofar.
Yana Shirin barin Falon ne yaji Muryan Iya na Gaisheshi Da Sauri ya Waigo yana
amsawa Cikin Sanyin Murya Iya tace"Alhaji Naila na Wajena Saboda ganin yanayin
Mufeedam.."Gyada kai kafin yace"Bakomai kin kyauta.."Har ya Juya ta Sake Fadin"Amh
Alhaji dama Ina son mgana dakai in ba Damuwa.."Cikin mamaki Tahir ya Waigo kafin
yace"Mgana kuma...? Toh Shikenan iya Kibari da Safe kafin na Fita Ki Tunamin yanzu
Dare yayi.."Jinjina kai Tayi kafin Tace"Shikenan Allah ya Tashe mu lafiya.."Da
Ameen Ta amsa Har ta Juya zata Tafi ya Kirata ta Waigo ya mikamata Fura guda Daya
karba Tayi tana mai Godiya Daganan ya mata sai da Safe ya Haura sama ko kallon
Dakin Farida baiyi ba.
Sai da yagama Duka al"adansa na Kwanciya kafin ya Dauko Laptop dinsa ya Dora Bisa
Gado ya Haye Tsakiyar gadon ya Cigaba da aikinsa Lokaci bayan Lokaci yana Kurban
Furar Daya Tsiyaya Cikin karamin Kofin glass bai kwanta ba sai Wajen 1pm kana ya
Kashe komai ya koma ya Kwanta bayan yayi Addu"ar barci.
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
"""Tahir Ya Fito Cikin Fitanshi na Zuwa Office yana Sanye Cikin American Suit
Dinsa,Black and White ya matse Wuyansa da Tie yana Dauke da Brifcase Dinsa Lokacin
daya Sauko Kasan Falo Ya Iske Basma da Laila da Bassam da Mudu suna zaune Bisa
Dinining Suna Breafsat Suna ganinshi Kowanne ya Washe baki Suna Fadin"Daddy gud
Mrning...?
Karisowa yayi yana Fadin"Mrning my Childreen How was Ur Nite.."Suka amsa da Fine
Kan Basma da Laila ya Dafa kafin yace"Laila da Mudan Hutunku ya kare Fa Tun last
Week ko .? Kai Suka gyadamai alamar Hakane Numfashi ya Sauke kafin yace"Ok Bari na
Dawo Kila ko Zuwa Gobe Ko Jibi Saturday Sai mu maida ku gida ko..? Kallon Junansu
Sukayi kafin Suce"Toh Daddy.."Suka Fada Suna Dariya Jin Harda Bassam zasu Rakasu
gida.
Teburin yabi da Kallo kafin yace"Ina iya da Mufeeda Bazasu karya bane..'Basma ce
tace"Bamu sani ba Daddy ammh iya Ta Dibarma Mufeeda Ta kaimata Daki Tundaga nan
Data Fito sai Ta Koma Dakinta Bamusan Abunda Ya Faru ba.."Basma Taa Fada Tana
kallon Tahir din Kafin ya samu Zarafin Mgana Bassam ya karbe da Cewa"Eh mana Daddy
Gidan Duk ba Dadi Mufeeda bata Fitowa yanzu Iya ma kamar Akwai Abunda ke Damunta
yau Duk kamar ba Ita ba.."Yafada cike da Kewa Irin Abun bayamai Dadi.
Shuru Tahir yayi kafin ya saki Ajiyar Zuciya yace"Ikon Allah Meyafaru ne..? Basma
tace"Bamu sani ba Daddy Kila Ita da Momy ne kafin Tatafi.."Da kallo yabi Basma Baki
bude kafin Yace"Tatafi..? Faridar bata nan ne..? Ina taje..? Ya jero musu Tambaya
Lokaci Daya.
Basma ta Zakuda kafada kafin Tace"Bamu sani ba Daddy Tadai Tafi Har iya ta mata
mgana Ta kusa Zaginta.."Ido ya zaro yana kallonta ganin Haka yasa ta Shiga maidamai
Abunda ya Faru,Jinjina kai ya Hau yana Jin Wani Bakinciki na Ratsashi,Wato Duk
Bayan Rusamai Rayuwa da Farida Tayi bai Isheta ba sai Tabi gari Ta gama Tonamai
Asiri ko..? Domin yana da Tabbatacin Bata je Kano Domin bada Safenan ya samu Wayar
Umma,bayan Sun gaisa Ta kara bashi hakuri game da Farida Tare da Fatan zasu zauna
Su Rungumi kaddaransu kuma yanzu bads Dadewa ba Suka kara Mgana Da Abba duk da
Mganar Business ne ammh da Farida Taje kano Jiya Dayaji lbri,Shi ba Wannan bama
Damuwarshi naga Goggo Abu Domin Innaro da Ashe Sun Kirashi Awaya Suna Sanar Dashi
ya Kokarta yazo Domin Baba Hakimi yayi mugun Fushi da goggo Abu baya Shiga Dakinta
kuma yahanata Shigowa Turakarsa kuma Baya Shiga Sabgarta Tayi kuka Tanuna Nadamarta
Ammh Baba Hakimi yayi Burus Da Ita Innaro ma Data Nemi Shiga Mganar Hakimi yaja
mata Kunni da Kakkausan Muryan Kan in Ta sake ta Kara Shiga Mganar Itama zai
Jingine ta Gefe Kamar yadda ya Jingine Goggo Abu..
Jin Haka yasanya Goggo Abu Ta Rikice sai Zazzabi da Ciwon kai Kafin kace kwabo ta
Kwanta Ciwo koda Likita yazo Dubata sai Iske Jininta yayi bala"in Hawa nan Dai ya
Dubata ya bata Mgunguna,ammh Duk da Haka Baba Hakimi bai Sakin ma Ra"ayinshi ba
Koda ma akayi Haka ko Shashen Goggon Abu bai leka Ba gefe Daya kuma Inna Fulera na
gida kwance ba lafiya Tun bayan Dawowarsu Hakimi ne Dayaji Lbri yasa Innaro da Ashe
Suka Tafi Suka Dubata itama nan Suka Isketa jiiki yayi Zafi Maman lantana ke Kula
da Ita Koda Suka zo suka Fada Hakimi bai Bata Lokaci ba ya Saka Aka kaita Asibitin
garin Danbatta,Itama dai Damuwar ne ya Rafketa Hawan Jininta ya Tashi Gado Aka bata
sai da ta Kwana Daya da Wuni kana aka sallameta Saboda Haka gabadaya Hankalinshi
ba"a Kwance yake ba yana Jin Damuwarsa na Saka Ahali Dadama Damuwa gashi ya
Lalatama Mufeeda Rayuwa da Farincikinta Gabadaya Saboda Shi bata da Sakewa kamar
baya.
Tsam yayi yana kallonta Cike da Mamaki kafin yace"Alright..."Juyawa yayi zuwa
Dakin Mufeeda ammah Kuma Acikin gangar Jikinsa babu karfin Gwiwa Turo kofar yayi Ya
Shiga da Siririyar sallama bata Jishi ba Tana Zaune Dirshan Akan gado Naila na kan
Cinyarta Kanta ba Dankwali sai Kitson Shikon Dake kanta Wata doguwar Rigar Roba ce
ke Jikinta Kirar Bhrain,Kofin Shayi ne Ahannunta Tana Sha gefenta kuma Farantin
Silba ne Cike da Kwai da Dankwalin Turawa Wanda Iya ta Kawomata Naila ce ke mika
hannu Tana yafiton kofin Shayin Cikin Sanyin muryanta tace"Nailata zaki Sha Shayi
ne.."Kamar tasani ko Ta daga kai Dariya Tayi Har Fararen Hokoranta Suka bayyana
Kofin takafa mata abaki Tana bata kadan Kadan Tana Sha,Gefe Daya kuma tana gutsurin
kwan Tana bata Tana Fadin"Zan Cigaba da baki Abincin aboye Nailata bana so kiyi
Rama.."Itako Naila batamin Jinta malulan kwanta Take Cike da Jin Dadi.
Tahir Dake Tsaye bakin Kofa ya saki baki da Hanci yana Kallonsu Gefe Daya Wani
Tsausayin Mufeeda ke kara Tasiri Acikin Ranshi ga Naila Wacce in ya kalleta sai
yaga ko Hakkinta Allah ya kama Farida dashi bazata Taba Jin Dadin Duniya ba,Ganin
Basuji Shigowarsu ba ya Sanya yayi gyaran Murya da Sauri Mufeeda Ta Dago Daga bama
Nailan kwai abaki ganin Tahir Tsaye sai ya kara Rikita ta Rude,Ta Riko Naila Lokaci
Daya Tana Kokarin Ijiye Kofin Shayi bisa Side Drower sai bai zauna Dakyau ba Da
Hanzari Tahir ya Isa Wajen ya Rike Kofin Lokaci Daya yana Dauke Farantin kwan
Tsurama Mufeeda ido Cikin Cikin Sanyinsa yace"Shiii..Is ok..Relax.."
Ya Fada yana Daidaita Natsuwarsa yana kuma kara gyara zaman Brifcase dinsa Dake
Hannunsa,Cikin Kunya da Wani Nauyi Mufeeda ta sadda kai Tana Fadin"Ina..ina kwana
Daddy..."
Bai amsa ba sai da ya Ijiye Brifcase dinsa gefen gadon Mufeeda ya mika Hannu ya
Dauki Naila Wacce Tunda ya Shigo Take mikomai Hannu kafin ya amsa yana Fadin"Lafiya
lau kin Tashi lafiya..? Ya fada cikin Kunya kadan Domin bayason ma yana kallon
Kwayan Idanuwanta.
Itama Kunyar Takeji Shiyasa Bata Dago ba tace"Lafiya lau.."Shuru ya biyo bayan
Mganar Mufeeda,Wacce kanta ke Kasa Duk kunya Ta gama kamata na Halin da Tahir ya
Isketa Wata Zuciya tace"Me zaki boye Abunda Yagama Dake.."Dam Take taji Hawaye Sun
Cikamata ido Shi kuma cikin Nazarinta ya Furta"Ya Jikin ki..? Kina jin Wani Ciwo
Acikin jikinki..?
Shuru Tayi kafin ta girgiza mai Batayi mgana Illah Hawayen Data Rikewa ne Suka
zubomata,Tsam yayi yana kallonta tana Share Kwallah cikin Tsausayawa ya Durkusa kan
Gwiwoyinsa yana Rike da Naila yace"Don Allah kiyi Hakuri mufeeda kiyafemin laifin
Dana aikata agareki Hakika na zama azzalumi Kuma naci Amana,Ina Jin kunyar kaina
Mufeeda.."Yafada Cikin Rawan Murya.
Dagowa Tayi ganinshi Durkushe agabatan Yasa Tace Da Sauri."A"ah Daddy Meye Haka..?
Don Allah katashi Ni Tun Daren da Abunda ya Faru Zuciyata ta yafemaka bayan ta
tabbatar bazaka Taba aikata Haka da gangan ba.."Tafada kai Tsaye Tana Dauke
Hawayenta Mikewa yayi Jikinsa Asanyaye kafin yace"Nagode Mufeeda,Ki sanar da Iya
duk sanda Kikaji Wani Chanji Ajikin ki kinji ko .? Cikin Ladabi Ta Daga kai Da
cewa"Toh Daddy.."Dan Mirmishi yayi kafin yace"Gud gal..Kuma kiyimin Alfarma zaki
saki Jiki kamar baya,Kinga su Basma basajin Dadin ganinki Haka.."Kanta na Kasa Ta
Dago da Niyyar mgana Suka Hada ido yadda idanuwansa ke Narkar da Zuciyarta yasa
Tayi Saurin Sadda kai Tana Fadin"Insha Allahu Daddy.."
Mganarta Tamai Dadi Cikin Farinciki ya Furta.."Allah yayi miki albarka,ga Diyarki
zan Fita aiki kada na Mkara.."Yafada yana mika mata Naila Wajen saka Hannuwanta ta
karba Hannuwansu Suka Hadu Waje Daya Wanda Dukkansu sai da Sukaji Wani Shock
Atare,Mufeeda Tayi Saurin Jan Hannunta Tana barin Jiki Shi kuma yayi Saurin
Doramata Naila kan Cinyarta,Lokaci Daya yana Daukan Brifcase dinsa ya Fice Daga
Dakin da Sauri da Kallo Mufeeda ta bishi Zuciyarta na Bugawa batasan Dalili ba Tun
Zuwanta gida nan Indai zata ga Daddy Toh Zuciyarta Ta hau buguwa kenan da Sauri
Sauri kamar Wacce Tayi Gudun Tsere..
Yana Fitowa yaci karo da Iya Dauke da Ghana must go Cike da Kaya Su basma na
Tambayata ina Zata,taci ko Lullubinta Cikin Mamaki ya Karisa Kusa Dasu sai Dai
Sukaji Muryanshi yana Fadin"Iya lafiya kuwa..? Ina zaki da Wannan kayan..?
Jin Muryansa yasa Iya Ta Durkushe Kasa Tana Fadin"Alhaji kayi Hakuri da Abunda zan
Fadamaka,Na yanke Shawaran zan bar aiki agidan nan bawai Dom kun Saba min ba ko
kuma kuna min Wani abu A"ah sai domin Tsira da Mutumcina.."Cikin Wani Haushi Tahir
ya Furta.."Kan Issues din Farida ne ko..? Yafada Cikin bacin Rai bai bama iya
Zarafin mgana ba yace"Tunda Muke Zaune Dake Acikin Gidan nan Iya na Taba Saba
Miki..? Iya ta Girgiza kai Tana Sharan Kwallah Ya cigaba da Fadin"Su basma fa..?
Nan ma ta girgiza kai ya kada kai yana Fadin"Toh Tunda babu Daya iya babu Inda
zakije matukar Ni Tahir Mansur Danbatta ina Raye,Koda Farida Take Takama Ta
Dalilinta Kikazo Gidan nan bata da Ikon Koranki Saboda Nima karkashin Ikona
Take,saboda Haka mganar Gaskiya babu Inda zakije kina Tare damu Mudin Rai.."Yafada
kai Tsaye kafin yace"Basma,Laila ku kama Jakar iya ku maida mata Ciki ni na Fita
sai na Dawo .'Yafada kai Tsaye yana Wucewa Cike da Haushin Farida ji yake kamar ya
yanke Duka alakan Dake Tsakaninsu Wata Zuciya tace"Not Now Tahir..Juz leave her to
pay Wht She Didt For u.
Iyya bata da yadda Ta Iya Su Basma Suka ja jakarta Zuwa Cikin Dakinta Suna Murna
Harda Su bassam Ihunsu ya Fito da Mufeeda Ita da Naila Tana Tambayan Lafiya nan
Basma Ke Sanar Da Ita Itama Murnan Tayi Jin Tahir ya Hana Tafiya Tana ji Acikin
Ranta In iya Tatafi ai Ta kara Shiga bala"i Fitowar Mufeeda yasa gidan ya kara Dadi
Tun Tana Dari Dari dasu Basma Har Ta sake ganin basu kyamaceta ba sai ma Kafa kafa
Da Sukeyi Da Ita Hakama iya Motsi kadan Sai Sunje meke Damunta Ita Tsausayi Su
basma Ke bata ganinsu yara ammh Susan Matsalolin Rayuwa Da yawa.
******
*DANBATTA*
Ranar Asabar Tun Safe Tahir Da Basma,bassam da laila da Muda Garzali ya Debesu Zuwa
Danbatta bayan Tahir ya cika Muda da laila da Sabbin kaya da Kayaan kwalama,gefe
Daya kuma an Cika Booth da kayan Abinci Aka bar Mufeeda Da Iya agida da Naila,
Wacce da zasu Tafi idanuwanta Suka Cika da Kwallah ganin Haka sai Tahir yace in
zata Ta Shirya Harda Iya Su Tafi Gabadaya ammh Sai Mufeeda Tace bazata jeba Ta
Shige Daki da Gudu Tana Dannen Kukanta Domin Tana Tunanin Da zarar Taje Danbatta
Nunata Za"ayi Tayi na Cewa Tayi Cikin Shege kuma Inna Fulera yanzu batazatayi murna
da Zuwanta ba Shiyasa Tace bazata Je ba Ta koma Daki Tana Kuka Abun ya Taba Ran
Tahir Har Suka Isa Danbatta kanzil bai ce ba Gabadaya Rayuwarsa batamai Dadi Daya
Tuna da Abunda ya Aikata ma Mufeeda sai yaji Duk ya Tsani kanshi.
Baba Hakimi na Waje da Jama"arsa Motar su Tahir Ta Tsaya Tunda Hakimi yaga Tahir
yazo Aranshi yace mganar Zainabu ne,Shiyasa Ko Fuskar bai Sakarmai ba bayan Yaran
Sungama gaisheshi Suka Shiga Cikin Gida Shi kuma ya Tsaya Waje Suna gaisawa da
Jama"a Kafin ya karisa gaban Hakimi ya zauna yana Tankwashe kafa,Yau din yana Sanye
ne Cikin Wani yadi kalan Sararin Samaniya Da Hulansa Zannar Bukar kallon Farko
zakamai ka Fahimci yayi Rama Sosai sai Dogon Hanci Kai Tsaye ya mika ma Hakimi
Hannu yana Fadin"Barka da Safiya Ranka ya Dade..".
Kai Tsaye Baba Hakimi ya kalleshi kafin yayi mirmishin Takaichi yace"Dama na sani
Tunda na Ganka nasan kazo kan Mganar Sakaryar Uwarku ce,Uhmm.."Yafada yana Kallon
Gefe Dayake babu Kowa saman Tabarman Tunda Tahir ya kariso Aka Watse aka barsu Su
Zanta,Gaban Tahir ya Fadi ya Dago Yana kallon Baba Hakimi Cike da Firgici Domin
Tunda yake da iyayensa bai Taba jin makamacin Wannan mganar yana Shirin Bude baki
yayi Mgana Baba Hakimi ya Dakatar Dashi bayan ya Dagamai Hannu yace Cikin kakkausan
Murya"Tashi ka Shiga Ciki zan Shigo yanzu Tunda kaima ka zama Sakarai mata na
Walagigi Dakai baka iya Katabus.."Kunya Ta kama Tahir ya Sosa keya kafin ya mike
yana Fadin"Ashigo lafiya..'"Ko kallonsa Baba Hakimi baiyi ba Domin Shima Haushinsa
yakeji yadda ya biyema Shirmen Mata baizo ya Sanar Dashi Mtsalanshi ba,Da kallo ya
bishi har ya Shige Gidan Idanuwansa Suka kada kamar yayi ma Tahir Kwallah Shikenan
gareshi kwara Daya Tal kamar Dubu ammh Abu Tayi Sanadiyar Jefa Rayuwarsa Cikin
Garari Bazai kyale ba Dole ne ya Nuna mata Kuskuranta Iskancin banza Wautar Wofi
Zumunci me?na Cuta da Rashin gaskiya,Haka Hakimi keta Fada Shikadai Acikin Ranshi.
Tahir Sashen Innaro yafara Zuwa Sai ya Tarar Bata Ciki Tana Shashen Goggo Abu kai
Tsaye ya Nufi Shashen Goggo Jikinsa Duk ba Dadi na Abunda ke Faruwa Tsakanin iyayen
nashi Ta Dalilinshi,Da sallama ya Shiga yana Kokarin Tube Takalmin kafanshi Ashe
Dake Zaune Gefen Goggo Abu Dake Kwance Kan Cafet Ta Tada kanta da Filo Ta mike Tana
mai Sannu da Zuwa sai Innaro Dake gefenta ,su Basma Kuwa nadaga Gefe Sun Jeru kamar
masu karban gafara,
Karisowa yayi yana Amsa ma Ashe Cikin Kulawa gefe Daya kuma yana kallon Goggo Abu
Dake Kwance Duk Ta Rame kamaer ba Ita,yana Kokarin zama Kusa da Ita Innaro
Tace"Sannu Attahiru..? Dago da kansa yayi yana kallon Innaro Cikin Kunya Domin
Kunyar Kanshi yake da Abunda ya aikata Hatta Ashe bai iya Hada Ido da Ita ba,Kansa
ya Sadda kasa bayan ya saka Hannu ya Rike Hannun Goggo yana kallonta Tana Kallonshi
Itama Idanuwanta Suna Taruwa da kwallah.
Innaro Tace"Karka damu Attahiru kadai jin Wani Iri mu iyayenka ne Munfi kowa
saninka Mu bar Haka amatsayin Gaddara mu Fuskanci gaba,Domin Hakimi yayi Fushi
Sosai kan Goggo Wlh har yau bai Tako Falon nan ba Balle yazo ya Dubata Nayi mgana
abanxa Daga Karshema yace In ban Cire baki na ba sai ya sabamin.."Tafada Kamar Tayi
Kuka,Dago da kansa yayi kafin yayi mgana goggo Ta Fara Kokarin Tashi Da Sauri Ya
Saka Hannu yana Taimaka mata Ita kuma Ashe ta saka mata Filo Abayanta ta Jingina
Suna Jeramata Sannu Atare
Kai goggo Abu Ta gyada Tana Share Hanci Tafara Mgana"Attihiru Don Allah ka Yafemin
Na cutar da Rayuwarka na Zama Sanadiyar Fadawarka Wani,Hali Wlh bansan Abun ya Wuce
Misali ba Na zata Farida mai Jin mgana ne,Gashi Ta sakani Cikin Fitina nayi
Sanadiyar da D'ana yayi Zina yayi ma Wacce ke kallonsa matayin Uba Ciki..Kaico na
Ni Abu gashi Babanku na Fushi Dani Ina zan Saka Raina naji Dadi.."
Tafada Tana Kuka Sosai,Tahir yayi Shuru yana kallon Goggo Zuciyarsa na Gudu Bayansa
ya Waiwaya da Niyyar yama Su Basma mgana su basu Waje sai yaga wayam Sun Dade da
Ficewa Tun Sadda Innaro Ta Fara mgana,maida Hankalinsa Yayi kan Goggo Abu kafin ya
Saka Hannu ya Riko Hannunta Cikin Tsausayawa yana Fadin"Bakomai Goggo Don Allah
kidaina bama Kanki laifi,Nima ina da Laifi Tunda na bari Tuntuni Farida Tafi
karfina ban Isa na gayamata Taji ba,Abunda ya Faru Tsakanina da Mufeeda goggo bamu
Isa mu Tsallakeshi ba Domin Rubutattace ne Daga Rabbil Izzati,Kidaina damun kanki
kinga Jininki ya Hau,ki,Daina damuwa Indai Mganar Baba Hakimi ne Abunda ya Kawoni
Kenan zan mai mgana Kuma Insha Allahu zai ji mganata Kinji.."Yafada yana Kallonta
LokaCi Daya yana Sanya Hannu yana Share mata Hawaye,Hannunsa ta Riko Tana kallonsa
kafin tace"Nagode Attahiru Allah yayi Maka albarka.Allah ya Kare Gaban ka da
Bayanka ya Raya maka Zuru"a,.."Da Ameen yake amsawa Su Innaro na Tayashi.
Cikin Alhini goggo Abu Tace"Ina Mufeedan? Fatan dai bawata mtsala..? Itama Inna
Fuleran Sai da Ta Kwanta Asibiti.."Tahir yace"Lafiyanta kalau goggo ba Wata Mtsala
sai Abunda ba"a Rasa ba,Eh Ashe ta sanar dani kafin na Wuce zan Shiga na Dubata
kuma na Nemi Izinin Hakimi kan ya bari na Tafi da Inna Fuleran Kaduna Kila Dukkansu
In Suna ganin Juna Hankalinsu ya Kwanta."
"Kul..karka Fara Ban Amince ba Kuma Ban lamunta ba.."Sukaji Muryan Hakimi Daga
Bakin Falon yana Shigowa Gabadayansu Suka Mike Banda Goggo Dake Zaune Tana
kallonshi Cikin Fada Baba Hakimi yace"Ka Barta anan,Kawai ka kyaleta zata Warware
Damuwa ce Kuma Ta zama Dole Domin barin Fulera garin nan Zargi zai Hau kan Mutane
Har Daganan lbrin ya Shigo Gari Abunda bana Fata kenan.."jinjina kai Tahir yayi
kafin yace"Hakane Ranka ya Dade An bar mganar.."
Tahir da Ashe Suka kalli Juna Cikin Rauni Tahir zai yi Mgana Kenan Innaro Ta
Rigashi Da Fadin"Haba Ranka ya Dade sai Hakuri,Tunda Abunda Ake Gudun ya Riga ya
Faru..."Ke Salamatu Rufemin baki.."Hakimi ya Katseta Cikin Fada Da Fushi.
Shuru Tayi Tana Kallonshi Cikin Nunata Da Yatsa yace"Kul Ki kama bakinki Kan Wannan
mganar in ba So kike na Saba Mii ba,kina Wata mganar Banza Inda Tun Lokacin da
D'anta yazo mata Bukatarsa Ta Saurareshi Haka Zata Faru..? Nace Haka zata Faru..?
Yafada Cikin Tsawa kafin ya Cigaba Da Fadin"Dalilin Rashin Sauraranshi Shi ya Jawo
komai,Banta ba Jin inda kaki naka kaso bare ba Zumunci Iskanci ko na Cuta Tunda Ita
Faridar batasan Ciwon kanta ba Su kuma Iyayenta Sun saka mata ido toh mu sai mu bar
Rayuwarmu Da'nmu Ta lalace ..? Ammh Saboda Sakarci,Kina babba Ki Haifi kamar
Attahiru,Da Aisha ammh baki da Wayau ko kadan,Zumuncin Dakike Mgana Ba Dalilina
Kikasan Ibrahim din da Aliyan ba..? Haka Kurum Saboda baki Daukeni Da Daraja ba,
Kika Dakatar Dashi Wai kada ya sanar Dani Sai da Abu ya Kwabe Kana kizo kina Kuka
kina Nadama Lokacin bata da Amfani.."Yafada yana Nuna goggo Da Yatsa Cikin Fada.
Ashe da Tahir dai ba Baki Domin yau kam An kure Baba Hakimi ba Kasafai Yake Fada ba
Sai an Kureshi,Hakurinshi Tahir ya Kwaso yana Saba Babban Rigansa yace"Ke ni bari
ma Kiji Haushinki nakeje Wlh kamar na Makeki Abu,Shiyasa na Kyaleki ki Girbi Abunda
Kika aikata Kin Cucu kanki ne Domin Ita Farida ba Ita kika batama Rayuwa ba
Marainiyar Allah kika saka Cikin Gararin Rayuwa kuma sai Allah ya Sakamata akanki
Domin Duka Laifin na Attahiru ya Rataya a Wuyanki ne Zainabu.."
Yafada Lokaci Daya ya Juya yana kokarin Ficewa Daga Falon Goggo Abu ko Banda Kuka
Babu Abunda Takeyi Innaro na Tsaye Ba bakin mgana Tahir ne ya Bi bayan Hakimi yana
Fadin"Baba...Ka Tsa..."Kai Saurareni nan Attahiru.."
Hakimi ya Katseshi bayan ya Waigo Sagale Tahir yayi yana Kallon Hakimi Wanda
yakallesa Shima yana Fadin"Bari kaji na Fada maka zaka batama kanka Lokaci ne Indai
Akan Mganar Abu ne,Gwara Tun Wuri kazo ka Wuce Sabgar ka zaifi maka in kuma ka
Dameni Wlh Allah Harda kai zan Hada na ci Muku Zarafi Domin kaima ina Cike dakai
yadda ka zauna mata na Kwallo da Rayuwarka kajima na Fada maka.."ke Aisha...?
"Fitio Maza Ki Tarkata ya"yanki ki Wuce gida kaima ka Tarkata naka ka koma bakin
Aikinta Ku barta Ta Shiga Nadamarta Ita kadai.."Yafada yana Ficewa Daga Falon.
Gabadayansu Jikinsu yayi Sanyi bamai Kwakwaran Motsi sai Kukan Goggo Abu Dake Tashi
Kasa kasa.
*Shakira*.
Anitha*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
""""Riƙe ƙugu Tahir yayi yana Sauke Ajiyar Zuciya, gefe Ɗaya kuma Zuciyarsa na Gudu
Sosai Saboda Damuwa, Ashe ce Dake gefe Ta ƙarasa Kusa da Goggo Abu Ta Zauna Kusa da
Ita Kafin Tace "Goggo..."
Ta faɗa Tana kallonta Innaro Dake Tsaye Ta Ɗora Hannu Bisa Haɓa Tana Faɗin "Wai
Hakimi meke Damunshi ne..?Tunda nake Dashi ban taɓa ganin yayi irin Wannan Fushin
ba.." Tahir ya waigo ya Fara Taku Zuwa Kusa da Goggo Yana Faɗin "Ranshi yana
ɓace...Dole a saurara mai Har ya Sauko Da kanshi.."
Ya faɗa yana Zama gefen Ashe, Dayan Hannun ya kama yana Faɗin "Goggo Don Allah Kiyi
Haƙuri kibar kukan nan Haka nan Nayi miki alƙawarin Komai zai Daidaita Insha
Allahu..." Ya faɗa yana Kallonta Goggo Ta Murmusa Tana kallon Tahir da Ashe kafin
tace "Bakomai...Allah yayi muku albarka Ku Tashi ku Tafi kubi Umarnin Mahaifinku.."
Ta faɗa Tana ƙoƙarin Ɓoye Hawayen Da Suka Taru acikin ƙwayan Idanuwanta.
Innaro ta saki Numfashi Tana Faɗin "Shine kawai magana Don Rashin Tafiyar Naku ma
Matsala ne, ku Tashi ku Tafi Insha Allah komai zai zo da Sauƙi, maganar Mufeeda
kuma Iya ta Dinga Kula da Ita Saboda yarinya ce..ko Goggo ya kika gani..?" Hannunta
Ta zare cikin na Tahir kafin ta saka Hannun ta Share Ƙwallarta Tana Faɗin "Eh Hakan
ma yayi Innaro, Allah ya Sauketa lafiya kabiya ka gaida Fuleran karka manta.."
Gyaɗa kai yayi kafin yace "Insha Allahu.." Har ya Miƙe Innaro Tace "Ya ita
Faridan...? Ina Fatan ba Wata matsala...?" Jinjina kai Yayi kafin yace "Eh Innaro
ba Wata Matsala..."
Sauke Numfashi Tayi kafin tace "Masha Allah...Ko jiya naji Mahaifinta suna Waya da
Hakimi kan mganar ne, Allah Ubangiji ya kawo mana Komai Da Sauƙi..."..
Gaba ɗaya Suka amsa da Ameen Kafin Ashe da Tahir suyima su Goggo Sallama Suka Fice
Suka barta Tana Share Ƙwallah Fita Sukayi Inda yabama Garzali Umarnin ya Shiga da
kayan Abinci Zuwa Cikin Gidan Hakimi, A ƙasa Suka Taka Shida Ashe Har Zuwa Gidan
Inna Fulera, Wanda Suna Tafe Tahir na Faɗama Ashe Abunda ya Faru da Wanda yake
Faruwa yana gaya mata kamar ya Zubar mata Da Hawaye, Cikin Tausayin Ɗan'uwanta Take
Lallashinsa Take bashi Shawaran karya Damu, kuma ya ƙyale Farida Duk inda Zataje
Zata Dawo ne bayan Duniya ta koya mata Hankali ya yarda Da Shawaran Ashe Duk da A
lokacin Farida bata da wani Fari Acikin Zuciyarsa.
A haka suka isa Gidan Inna Fulera, Ashe ce Ta fara shiga Suka Gaisa da Inna Fulera
da Maman Lantana kafin tace musu Tahir zai Shigo Cikin Sauri Maman Lantana ta gyara
Tabarma Tahir ya Shigo ganin Maman Lantana ne Awajen yasaka Daga Ashe Har Tahir ba
Wanda ya Tada maganar Illah Sunkuyar da kai Da Tahir Yayi kunyar kansa na Ƙara
kamashi ganin yadda Inna Fulera ta Rame Lokaci bayan Lokaci Tana Share Ƙwallah...
Basu Wani Daɗe ba Tahir ya Miƙe zai Tafi bayan ya bama Ashe 30k yace Tabama Inna
Fulera, Ashe na Bata taƙi karɓa Sai Ta Fashe da Kuka Lokaci Ɗaya Ta Ɗago ido Tana
kallon Tahir bayan ta Ɗago Daga Kwancen Datake Maman Lantana Tana gyara Mata Filon
Kanta Saboda Taji Daɗin Zaman Sosai.
Cikin Muryan Ciwo da Kuka Inna Fulera tace "Alhaji....."Ta faɗa Muryanta na
Sarƙewa, cikin Sanyin Jiki Tahir ya Tsaya cak kafin ya Waigo Zuciyarsa na Tsinkewa
Sosai Cikin Muryan Sanyi da Roƙo tace "Bana Buƙatar Kuɗinka Alhaji Abu Ɗaya Nake da
Buƙata Awajenka.." jikinsa na Rawa ya Dawo ya Duƙe agaban Inna Fulera yana Faɗin
"Ki Faɗi Abunda Kike Buƙata komai kike Buƙata matuƙar na Mallakeshi zan baki Shi
Inna.." Ya faɗa Cikin Karaya..
Muskutawa Tayi kafin tace "Ba komai nake Bukata ba Illah ka Riƙe min Mufeeda
Tsakani ga Allah...Ka zama gatanta..!kaji ƙanta..! Ka jibanci lamarinta...! Ka zama
garkuwa a gareta Alhaji Domin Duk Duniya Mufeeda bata da Wani gata bayan kai..Don
Allah kar ka barta tayi kukan maraici In kamin Wannan Abun Ka gamamin komai kuma
Bana Buƙatar Wani kuɗi ko Kawan Duniya Farin cikin Mufeeda kaɗai Shine Burina
Alhaji.." Ta faɗa Tana Rushewa da Kuka, Maman Lantana Dake gefe kanta ya Ɗaure amma
bata kawo komai ba sai ta barshi a ƙila zafin Ciwo ne ke Damun Inna Fuleran.
Ƙuri Tahir yama Inna Fulera da Ido kafin ya maida kallonshi kan Ashe Wacce
Idanuwanta Suka Cika da Ƙwallan Tausayin Inna Fulera Iska mai Zafi ya Furzar kafin
yace "Girman alƙawari Inna Ba Abu bane mai Sauƙi, Amma Duk Da Haka Nayi miki
Alƙawarin zama Gatan Mufeeda, Nayi miki alkawarin bazan bari Mufeeda Ta ƙara kukan
Wani Abu ba...Sai na zama Silan Murmushinta anan gaba.." Ya faɗi Haka Idanuwansa
Sun kawo Ruwa kafin ya miƙe da Sauri ya Fice Saboda Yadda Inna Fulera Ke kuka Tana
Godiya sai yaga Kamar Bazata Tashi ba, Lokaci Ɗaya kuma Kunyar Abunda ya aikata ke
Dawo mai Har Ashe ta Fito yana Tsaye yana Maida Hawayen Idanuwanshi Haka Suka Jero
Har Zuwa gidan Hakimi ba Wanda ya ƙara magana, bai koma Cikin gidan ba Ashe ya
umarta data cema su Basma Su Fito Tare Suka Fito Dasu Laila sama sama yayi ma
Hakimi sallama suka Shiga mota Har da Ashe Har gidanta Suka kaita Kafin su Sauketa
ita dasu Muda da Tsarabansu 20k yabama Muda da Laila ita kuma Ashe ya kara mata 10k
ta ƙara Da Wanda ya bama Inna Fulera Taƙi karɓa Haka Motarsu Ta Ɗaga Ashe Ita da
'ya'yanta Suna Daga maSu Hannu Har Suka ɓace ma ganinsu.
Sai yamma Suka Shigo Kaduna Tahir na Sauri Ko Gida bai Shiga ba Garzali ya Juya
Dashi kamfani ya samu Kiran gaggawa bai Dawo ba sai Dare Lokacin kowa yayi barci
iya kaɗai ya Tarar Farke, Mufeeda Ita da Naila Sun Daɗe da yin barci gaisawa sukayi
sama sama, kafin ya Haura Zuwa Ɗakinsa Ransa Duk babu Daɗi ko yayi Wani Motsi sai
ya Tuna da Alƙawarin Inna Fulera wanda Maganar da Suka gama Tattaunawa da Ishaq
kenan kafin Su Rabu gaba daya Abubuwa sun mai yawa yanzu Farida bata gabanshi
Matsala Goggo ce Sai Tausayin Mufeeda Daya ƙi barinshi Su sukafi Zama Cikin Ranshi
Suka Hanashi Sukuni.
****
Farida kuwa Tana gidan Bilkisu Wajen Kwananta Uku amma basu ci karo da Mijin
Bilkisu ba mai Suna Aliyu Saboda Tun Safe yake Fita kuma sai Dare yake Dawowa, Sai
ya Fita Farida ke Fitowa Haka Kuma kafin ya Dawo Bilkisu zata san yadda Tayi Ta
Hillaceta ta koma Ɗaki Abunda ke bama Farida Mamaki yadda Bilkisu ke Rawan Jiki da
Abban su Walida in ya Dawo Haka zata Tsala Wanka, Taci Gayu Tana Kwakwarsa, In ko
Ta mata sallama bata ƙara sakata a ido sai Washegari bayan ya Fita, Amma kuma Tana
Daga Cikin masu bata Shawara ko Acikin group ɗinsu na makaranta Kan Mace ta Daina
sakarma Namiji amma Ita gashi Bata Iya Haɗa komai da Mijinta.
Wani Abunda baima Farida Daɗi ba Shine yadda Bilkisu Ta Dinga yaɗa Abunda ya Faru
Wajen Sauran Ƙawayensu Waɗanda basu san Meke Faruwa ba Haka Suka Haɗu agroup ɗinsu
na Classic Ladies Sukayi Ta Tsinema Tahir Aciki Harda masu bata Shawaran Takaishi
ƙara Kotu, yaƙe kawai Farida Keyi amma Bata jin Daɗin yadda Billy ta Fallasasu A
duniya ba Ko ba komai Tana Son Tahir Kuma Har gobe yana Matsayin Uban 'ya'yanta ne,
Kuma Mijinta.
Ɓangaren su Umma kuwa basu san Abunda ke Faruwa ba Don Daga Faridan Har Tahir ɗin
ba Wanda basa Waya Dashi amma ba Wanda yace ga wani Abu, Ita Farida Tsoron Su Umma
ne Domin Tasan Ranta sai ya ɓaci Balle Abba dayayi Fushi da Ita don Musamman ya
Kirata ya Zageta Tas, Balle kuma tace Ta Baro Gidan Tahir ai kila sai Abba ya Kusa
Tsine mata, Shiko Tahir Faridan ne Kwata Kwata bata gabanshi Baya Fatan ya ƙara
Buɗan baki ya Faɗi Wani Abu Daya Danganceta ya Ratayeta Gefe ne Domin Ahalin Da
yake Ciki yafin Jin Tsananta da Haushinta Fiye da Kanshi Shiyasa Ko Umma ta
tambayeshi Suna Zaune lafiya yake cema ta ba wata matsala Domin Kaucema Duk Abunda
zai Dawo Da Farida Yamafi Jin Daɗi da bata nan Ko ba komai bayasan Abunda zai Dinga
Takura Mufeeda.
Sai Ranar Data Kwana A cikin Gidan Kana Suka Ci karo da Abban su Walida, Ranar
bai Fita ba Kwata kwata yana gida, Lokacin Daya ga Farida yayi Mamaki sosai nan
yake Tambayanta Yaushe tazo..? Sai tace mai ta kwana biyu ma..Ido ya Zaro yana
kallon Billy Wacce Tayi Fiƙi Fiƙi da Ido Zuciyarta na Tsananta Bugu Wani kallo yabi
Farida Dashi bai dai yi magana ba Amma Acikin Ranshi yana Tunanin Wani Shirme kenan
Mace da Gidan Mijinta Kuma Tazo Gidanshi Ta tare, Ina bazai Ɗauki Wannan Iskancin
ba.
Bai mata magana ba sai da Suka Shiga Cikin Bedroom Ɗinsu kana ya Tsareta da Ido
yana Faɗin "Da wani Dalili Farida Tazo nan gidan Harta kwana uku ban sani ba..? Ke
dama wani Manufa Matar Da take da Mijinta..?"
Ya faɗa yana Hararanta Sanin Halinta na Shanshanci Shi bai Sake mata ba Shiyasa Duk
yadda Billy taso tayi Iskanci bata samu Dama ba, Cikin Rawan Murya tace
"Dama..Dama..Umh..." Tsawa Ya Daka mata yana Faɗin "Dama Menene..? Baki zaki Buɗe
kiman magana Yadda zan Fahimceki kinsan bana son Raini ko....?"
Kai ta gyaɗa kafin tace "Matsala suka samu da Abban su Basma..." Kallonta yayi A
ɗage kafin yace "Matsala..?" Ya maimata da Sigan Tambaya kai Ta gyaɗa mai alamar
Hakane, Cikin Dariyan karki Raina min Wayau yace "Kuma Shikenan Don Sun samu Saɓani
ita da Tahir sai kuma akace tazo gidan Aurenki ta tare ko..? Ke gaki Uwarta ko kuma
Mai bata Shawaran karta koma gidan Mijinta ta cigaba da zama agidan naki Mijin..?"
Ya faɗa yana kallonta Cikin ɓacin Rai..
Jikin Billy na Rawa Ta Riƙo Hannunshi Tana Faɗin "Don Allah ka Tsaya ka Saurare
Abban Walida Wallahi Tahir ya chanchanci Farida Data barshi Amanarta fa yaci Shida
yarinyar Datake mata Renon Naila.." Ta faɗa Lokaci Ɗaya Tana Zaunar Dashi gefe Ɗaya
Kafin ta Fara Rattaba mai yadda Akayi Billy Saboda Sharri Harda ƙari kamar Agabanta
Akayi
Haba Aliyu ya riƙe Kafin yace "Ke Bilkisu bana son Ƙarya fa..? Shi Tahir ɗin..?
Haba Don Allah ya za'ayi mutum mai Daraja ya aikata Haka, Tahir fa Yana da Kima
Sosai a idanuwan Waɗanda Suka sansa.." Ya faɗa yana Tantama Rantsuwa Billy Ta fara
Jera mai, Domin ya yarda Da Ita, Bai yarda ba Miƙewa yayi yana Faɗin muje naga
Faridan, Jiki na Rawa Tamai Jagora Zuwa Ɗakin data Sauke Farida, Cikin Tsare gida
yake Tambayanta gaskiyan lamarin Cikin Kuka Farida ke labarta mai Hadda Hukuncin da
Iyayenshi Da nata Suka bashi goyon Baya.
Tana Faɗa tana Share Ƙwallah, Jinjina kai Aliyu yayi kafin yace "Lallai ba Shakka
In ko Hakane Tahir bai kyautama kanshi ba ya Cuci kanshi kuma ya Tozarta iyayensa
Da kuma Zuri'arsa..Ya bani kunya Sosai, kuma sai na kirashi na mai magana.." Da
Sauri Farida tace "Don Allah Abban Walida ka ƙyaleshi ko kayi mai magana bazai
Saurareka ba baya ganin Abunda ya Aikata amatsayin laifi Tunda Haryana Ikirarin
data bar gidan Gwara ni na Fita na bar mai gida.."
Miƙewa Aliyu yayi Daga kan Sofa yana Faɗin "maganar banza kenan Har office ɗinshi
Zani Wallahi..Sai na gaya mai gaskiya sai dai ko karyaji Daɗi.." Daga Haka ya Fice
Daga Ɗakin Cike da Mamakin Tahir ɗin Duk da ba wani Kusanci Suke da Juna sosai ba,
amma Suna Taɓa Juna Lokaci bayan Lokaci Saboda ƙawancen Matansu Da ba yanzu yake
ba, Yana Fita Farida Ta Miƙe zatama Billy magana tayi Saurin Dakatar da Ita tana
Faɗin "Kinga Farida Bar maganar nan sai gobe..Yanzu lokacin Abban Walida ne kada mu
Shiga Hakkinshi Nasan, Halin yan kaya na.." Daga Haka ta Fice Ta bar Farida Riƙe da
baki Tana Binta da Kallo.
****
Washegari kuwa Da Misalin Ƙarfe 3:00pm na Rana Aliyu ya ƙwanƙwasa Ƙofar Office d'in
Tahir inda ya bashi Umarnin Shigowa Suna Tare da Ishaq lokacin Suna Wani Lissafi
ganin Aliyun sai da yayi mgana Cikin Fara'a Ya Tarbeshi yamai iso Zuwa Kujeran Dake
office d'in Ruwa ya kawo mai Ya Zuba mai ya Mika mai ya karɓa yana Mai Godiya sai
da yasha Ruwan ne ya Miƙawa Ishaq hannu suka gaisa Cikin Sakin Fuska ya kalli Tahir
yana Faɗin "Alhaji Tahir Wajen ka nazo, Wata maganace mai Muhimmanci ke Tafe
dani.."
Shiru Tahir yayi kafin yace "Allah Sarki ba komai ina Jinka.." Ya faɗa Cike da
Mamaki Lokaci Ɗaya yana zama agefensa, Kallonsa Aliyu yayi kafin ya maida kallonshi
kan Ishaq, Tun kafin yayi magana Tahir yace "Karka damu ka faɗi maganar Ishaq
Tamkar Ɗan'uwa yake a gareni.." Zakuɗa kafaɗa Aliyu yayi kafin yace "Kana da
Labarin Matarka Farida na gidana Tun Ranar data bar gidanka..?"
Tahir ya Ɗago ya kalli Ishaq shima ya kalleshi kafin Duka su maida Hankalinsu kan
Aliyu Lokaci Ɗaya Tahir yace "Ah...Ina zan Sani kuwa Alhaji Aliyu.." Ya faɗa Cikin
Halin Rashin Damuwa, Gyara zama yayi kafin yace "Toh Tana gidana nima bansani ba
sai jiya na sani Shine na Turke Ita Bilkisun Shine Take Sanar dani Wani Labari mara
Daɗin Ji ban yarda ba sai da Na Kira ita Faridan Na ƙarajin Ta bakinta Wai Alhaji
Da gaske ne Maganar da Suka Faɗa min..?"
Miƙewa Tahir yayi yana Kallon Aliyu kafin yace "Wata magana kenan..?" Ya faɗa
Jijiyoyin kansa Sun Fara Tashi Saboda Ɓacin Rai Cikin Jimami Aliyu yace "Na kama
yarinyar Da kuka Ɗauko Daga Garinku tana muku Rainon Naila Ciki.." Ya faɗa yana
Sakarma Tahir ido, Runtse ido Tahir yayi Zuciyarsa na Tafasa kamar tayi Bindiga
Haka Shima Ishaq yana Tsinema Farida ne a Cikin Ranshi, shi Wallahi ko Zahra bai
yarda ya bata wannan Labarin ba balle ke ace Mijinki amma baki da Buri sai na Tona
mai Asiri ki tozartashi.
Taku Tahir yayi Zuwa bakin Window Office ɗinshi ya yaye labulen Wajen Cikin Juya
baya yace "Eh Da gaske ne Aliyu..Nama Mufeeda Ciki, amma Duka Abunda ya Faru ba
laifina bane Laifin Farida ne Ita ce Sanadiyar Jefani Cikin Halaka amma Wallahi
bayan Matata Farida ban taɓa Keta Gonar da ba Tawa ba sai akan Mufeeda Wacce
Ƙaddara ta Hau kanmu.." Ya ƙarashe Faɗa Cikin Muryan Kuka, Miƙewa Aliyu yayi yana
Faɗin "Ashsha Kaji ko..? Abu baiyi Daɗi ba.."
Tahir bai bashi Zarafin ƙara magana ba, ya Shiga bashi Labarin irin zaman
Wulaƙancin Dayayi da Farida da yadda ta banzatar da Rayuwarsa da Ƙoƙarinsa na ƙara
Aure da yadda Goggo Take Dakatar dashi har Zuwa Faruwan komai Ya ƙarashe yana Faɗin
"Wallahi Tallahi..Farida Ta Cutar dani Cutar da Allah ne kaɗai zai sakamin, Sai
Farida tayi Wata Huɗu bata kalleni A shimfiɗa ba, Ku gayamin Ni Dutse ne ko Gunki
da bazan Buƙaci mace ba..?" Ya faɗa lokaci Ɗaya yana Juyo da Fuskarsa Wacce Hawaye
suka Wanke mishi ita.
Daga Ishaq Har Aliyu Jikinsu yayi Sanyi Sosai Aliyu ne ya ƙarasa Kusa Dashi ya
Dafa Kafaɗarshi yana Faɗin "Cool Down Ka daina Kuka, Haƙiƙa Wannan Abun da ya faru
ƙaddara ne ko Kuma nace Darasi ne ga Farida da Goggo, Amma fa maganar gaskiya kana
da babban Laifi Tahir na yarda kabar Farida ta Rainaka take yarda taga Dama bayan
Kai kake Aurenta aiko Min gatan da iyayenta Suka bata Tunda tabar Gabansu Ta Dawo
ƙarƙashin Ikonka ya kamata ka Nuna mata ƙwanjinka na Mulkinka Amatsayinka na Namiji
mai Cikakken Iko Agidanshi.. Maganar gaskiya kayi Kuskure.." Ya faɗa yana Murza
Kafaɗarsa.
Numfashi Tahir ya Sauke kafin yace "Tabbas maganarka Hakane... Haƙurina da girman
Iyayenta Danake gani Da kuma Nasihan Goggo Akaina da Kuma 'ya'yan Dake Tsakanina da
Farida yasanya Bana iya Mata Wani abu, In tayi ba Daidai ba Shine Kuskure na barta
ta saba da Komai tayi Daidai ne Tabbas nima ina da Laifi ba komai Ake ma Haƙuri ba
Gashi Haƙurina yajamin naje na Afkama Marainiyar Allah Daga Ƙarshe na zama Abun
YaɗaWar Farida Kamar bamu Haɗa komai da Ita ba, ba komai...Haka Allah ya Tsara
min.." Ya faɗa yana Share Hanci kamar Wani yaro.
Kafaɗarsa Aliyu ya Daka kafin yace "Kazama namiji Abokina ka ganni nan bana ma
Bilkisu da Wasa Tunda na Lura tana da Rawar kai Ubanta Nakeci tasan Halina ko yanzu
ɗin ma ina komawa zan Koro Faridan Dole ta Dawo Tunda bata da Wajen Zuwa..."
Da Sauri Tahir yace "No..no plz ka ƙyaleta Ka barta ta Zauna Da kanta zata Dawo ba
sai kamata magana ba ai zataga Abunda saɓanin Shi Suke gaya mata zata ma kanta Faɗa
Tun kafin Wani ya mata.." Ishaq yace "Shawara mai kyau Tahir..."
Aliyu ya Saki Hannu yana Faɗin "While Tunda kace Haka zan saka musu ido.. Amma True
Tak, Yarinyar nan ta Haihu ka Aureta Wallahi Sweet Sixtyn suna da Daɗin Sha'ani,
Tuni Farida zata Rena kanta Ta Dawo Tana begenka Lokacin Da ka mata Nisa.." Dariya
Ishaq ya saka kafin yace "Shawara mai kyau..Dama Shi ya Chanchanta yayi Wuf da
Ita.." Hararanshi Tahir yayi Bai yi Magana ba, Shima Aliyu Dariya yake kafin su
Cigaba da Tattauna maganar Tare Suka Fito Sai da Sukayi sallar La'asar Cikin Jam'i
kana suka Rako Aliyu ya Hau Motarsa Zuwa gida, su kuma suka koma Office d'in Tahir
Ishaq bai Dawo da Maganar ba ganin Tahir ya basar da Zancen ya Ɗauko Lissafinsu
suka cigaba dayi amma Cikin Ran Tahir Tsanar Farida ce ke ƙara Ninkuwa in ya Tuna
Tana chan tana Yawo Dashi Acikin Duniya kamar babu Igiyan Aurenshi Akanta.
******
Hatta da Islamiyya ta koma Abunta kamar ba Ita ba, sai dai Tayi Kiɓa Sosai, Ta
ƙara Fari ta Cika ta Ko'ina Saboda tana samun Abunda Take so Abincinta Dama Shine
Faten Wake, sai ƙosai da Koko sai kayan kwaɗayi Irinsu Goriba, yalo Sai Ice cream
Wanda In Mufeeda bata Sha ba kamar Cikin zai ɓare, Shiyasa Tahir kullum zai Dawo
sai ya Shigo mata Dashi, Ba laifi Iya na Kula da Ita sosai su Basma ba'a barsu
Abaya ba Lokaci kaɗan Mufeedan Ta Saki Ranta sai dai Tunanin Innarta Dayaki barin
Ranta.
Ɓangaren Su Goggo Abu kuwa ba Wani Cigaba, Tahir Sau Ɗaya ya Kira Baba Hakimi Awaya
Tunda yaji ya fara mai maganan Goggo Abu ya Datse Kiran, Tun daga Ranar ko ya
Kirashi baya Ɗauka Dole ya Haƙura sai dai yana Kiran Goggo Akai akai Yana ƙara bata
Haƙuri amma ya Ɓoye mata Shima Saboda Ita Baba Hakimi ya Daina ɗaga Wayarsa sai dai
ya Dinga Nuna mata ta kwantar da Hankali komai xai Daidaita.
*******
Yana Toilet yana Wanka, Akayi ta Kiran Wayarsa bai ji ba sai da ya gama Wanka ya
ɗauro Alwala ya Fito Ɗaure da Towel A ƙungunsa Ƙaramin na Saman kansa yana Tsane
Ruwan Jikinsa, Yaji Kiran Wayarsa Cikin Sassarfa ya isa Kusa da Wayar, Abunda ya
bashi tsoro ganin Kiran Baba Hakimi, Da Asuban Fari Domin Lokacin Wajen ƙarfe
4:43am ne.
Cikin Firgici Da Tsoro ya ɗaga Kiran yana Faɗin "Salamu Alaikum Baba..?" Ya faɗa
Cikin Rawan Murya banji me akace ba Sai dai naji Tahir ya saki Salati yana Faɗin
"Innalillahi Wa'inna Alaihirraju'un..Allah ya Jiƙanta da Rahma Allah yasa ta
Huta..."
Ya faɗa kafin ya Ɗauke Wayar A kunnensa Cikin Mutuwar Jiki ya Faɗa gefen gado yana
Dafe kanshi Ko'ina na Jikinsa na Rawa, lokaci ɗaya Yaji Hawaye Sun Cika mai ido Har
Sun Fara gangarowa.
*Shakira*
*Aisha Alto*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
........Ya Daɗe Zaune a gefen Gado yana Dafe da kanshi yana Jimamin Abunda Baba
Hakimi ya Sanar Dashi, Tausayin Mufeeda na Ƙara Cika masa Zuciya. Rashin Mahaifiya
Akwai Ciwo balle Ita Daba Uwa ba uba..
Ya daɗe Zaune Baisan Iya Adadin Lokacin Daya Ɗiba yana Tunani da Kuma Tausayin
Mufeeda ba, Kiran Sallah ya ƙara Jiyowa Daga Masallatan Dake Kusa Dasu Zabura yayi
ya Miƙe Lokaci Ɗaya yana Duba agogon Wayarsa yaga 5:10am Da Sauri Ya Nufi Wardrope
ɗinshi ya Buɗe ya Ɗauko Wata Jallabiya mai Ruwan Toka ya Zura Hula ya sanya kafin
ya Ɗauki Carbin sa ya Fice Daga Ɗakin.
Ƙasa ya Sauko Zuwa Ɗakin Bassam Shi ya kuma Tashi Su Basma, Iya kuma Koda ya Leƙa
Ɗakinta Ta tashi sai yace Ta tashi Mufeeda Lokacin Sallah yayi, Daga nan Suka Wuce
Masallaci Shida Bassam sai Wajen Bakwai Saura Suka Dawo Suna Shigowa Falon Suka
Iske Basma Tsaye da Uniform A jikinta Cikin Girmamawa Ta Duƙa ta gaishe da Tahir,
Cikin kallonta yake amsawa yana Faɗin "Ku Saka kayan gida ne Basma Gaba ɗayanmu yau
Ɗanbatta zamu.." Tare da Bassam Suka Kalleshi Cikin Murna Suka ce "Da gaske
Daddy..?" Kai ya gyaɗa musu alaman Hakane Tsalle Suka Farayi alamar Murna Cikin
Dakewa yace "Ku ɗiba kayanku koda Kala Uku uku ne sai bayan Kwana Uku zaku Dawo.."
Jin Haka yasa Suka Zura da Gudu Zuwa Ɗakunansu da Kallo ya bisu Acikin Ranshi yana
Faɗin Kurucci Dangin Hauka.
Yana Shirin Haurawa Sama Iya ta Fito Daga Kichen ganinshi yasa Ta saki Fuska Tana
Faɗin "Ah...Alhaji Barka da Safiya.." Cikin Sanyi ya waigo yana Faɗin "Ina kwana
Iya..?" Ta amsa da lafiya lau bai bata Zarafin magana ba yace "Ahm Iya Ki Shirya
kayanki ki kuma Saka Mufeeda Ta Shirya Kayanta Ɗanbatta zamu yanzu da Safen nan."
Iya ta Ji Zuciyarta ta Tsinke da Sauri Tace "Ɗanbatta kuma Alhaji..? Allah sa
lafiya..?"
Shiru yayi kafin yace A hankali.. "Mahaifiyar Mufeeda ce Allah yama Rasuwa Jiya da
Daddare yanzu Baba Hakimi ya Kirani yake Faɗa min.." Dafe Kirki Iya Tayi kafin tace
"Innalillahi Wa'inna Alaihirraju'un..." Ciwo Tayi Alhaji..?"
Kai ya gyaɗa mata kafin yace "Eh har ta kwanta Asibiti ma, Ki Taimakama Mufeeda Don
Allah Iya, Kuma karki Sanar da Ita Domin batasan Halin Da'ake Ciki ba.."Jinjina kai
Iya Tayi Tana Faɗin "Allah Sarki Haƙiƙa Mufeeda Tayi Rashi babba..Allah Ya Jiƙan
Inna Fulera, Insha Allahu Alhaji yanzu zamu Shirya.." Ta faɗa Cike da Tausayawa.
Gyaɗa mai kai yayi kafin ya Haura sama Ita kuma ta Koma Kichen Ta Cigaba da Soya
Dankali, cikin Jimami da Tausayin Mufeeda sai da Ta kammalah Duka Abun karyawan Ta
kwaso Zuwa Dininng kana Ta Shiga Ɗakin Mufeeda Ta Isketa Tayi Wanka Har ta shirya
Cikin Uniform ɗinta Naila ma Ta mata Wanka Ta Shiryata Cikin Riga da Wando, Tana
gefen Gadon Tana Riƙe da Hannun Naila wacce Ke Tata tan Tafiya, cike da Tausayin
Mufeeda Iya ta Shigo Ɗakin Tana Faɗin "Mufeeda Ki Cire kayan Makarantar ki saka na
gida kuma ki Haɗa kayanki Cikin Akwati Naki dana Naila yanzu Alhaji ke gayamin
Ɗanbatta zamu Tafi Dukkanmu sai mun kwana Biyu A chan.."
Da Sauri Mufeeda Ta Ɗago Tana kallon Iya Cikin Fitar Magana tace "Ɗanbatta kuma
iiya..? Na Shiga Uku ko Gida Daddy zai maidani..?" Ta faɗa Idanuwanta na Cikowa da
Ƙwallah Saurin girgiza kai Iya Tayi Tana Faɗin "Ko Ɗaya inaga dai Hutu Alhaji ya
samu yakeso muje chan Muyi Hutun.." Ta faɗa Tana Ƙara Jin Tausayin Mufeedan, jin
Haka ya saka Mufeeda Ta Washe baki Tana Faɗin "Da gaske Iya..? Yau zan kwana A
ƙirjin Innata.." Ta faɗa Cikin Farin ciki Lokaci Ɗaya Tana Ijiye Naila kan gado ta
isa Wajen Akwatinta ta Ɗauko, Iya Fita tayi Tana Sharan Ƙwallar Tausayin Mufeeda.
Shiko Tahir kafin ya Shirya sai da ya Kira Ishaq ya Sanar Dashi Cikin Tausayawa
Ishaq yace Ya Jirashi gashinan Zuwa Su Tafi Tare Haka ko Akayi, ƙarfe 8am da 'yan
Mintina Gaba daya Sun gama Shirinsu Sun karya Tahir ne ma bai Karya ba, Lokacin da
Suka Fito sai ga Ishaq ya ƙaraso, musabaha Sukayi da Tahir Su Basma kuma Suka
Ranƙwafa Suna gaisheshi ya amsa yana Shafa kansu, Nan da nan Suka Shiga Mota bayan
Garzali ya Zuba kayansu Cikin Booth d'in Motar, Harda Tahir Shima da Jakar kayansa,
Cikin gida kuwa Iya sai da ta kashe komai na Wuta Kana Suka Fito, Motar Garzali Su
Iya da Basma da Bassam da Mufeeda Suka Shiga Tahir wanda ya ke Riƙe da Naila, da
ishaq suka Shiga Motar Ishaq ɗin, Tara da Wani Abu na Safe Suka Ɗauki Hanya bayan
Tahir ya Kira Baba Hakimi yace Atsahirta da Jana'izar Inna Fuleran Har su Iso ko
Mufeeda ta samu ganin gawar Mahaifiyarta Suna Tafe Suna Janjanta Abun Shida Ishaq,
Lokaci Ɗaya kuma suna Gudu ba Sosai ba.
******
Ƙarfe 11 da 'yan Mintuna Motocinsu Suka Yada zango A ƙofar Gidan mai girma Hakimin
Ɗanbatta Inda Suka Tarar da Al'umma Tsaye, wasu kuma Suna Zaune da alaman dai
Isohuwarsu Ake jira, Mufeeda Kuwa Tunda Suka Shigo garin Ɗanbatta gabanta ke Faɗuwa
Zuciyarta bata Tsinke ba Sai da Suka Tsaya A ƙofar Gidan Duk da Ƙofar Gidan Hakimi
ba'a Rabashi da Jama'a amma na Yau Daban ne, Sukansu su Basma Sunyi Wani Iri balle
da Suka Firfito Daga mota Sunji Ana gaisawa da Tahir Ana mai gaisuwa, Umarni ya
basu kan Su Shiga Cikin Gida, Shi kuma Idanuwansa na kan Mufeeda bayan ya Miƙawa
Iya Naila.
A cikin gidan ma Cike yake da Mata Tunda nan Aka kawo gawar Inna Fuleran Bayan ta
cika Akayi mata Wanka da Suturu Tunda Suka Shiga gidan Mufeeda ke Jan Ƙafa, kamar
Mara Lafiya, barinma yadda jama"a ke Binta da kallon Tausayi Basu Dai Tsaya ba sai
da Suka Shiga Falon Goggo Abu Inda Suka Iske Goggo Abu zaune da Hijabi Da Carbi
Ahannunta gefenta kuma Innaro ce sai Ashe da Maman Lantana Dake gafe Daga
Tsakiyarsu kuma gawar Inna Fulera ce Lulluɓe Cikin Likkafani Tunda Suka Shigo Ɗakin
Maman Lantana Ta ɗago Tana Kallon Mufeeda Idanuwanta na Zubar da Ƙwallah Tun daga
Lokacin Jikin Mufeeda ya fara Rawa Saboda yadda gabanta ya fara Tsinkewa Lokaci
Ɗaya.
Basma ganin gawa ne yasa Ta koma bayan iya Tana Rawar Jiki Ita ko Mufeeda Maman
Lantana ta Nufa Tana Faɗin"Maman Lantana lafiya naga kina kuka..? Waye nan kwance
ya Rasu..? Ina Innata naga banganta bane.." Ta ƙarashe Faɗa Cikin Fitan Hayyaci
Hannunta Mama Lantana Ta Rik'e kafin Tajata har gaban gawan Inna Fulera ta saka
Hannu ta yaye Farin likafanin Da'aka Lulluɓeta Dashi Dayake Tana Cikin Makara ne,
Fuskar Inna Fulera Ta bayyana Kwance Bata Numfashi.
Daskarewa Mufeeda Tayi Tana bin gawar da kallo Cikin Rashin Hayyaci Kafin Ta Sulale
ƙasa Ta Duƙe Gaban Gawar bakinta na Rawa Muryanta na Tsinkewa Take Faɗin "Inn...
Innata..Ta..na barci ne ko..?" Ta faɗa Lokaci Ɗaya Ta Ɗago kai Suka Haɗa ido da
Maman Lantana Hawaye Sun Fara Wanke mata Fuska Jikinta na Rawa ganin Tana Taɓa Inna
Fulera ba motsi gashi Duk An Nannaɗeta Ciki Likafani Zuciyarta Ta Tabbatar mata da
Sai Mutum ya Mutu Za'ayi mai Haka Kenan Innarta Ta Rasu..? Zuciyarta ce ta karye Ta
Faɗa jikin Gawan Tana Faɗin "Innata ki Tashi...Nasan kina Jina..? Nice 'Yarki
Mufeeda ki Tashi ki ganni nasan Wasa Kike man baki Mutu ba.." Ta Faɗa Tana Kuka
Wurjajan Su Goggo Abu Saboda Tausayi Sai Sharan Ƙwallah Suke na Tausayin Mufeeda
Maman Lantana ne ta ƙaraso kusa Da Ita ta Riƙota Tana Kuka Take Faɗin "Bar Kuka
Saman gawa Mufeeda Fulera ta tafi..Sai dai muyi mata Fatan Dacewa Ta Cika Da Kalmar
Sunanki Abakinta bayan Ta Jaddada albarka agareki.." Ƙyam Mufeeda Ta Tsaya Da
Kukanta Tana kallon Maman Lantana Cikin Fitan Hayyaci Take Faɗin "Da gaske ne dama
Inna ba barci Take ba..? Innata fa Ta Rasu kika ce..?" Na Shiga uku ni Mufeeda ina
zan Saka kaina..?" Ta faɗa Tana Sakin Wani Marayan Kuka, kamar zata Shiɗe Lokaci
Ɗaya Tana ƙara Sulalewa kan gawar Iya da Basma na waje Ɗaya Suna Sharan Ƙwallah
Hatta Naila Datake yarinya Ganin Mufeeda na Kuka Itama sai Ta Fashe da Kuka ganin
Yadda Mufeeda ke ƙanƙame gawar Inna Fulera ne Tana Kuka Tana Faɗin Inna Ki Tashi ya
sanya Innaro Tashi Ta Riƙota da Ƙarfi Cike da Tausayi amma sai Mufeeda Ta Turje
domin Wani ƙarfi ne yazo mata ta ƙwace kanta ta koma ta ƙara kwanciya kan gawar
Inna Fulera Tana Kuka Daidai lokaci kuma Su Tahir Suka Shigo Dashi da Ishaq da Wasu
mutane su Shida Sunzo Daukan Gawar, Tun Shigowar su Mufeeda Cikin gidan Tahir ke
Cikin Zullumi yanzu ma yana Shigowa Idanuwanshi na kanta Gaba ɗaya Jikinshi na ƙara
Sanyi Kusa da Ita Suka Isa kafin ya Sanya Hannu ya Dafa kafaɗarta yana Faɗin
"Mufeeda..." Ya faɗa Cike da Rauni.
Jin Muryansa yasa ta Ɗago da Sauri Ganinshi yasa Kawai Tayo Rimi ta afka mai Har
sai da ya zauna kan Cafet ɗin bayan yayi Saurin Riƙeta Cikin Kuka Take Faɗin
"Kagani Wai Daga Innata na barci suna cewa ta mutu, Zata Tashi ko Daddy kace mata
Ta tashi gani nazo.." Ta faɗa Tana Zubar Hawaye Zuru yayi mata da Ido kamar ya
Fashe mata da Kuka Cikin Fitar magana yace "Kinga Kwantar Da Hankalinki, kinji
ko..? Kin Taɓa ganin Wanda ya Mutu ya Dawo..?" Girgiza kai tayi kafin ya cigaba da
Faɗin "Toh ki saka Aranki Inna ta tafi bazata Taɓa Dawowa ba...Yanzu Addu'arki
kaɗai Take buƙata ba Kukanki ba.." Tsuru tamai da Ido Hawaye na Zuba mata Shar
kafin tace "Bani da Kowa...Inna itace gata na...Ya zanyi na Shiga Uku.." Baki ya
Rufe mata yana Faɗin "A'ah kina damu...Mune gatanki Mufeeda nayi ma Inna Alƙawarin
zan zamo garkuwarki Har Ƙarshen Rayuwarki ki daina Kuka Tashi ki bari Aɗauki
gawarta Amata Sallah zamu kaita gidanta na gaskiya.." Ya faɗa yana Ɗagota Tsaye
kafin yama Su Ishaq alama da Ido kan Su Ɗaga gawan Gaba ɗaya Falon ko Mamakin yadda
Tahir ya Iya Shawo kan Mufeeda Akeyi, wacce Tun Taga Da Gaske za"a Fita da Gawan
Inna Fulera sai ta ƙara Tuburewa Tana Kuka Tana Ƙoƙarin Ƙwace kanta Tana Faɗin
"Wayyo ku Dawo min da Innata Ku Dawo min da Ita.." Take Faɗa Tana kuka Tana miƙa
Hannu Har Aka Fice da Ita Agaban Idanuwanta Luu kawai Tayi Ajikin Tahir alamun Ta
Sume, Fuskarta yake Shafawa yana Kiran Sunanta, Innaro da Ashe Suka Taso da Sauri
Suka Riƙota Suka Shiga da Ita Uwar Ɗakin Goggo Abu Mama lantana kuma Ta bisu da
Ruwa Shi kuma Tahir Da Sauri ya Fice yana Ji kamar Shima ya share Ƙwallar, Da
kallon Tausayi Goggo Abu Ta Bishi Itama Ƙwallar Take Sharewa Domin Har yanzu bata
Ishi Baba Hakimi kallo ba.
Har Aka kai Inna Fulera gidanta na Gaskiya Mufeeda bata ƙara magana ba Bayan Ta
Farfaɗo Tana dai Zaune Zuru Hawaye na Zubar mata Kowa yazo ita yake Tausayi ba Uwa
ba Uwa Gashi ba wani ƙwaƙƙwaran Dangi, Mutane sai magana Suke Wasu na Faɗin Ai
Taimakonta Ma gidan su Hakimi, Sune gatanta, gida ya cika da 'yan Zaman Makoki
Hakama Ƙofar Gida Cike da Mutane Ciki Harda Su Tahir da Ishaq Harda Garzali Direba
Wanda Tahir yace ya Koma gida yace ya barshi ya samu Jana'iza Mutane da Kuma
alhinin Mutuwa ya saka ba Wanda Ya Lura ba Farida balle Har Ya Tambayeta Goggo Abu
ne ke Damuwa Da Ita, Toh Itama Tana Ta kanta ne Ba wanda Ya Tuna Da Ita sai
Washegari Da Umma Suka zo gaisuwa Ita da Abba,Tun Ajiya Ishaq ya koma Shida Garzali
inda Tahir yace Ranar Uku ya Dawo ya Ɗaukesu.
Tahir ya Shiga Cikin Gida Da Rana gaida Umma Naila na Hannunsa bayan Tagama ma
Tahir gaisuwa Shiko Rabin Hankalinsa naga Mufeeda Wadda Cikin Kwana Ɗaya Ta Fita
Hayyacinta Kukan Zucci Take Wanda Sai dai Aga Hawaye na Zubo mata Ta fita
Kamanninta Fuskarta Ta Kumbura Idanuwanta Sunyi Jawur Tana Kusa Da Goggo Zaune ta
Tsurama Cafet Ɗinta ido Yana Nazarinta ne Umma Tace "Wai ni kam Ina Farida ne Tunda
na Shigo ban Ganta bane ko Tana Shashen Innaro ne..?"
Gaba ɗaya wajen Aka Zuba ma Tahir Ido, dama Cikin Uwar Ɗakin Goggo Abu ne, Daga
Umma sai Mufeeda sai Goggo Abu Innaro ma Tana Falo Ita Da Ashe da Sauran Jama'a
Cikin Dakewa Da Rashin Damuwa Tahir yace "A'ah Umma bata zo ba.." Cikin mamaki Take
Faɗin "Bangane bata zo ba? Tahir Mutuwa fa Akayi Shine ka ƙyaleta Taƙi Zuwa..?"
Murmushi yayi kafin Yace "Nifa Umma Tun Washegarin Tafiyarku Farida ta saka ƙafa Ta
bar gidan Batare Dana san Inda Taje ba.." Salati Umma ta Saki Kafin Tace "Na shiga
uku ni Aliya Farida Zata Kasheni Lokacina bai ƙare ba Haba Tahir Shine Duk Tsawon
Wannan Lokacin Baka Taɓa Sanar damu ba..?" Kansa ya Sunkuyar batare Daya ce komai
ba Mamakin Goggo Abu yake Yadda Ko ƙanzil batace ba Lalle Goggo Taga Rayuwa.
Cikin Ɓacin Rai Umma Ta Ciro Waya Ta Dokawa Farida Kira, lokacin da Kiran Umma ya
Shigo Tana Zaune Afalon Na Billy Tana kallon Ikon Allah, domin Abban Su Walida ne
yayi Tafiya yau zai Dawo Shine Billy Ta kasa Sukuni da Zama Tsakanin Kicthen da
Falon ƙayataccen Girki Take mai Tana Rawan Jiki, Farida Abun na bata mamaki In Taga
Abunda Billy ke Aikatawa kamar ba da ita Cikin masu Zugata kan ba'a Sakarma namiji
Fuska Balle kai mai Rawan Jiki Itako Tunda Tazo Gidan Matuƙar Taga Billy Afalo Toh
Abban Walida ya Fita ne In ko yana nan bata da Lokacin kowa bayan An Chaɓa Ado An
Shiga Kichen Anyi Girki Ta Tuna Sanda Billy ke Bata Shawaran Ta Ɗauko mai aiki Kada
ta zama baiwa mai abinci, Abun bai ƙara Ɗaure mata kai ba, sai da taga yadda Billy
ke Rawan Jiki ko Muryan Abban Walida Taji, kenan Itace Suka Maida Sakarya da Suke
Sanar Da Ita Tsakaninta da Namiji bawani Ragowa in Tanaso ta ƙwaci 'Yancinta..?
Tana Cikin Wannan Tunanin Wayarta Ta Shiga Tsuwa, ganin Sunan Umma sai da gabanta
ya amsa Tana Ɗagawa Umma tace "Kinci Ubanki Farida.." Cikin Mamaki Farida Tace "Kai
Umma me nayi kuma..?" Umma tace "Ubanki kikayi Nace Ubanki kikayi..Ashe Farida Baki
da Mutumci bansani ba? Kina gidan Uban waye Bayan kinbar gidan Mijinki...?" Tura
Baki Farida Tayi kafin Tace "Umma ina gidan Billy...."
"Billyn ubanki Sakarya mara Tunani Wato ita Tana Gidan Aurenta Ke kuma Ta barki ki
Zauna Tunda baki da mafaɗi, Toh maza ki Haɗo Yanaki yanaki Kizo Ɗanbatta yau ɗin
nan muna Jiranki Nida Abbanki munzo Gaisuwar Rasuwar Mahafiyar Mufeeda.." Daga Haka
Umma Ta Katse Kiran.
Sororo Farida Tayi Ranta na ƙuna da Sunan Mufeedan Da'a Aka Ambata Amma Haka Ta
tashi ko kallon Ɓarayin da Billy Take bata yi ba Wacce ke Jera Kuloli bisa Dinning
Ɗakin Da'a Aka Sauketa ta Shiga Tana Hawaye Ta Haɗa kayanta Tsab Ta Ɗauko Mayafinta
da Akwatinta ta Fito, A falo Suka ci karo da Billy Cikin mamaki tace "Ah Farida Ina
Zuwa naganki da Akwati Haka..?"
Kai Tsaye Farida tace "Ɗanbatta zani..." Sheƙeƙe Billy ke Binta da kallo kafin tace
"Wai koma ma Tahir ɗin zakiyi Don Rashin Zuciya..?" Cike da Haushinta Farida Tace
"Eh zan koma ma Mijina Tunda na lura masu bani Shawaran yadda zan Tafi da gida Su
basu amfani da Shawaran ko Kaɗan.." Sororo Billy Tayi Domin Tagane magana Farida ta
yaɓa Mata, Ɗaure Fuska Tayi kafin tace "Au Haka zaki ce...? Ke kika sani Ai 'yanci
Ake Neman ƙwatar miki Mutumin daya Tozartaki yama 'Yar aikinki ciki ai magana ta
ƙare.."
Farida Takama Hanyar Fita Take bama Billy Amsa Cikin Dakewa tace "Eh 'Yanci Abarni
na ƙwatarma kaina kamar yadda Kuma naga kuna Ƙwatarma kanku, kuma maganar yama 'Yar
Aikina ciki Gwarashi nashi ya bayyana Mijin Wata Fa.? Uban wa yasan Wani Ta'asan
yake Aikatawa Adai yi Sha'ani.." Baki Billy Ta kama kafin tace "Kambu...! Amma
kafin ta Sake Wata Magana Farida Ta Fice da Kallon Mamaki Ta Bita Kafin Ta taɓe
baki tace A fili.. "banza.Allah sa Kin Fara Wayau kenan.."
Itako Farida Motar Ta ta Ta Shiga Taba ta Wuta sai da Ta Fahimci Lafiyarta kana Ta
saki Hon Megadi ya Buɗe mata Ƙofa ta Fice da Gudu Cikin Lokaci kaɗan Ta Ɗauki
Hanyar Ɗanbatta Zuciyarta Cike da Fargaban Wani Irin Hukunci Zata karɓa Wajen Umma
da Abba.
*Aisha Alto*
*Shakira*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
Ƙarfe 2:40pm. Ta isa Ɗanbatta, Tahir da Hakimi da sauran mutane suna zaune a ƙofar
gidan suna karɓar gaisuwa gurin jama'a masu zuwa musu ta'aziyya, haka ta ratsa tana
sunne kai ta shige cikin gidan, tana shiga direct ɗakin Goggo Abu ta dosa.
Tana shiga da Umma suka fara haɗa ido, rass taji gabanta ya faɗi tana turo baki ta
ƙarasa ciki ta zauna a kusa da Goggo Abu ta duƙar da kai taƙi kallon kowa dake
ɗakin, Mufeeda kuwa tana ganin Farida ta shigo tayi maza ta miƙe ta fita falon
Goggo ta zauna, don bata son abinda zai haɗasu da Farida guri ɗaya, gani take zata
iya rufeta da duka don haka take jin tsoronta.
Miƙewa Goggo Abu tayi itama ta fito falo gurin Mufeeda ta zauna akabar Umma da
Farida kaɗai a cikin uwar ɗakin, ɗagowa Farida tayi tana kallon Umma tace "Umm..."
Da sauri Umma ta dakatar da ita tana watsa mata harara take faɗin "Uban me ya kai
ki gidan Bilkisu Farida...? Wato dai ke har yanzu bazaki natsu kiyi hankali da
duniya kisan me take ciki ba ko Farida.? Yanzu da kika je gidan Bilkisun uban me
kikaje tayi miki? Me ma yasa kika saka ƙafa wai kika bar gidan mijinki da 'ya'yanki
bayan duk irin faɗan da nayi miki ranar kafin mu tafi? Wato baki ji ba shine kika
shure kika tafi gidan ƙawa har na tsawon kwanaki huɗu kina can a zaune saboda gaki
ballagaza ko...? To uban me kika je yi gidan aurenta tayi miki..? Tana zaune da
mijinta lafiya ke da baki san mutunci da darajar naki mijin ba shine kika kwashi
jiki kika tafi gidanta tayi miki maganin taki matsalar ko?" Ta faɗa a hasale tana
ji aranta kamar ta tashi ta rufeta da uban duka saboda takaicinta, ita ko Farida
wani bala'in haushin Bilkisu ta ƙara ji a zuciyarta, take wasu hawaye suka fara
zubowa daga cikin idanunta Umma na kallonta tace "Ai kuka kam yanzu kika farashi
Farida..tunda dai kince ke ba mai hankali da tunani bace balle kisan ya kamata, na
ɗauka zaki yi nadama ne saboda abinda sakacinki da toshewar tunaninki ya janyo muku
ke da mijinki, ashe ba haka bane, ke inda tunaninki yake daban, abinda kika
ɗaukarwa zuciyarki tun farko shi zaki ci gaba da yi. To kiyi Farida, bance ki fasa
ba kici gaba..." Haka Umma tai tawa Farida faɗa, ta inda take shiga ba ta nan take
fita ba, Farida kuwa in banda kuka ba abinda take yi har da shassheƙa, sai yanzu ne
ita da kanta take ganin aibun abunda tayi a rayuwarta, bata kyautawa kanta da
'ya'yanta ba, uwa uba kuma mijinta, bata tashi sanin babban kuskuren data tafkawa
rayuwarta ba, sai data je gidan Bilkisu taga yanda take yiwa mijinta take kaffa
kaffa dashi, bata haɗa komai da mijinta ba. Ita yanzu wace riba zata ce taci na
irin halayen dasu Bilkisu suka dinga zigata suna ɗorata akai kuma tana bi...?
Umma ce ta katse mata tunanin da take da faɗin "Yanzu a irin waɗannan abubuwan da
kike yi wace riba kika samu? Me kuma zaki ɗorar? Miji ya gaji da halinki, har ya
daina damuwa da duk wasu lamura da suka shafeki, kin kaisa bango halayenki sun gama
isarsa, kin tafi kin bar gidan mijinki da 'ya'yanki kin tafi gidan ƙawa kin zauna
har tsawon kwanaki, kin gama fallasa kanki da zuri'arki a gaban ƙawayenki, sirrin
gidanki da komu bai kamata mujishi ba kin gama tallatashi a titi ga wasu can kinyi
terere da mijinki, don nasan sai kin gaya musu duk abinda yake faruwa, tunda
tunaninki ya gama toshewa..." Ta faɗa tana murmushin takaici, wani kukan baƙin ciki
Farida ta fashe dashi tana girgiza kanta, kafin ta ɗago hawaye na tsirarowa daga
cikin idanunta tace "Umma don girman Allah..." Sake dakatar da ita Umma tayi da
faɗin "Komai kika yi fa kanki kika yiwa, nidai zanci gaba da tayaki addu'a Allah ya
shiryeki yasa ki gane gaskiya. Don haka maza ki tashi kije ki yiwa Mufeeda
gaisuwa..." Ta faɗa tare da miƙewa, itama Faridan tashi tayi tana share hawayen
fuskarta tabi bayan Umma suka fito falo, inda Goggo Abu da Mufeeda suke sai Nailah
da Iya da Maman Lantana, Umma zama tayi a kusa da Mufeeda tana kallon Farida da
tayi tsaye tana kallon Mufeeda a sace tana turo baki alamar bazata iya ba an takura
mata, wani kallo Umma ta watsa mata ba shiri ta dubi Mufeedan data sunkuyar da kai
ƙasa tana wasa da bakin hijabinta, sai data zabga mata uwar harara kafin ta ɗauke
kai tana faɗin "Ya ƙarin haƙuri...Allah ya jiƙanta ya gafarta mata.." Ta faɗa a
tare tana zama a kujerar dake falon.
Ranar a nan Umma ta kwana yayinda Abba kuma suka juya shida direba suka koma wanda
sai ranar addu'an uku sannan zai dawo bayan anyi addu'an uku da safe sai su koma
tare da Umma.
************
Yau akayi addu'an ukun Inna Fulera, bayan mutane duk sun watse yayi saura sai yasu
yasu a gidan, suka taru dukkansu da Baba Hakimi da Goggo Abu da Innaro da Tahir da
Ashe dasu Basma da Bassam sai Farida da Mufeeda da Umma da Abba.Sai Ishaq da Zahra
da Suka zo Suma, Sai da suka haɗu gaba ɗayansu kafin Baba Hakimi yasa Tahir yayi
addu'a aka shafa, sannan ya fuskanci Mufeeda wacce ke zaune a ƙasa ta duƙar da
kanta ƙwalla na zubo mata, nan ya shiga yi mata nasiha sosai da nuna mata ta dinga
yiwa mahaifiyarta addu'a ta daina mata kuka, kanta ta gyaɗa masa kafin ta ɗago tana
share ƙwallar tausayin kanta.
Umma ce ta gyara zamanta tana kallon Abba take faɗin "Gata nan Alhaji ka tambayeta
inda ta tafi tabar gidan mijinta da 'ya'yanta tsawon kwanaki bata gidan
aurenta...ba tare da tazo gida ba, ba kuma tazo nan Ɗanbatta ba..." Ta faɗa tare da
nuna masa Farida da tayi tsuru tsuru tana raba idanu, wani kallo Abba yayi mata
yana faɗin "Au wato bayan mun tafi shine tabar gidan tayi wani guri, saboda bata ji
maganar da mukayi mata ba..?" Gyaɗa kai Umma tayi tace "Ai kuwa babu abinda ta
ɗauka a faɗan da akayi mata.." Ta faɗa tana kallon Farida.
Gizgiza kai Baba Hakimi yayi yana faɗin "A'a bafa kusan dalilinta na barin gidan
ba, ƙila dai akwai abinda shi Attahirun yayi mata ne..." Da sauri Abba ya katseshi
da faɗin "A'a Mansur, karka ce haka, ai yana gaba da ita, kuma ko ba haka ba ai
mijinta ne shi, kuma kome zaice mata ai bai kamata ace tayi fushi tabar gidan ta
tafi wani guri daban inda ba'a sani ba..."
Baba Hakimi na kallon Abba yace "Ka bari muji abinda ya faru a bakinta tukunna..ke
Farida faɗa mana abinda Attahiru yayi miki da yasa kika bar gida..?" Ya faɗa yana
kallonta, ƙara sunkuyar da kai tayi ta shiga rattabo abinda ya faru ranar bayan
tafiyarsu tana haɗawa har da sharri tana ƙullawa, tunda ta fara maganar kawai Tahir
ya girgiza kai yana sakin murmushi bai ce komai ba, har ta dasa aya...
A harzuƙe Abba yace "Wato a ranar da muka gama magana akai miki faɗa a ranar kika
sake shuka wata tsiyar ko Farida..? To ki sani wallahi tallahi babu inda Mufeeda
zataje tana nan zaune daram a gidan anan zata zauna ta haihu, sai dai ke kibar
gidan don ubanki kije duk gidan ubanda zaki amma banda gidana, kuma wallahi duk
ranar da kika sake fita kika je wani waje bada yawun mijinki ba ko kika fita saboda
nuna kinfi ƙarfinsa Allah ya isa bamu yafe miki ba, tunda ke bazaki taɓa yin
hankali ba..." Ya faɗa a zafafe yana sauke numfashi, sake rushewa da kuka Farida
tayi har tana jan numfashi kamar zata shiɗe saboda baƙin ciki, nan Umma ma ta ƙara
dasawa sukayi mata tass, abin mamaki Goggo Abu na zaune tayi laƙwas sai bin kowa da
kallo kawai take ta kasa magana.
Baba Hakimi ma yayi mata faɗa sosai sannan ya haɗa har da Tahir shima yayi musu
faɗa kafin ya ɗora da faɗin "Kiyi haƙuri Farida ki rungumi Mufeeda ki tausayawa
rayuwarta, ki zauna da ita lafiya kinga marainiyace, ki ƙara riƙeta kamar yanda
kika fara riƙeta ada..idan cikinta ya isa haihuwa watan ya tsaya Innaro zata zo can
gidan naku ta zauna don ta riƙa kula da ita har ta haihu.." Ya faɗa yana ƙara
lallashin Farida kan ta zauna lafiya da mijinta ta kula da 'ya'yanta.
Daga ƙarshe dai Baba Hakimi ya saka musu albarka tare da yi musu fatan alkhairi da
gamawa lafiya dukkansu.
Nan Tahir ya matso gaban Abba ya duƙar da kai bai ce komai ba, lura da hakan da
Abba yayi yasa yace "Me yake faruwa ne Tahir.? Ko akwai wata matsala ne kuma...?"
Jinjina kai Tahir yayi alamar Eh.. Abba na gyara zama yace "Ka faɗa min ko mene ne
Tahir insha Allahu indai inada dama Allah ya bani iko zanyi maka maganinsa..."
Cikin jin daɗi Tahir ya ɗago yana faɗin "Dama Abba inaso ne ka roƙi Baba ya yafewa
Goggo Abu.." Ya faɗa yana jin ƙwalla na taruwa a cikin idanunsa, saurin ɗagowa Abba
yayi yana kallon Baba Hakimi, kafin yayi magana Baba Hakimi ya rigasa yana murmushi
yace "Na riga na yafe mata duniya da lahira, Allah kuma ya yafe mana baki ɗaya ya
kiyaye gaba.." Da Ameen duk suka amsa, kafin Tahir ya fara miƙewa Shida Ishaq
suka fita daga ɗakin suka nufi ƙofar gida gurin Sauran Jama"an Dake Wajen Wadanda
Suka zo Addu"arku Uku ba Dadewa sai ga Su Abba Suma Sun Fito Suna Tattaunawa shida
Baba Hakimi.
A ranar Umma da Abba suka koma Kano, da yamma suma su Tahir da Farida da Iya da
Mufeeda da yara duk suka tattara suka yi shirin komawa Kaduna, mota biyu sukayi
Tahir da Farida da Mufeeda suka shiga motar Ishaq, su kuma Basma da Bassam suka
shiga motar Tahir da Garzali ya tuƙo suka ɗauki hanya, bayan sun bar motar Farida a
nan gidan Baba Hakimi akan washegari Garzali zai dawo ya ɗauka.
******
A hankali abubuwa suka fara daidaita, sai dai Farida tana tsananin kishin Mufeeda,
amma tana ƙoƙarin dannewa bata son a gane, don irin tsantsar kulawar da Tahir ke
nuna mata kwata kwata bata so, amma tana yi tana dannewa, bata so a gane tana jin
haushi.
Haka a ɓangaren Tahir shima kwata kwata baya ganin hasken Farida, don ta gama sire
masa gaba ɗaya a ransa, daurewa kawai yake yana nuna kulawarsa a kanta, kuma yana
ƙoƙarin sauke hakkinta dake rataye a wuyansa, amma duk ɓoyewarsa sai data gane, don
a komai ya ƙara canza mata sosai, kusan rabin kulawarsa gabaki ɗaya yanzu duk ya
ɗorata akan Mufeeda ne.
A lokacin ne kuma su Mufeeda suka shiga Jss2 suna ci gaba da karatunsu, bata da
matsalar komai ta ƙara wani kyau da haske, sai dai kusan kullum kafin tayi barci
sai ta tuna da Innarta, idan tai kuka sai ta share hawayenta kuma tayi mata addu'a.
Haka rayuwa taci gaba da tafiya wani lokaci aji daɗi wani lokacin kuma aji akasin
haka,Farida Bata Kaunar Ta Bude Ido Taga Mufeeda da Ciki Acikin gidannan Tsoronta
Daya ne Abba da Umma Tasan yanzu Abu kadan Zatayi Suyi Fushi da Ita Sosai,Abunda
kuma ke karamata Kishin Mufeeda Shine ganin yadda Tahir ya Watsar da al"amarinta
bai Cika damuwa da Al"amarinta ba,gasu Bassam Sun ki marata baya Sun bi Bayan
Mahaifinsu,Haka Suke Kafa kafa da Mudeeda kamar su lasheta komai take bukata tana
samu Koda yaushe Cikin Tallalinta Sukeyi.
Tuni Farida ta Watsar Da Shawaran Kawayen banza,Tunda Agroup Dinsu Billy Taje Tana
bada Lbrin Zata kwatar mata yanci Ta gayamata mgana Ranta ya baci,ta Shiga group
din Ta maida mata martani Tamata Wankan Tsaki Billy Tasan bata da gaskiya Sai ta
kama kame kame,anan Akayita bata Hakuri Daga karshe Fitama Farida Tayi Daga Group
Wasu Dadama Sun Bita Suna bata Hakuri Suna Fadamata Kowa Data gani Anan yana
lallaba Aurensa ne,ba wani mai Sakaci,sai Lokacin Farida Tagane tayi Wauta
babba..Wato Duk Acikinsu itace Sakarya Tayi Kuka Sosai kamar Ranta zai Fita Tayi
Nadama sanda bashi da amfani,Tadaina Fita kwata kwata Wanda Ta gyara Domin Shi ko
kallo bata Isheshi Ba Domin yafi Nuna kalawarsa Akan Mufeeda Fiye Da Ita,Abunda
yasa Farida Rama kenan Atsaye Duk tayi Wani Zuruzuru Da Ita.
***********
Cikin Mufeeda ya ƙara fitowa sosai yayi girma gwanin ban tausayi, Tun yana Wata
Hufu Tafara Zuwa Awo Anan Iyali Hospital,kuma shi yake kaita watarana In yana da
Lokaci Ranar dai bai samu Zuwa ba sai Garzali ya kaita ita da Innaro,tsufan cikin
nata ne, yasa Tahir ya hanata zuwa islamiya yace ta riƙa zama a gida makarantar
boko zata rinƙa zuwa kaɗai, duk ranar da ba makaranta tana zaune a gida, hakan yana
ƙona ran Farida sosai ya baƙanta mata zuciya, don ta tsani ganin cikin bata ƙaunar
tayi tozali dashi kwata kwata a rayuwarta, jira take kawai Mufeedan ta haihu Tahir
ɗin yasan nayi da ita.
Baba Hakimi ya cika alƙawari Tahir na sanar Dashi Cikin Mufeeda ya Cika Wata Tara
yace ya Aiko Garzali ya Ɗauketa, nan da nan kuwa ya aikashi sai ga Innaro Ta Iso
Abunda ya ƙara baƙantama Farida rai ganin Ɗakin Mufeeda Tahir yace A sauketa Suna
Murna kamar ba Ɗan Shege za'a Haifa ba, Haka Tazo da Jiƙe jiƙe Saboda Maganin
sanyi, Take Ta bama Mufeedan Ita da Iya ba'a san Wanda yafi Wani kula da Mufeedan
ba, Goggo Abu kuwa Batama ta Farida yanzu Domin Da ƙyar ta samu bayan Abba ya saka
Baki Hakimi ke Kulata Ko a hakan ba kamar baya ba, Shiyasa Take ƙoƙarin gyara
Kuskuranta ta kuma Ƙudirci Wani Abu A ranta Jira kawai Take Allah ya Sauke Mufeedan
lafiya Ta Aiwartar da Ƙudirinta Domin yanzu Tausayin Mufeedan Take Kullum Cikin
Kira Take awayar Innaro Ana bama Mufeeda Tana Tambayanta Me take ji..? Wani Lokacin
Dariya kawai Mufeeda keyi bata cewa komai Domin Yawanci Tambayan Tahir kenan Inya
Shigo Dubata da Safe da Kuma bayan Ya Dawo ko Shi bata bashi Amsa sai dai ta
Sunkuyar Da kai Aranta Tana Jin Daɗin yadda Daddy ya fara maida Jikinshi ba kamar
Farkon Al'amarin ba.
*Anitha...*
*Aisha Alto...*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
*BABI NA ASHIRIN*
""Ɓangaren Kayan Haihuwa Kuwa Babu Abunda Tahir bai gama Siya ba Kuɗi masu yawa ya
Ware ya bama Matar Ishaq Zahra ta sayo komai da komai Kayan jariri kuwa komai Biyu
ta Siyo na Mace Dana Namiji Tace Saboda Tahir bai yarda an mata Scanning ba, balle
aga mai Zata Haifa.
Kuma Zahran Da kanta ta kawo Kayan Gidan, Abunda Ya ƙarama Farida Ciwo yanzu Har
Takai matsayin da Bata da Wani amfani Wajen Tahir, ya maida kanshi dashi da
'yan'uwansa da Iyayensa Wajen Tattalin Mufeeda, Sai dai Tayi Wuni Cikin Ɗakinta
Taita kuka bamai lallashinta Ita baga kulawan Miji ba Haka Zalika ma Su Bassam
banda Gaisuwa babu Abunda Ke Haɗasu Koda yaushe Suna Ɗakin Mufeeda suda Iya da
Innaro Wani Lokacin Tana Falo sai dai Tajiyo hirarsu Da Dariyansu Mufeeda kuwa Ko
ta ganta ta gaisheta Farida bata amsawa Sai dai Ta bi Cikin Jikinta da kallo Cike
Da Kishi ganin yadda yayi Girma yana Neman Rinjiyan Mufeedan, Burinta da Fatanta
Allah Ya Sauke Mufeedan Lafiya ta ƙara gaba Allah barshi abunda Zata Haifa In Ta
gama Shayarwa akaisa gidan Marayu Domin ba Wanda Zai Gurɓata mata 'ya'ya dana Shege
******
Yau ɗin takama Jumma'atu Babban Rana ce, Misalin ƙarfe 9 na Safe Duka suna Zaune A
falo Suna Hira Innaro, Iya da Basma sai Bassam Dake wasa da Naila Wacce Take
Tafiyanta yanzu Sai Mufeeda dake Zaune kasan Cafet Ta Buɗe ƙafa Hannayenta na Baya
ta Dafa ƙasa Ga Cikinta nan Wani Randa guda yayi girma sosai har yayi ƙasa, Ta
kumbura Ko'ina na Jikinta ya Buɗe ya ƙara Girma, In ka kalleta Farat Ɗaya kamar ba
Mufeeda ba Domin Ta Cika Ciki ya sakata tazama ƙatuwa, su Basma suna Hutun Ƙarshen
Shekara in suka koma zasu Shiga jss3 hadda kawai Suke Zuwa yanzu da Islamiya.
Aya ce agabanta Tana ci Tana Dariyan Labarin da Iya ke basu na Matar ƙaninta da Ta
faɗa masai, Basma Saboda Dariya Harda Riƙe Ciki, Mufeeda ma Dariyan Take lokaci
Ɗaya tana Cin Ayanta, Farida Data Sauko Daga Sama ta bisu da kallon Takaichi Da
ƙyar ta iya Buɗe baki Ta gaida Innaro, Iya ta gaidata Hakama Su Basma Duk ta amsa
amma Mufeeda na Gaisheta tayi kamar bata jiba ta Shige Kichen Abunta Mufeeda bata
damu ba Domin Inda Sabo ta Saba da Hallayar Farida.
Ruwa ta Ɗauko Kafin Ta sake Haurawa Sama Ƙofar Bedroom D'in Tahir Tabi da kallo,
Tun Jiya Daya Dawo Daga Lagos bai sake Fitowa ba, Buɗe Ƙofar tayi Ta Shiga ta
Iskeshi kwance Cikin Bargo yana barci Ƙyalesa Tayi Ta Fito Daga Ɗakin Tana Tunanin
gajiyace Domin Wajen Satinsu Daya achan Shida Ishaq ne Suka Tafi Taran Sabbin
Motocinsu da Zasu zo ta Jirgin Ƙasa, Toh basu iso ba Sai Shekaran jiya Da Daddare
Su kuma jiya suka taho Zuwa Kaduna.
Ɗakinta ta koma ta Sha Ruwa kana Ta Koma ta kwanta Tana Tunanin Da Zarar Mufeeda Ta
Haihu Ta bar mata gida Zata gyara Duka mu'amalanta da Mijinta Harda 'ya'yanta
Batasan Cewa Lokaci Tuni ya Ƙure mata ba.
Mufeeda Dake Dariya Ƙasa ƙasa, Taji kamar bayanta ya amsa Da Sauri ta gimtse
Dariyan Tana jin Lokaci Ɗaya maranta ya Ƙulle, Cije baki tayi ganin ba Wanda ya
lura da Halin Data ke ciki Ta Dafa Kujeran Ta Miƙe A hankali Tana Cije baki Lokaci
Ɗaya Innaro da Iya Suka kalleta kafin Innaro taceb"Mufeeda lafiya..? Ina zaki
Haka..?"
Saurin Sakin Murmushi Tayi kafin tace "Bakomai Innaro Toilet zan Shiga.." Innaro
tace "Ayyah..Jeki Dawo.." Ta faɗa Tana kallonta da Sauri Mufeeda ta Fara Taku Zuwa
Ɗakinta Tana Daurewa amma Fa Cijewa kawai take saboda yadda Ƙugunta ya Riƙe ga
Maranta ta Ƙulle Waje Ɗaya,bHar ta Shige Ɗakinta Innaro na Binta da kallo kamar
tana so Ta Ɗago Wani Abu...
Mufeeda Da ƙyar Ta iya kai kanta Tsakiyar Ɗakinta kafin ta Durƙushe Tana Riƙe gadon
Hannu Biyu Jin Ƙugunta kamar zai Tsage gida Biyu, Zufa ce ke Keto mata kamar Wacce
Ake Gasawa Salati Mufeeda ke Saki Cikin Ranta Lokaci Ɗaya Hawaye na Wanke mata
Fuska ko Bata sani ba Wannan Azaban Data keji Ta Gane Naƙuda ce, Tun Abun na Ƙasa
ƙasa Har ya gagari Tunanin Mufeeda Kuka Take Wurjajan da Majina Domin Tagama Yanke
Kauna wallahi Mutuwa Zatayi domin Wannan Azaba Ta mutuwa ce.
Innaro ce Taga Shirun na Mufeeda Yayi yasa Ta kalli Basma Tana Faɗin "Ke Basma Maza
Tashi ki Dubo min Mufeeda najita Shiru ne.." Da Hanzari Basma Ta Miƙe Ta Nufi Ɗakin
Mufeeda Halin Data Tarar da ita ya bata Tsoro Cikin Firgici Tace "Innaro kuzo kuga
Mufeeda.." Ta fada da Ƙarfi Jin Haka yasa Innaro da Iya Suka fara Rige Rigen Shiga
Ɗakin Mufeeda Hankalinsu a Tashe, Bassam Dai Naila ya Ɗauka Wacce Ta Fashe da Kuka
lokaci Ɗaya bai bisu Ɗakin ba ya dai Tsaya A falon yana Tunanin ko lafiya...
Kallo Ɗaya Innaro Tama Mufeeda Ta Fahimci Tana kan Gwiwa Basma Ta kallah Wacce Har
Ta fara Hawayen Tausayin Mufeeda tace "Maza kije ki kira min Daddynki.." Da gudu
Basma Ta Fita ta Haura sama Tahir na kwance Cikin Barci Yaji Basma na Faɗin "Daddy
Daddy...Ka Tashi Innaro na Kira Mufeeda Zata Haihu Tana ta kuka.." Take Faɗa Tana
Kuka Itama.
Zumbur ya Miƙe Daga Kwancen Yana Kallon Basma Ido ya Zaro yana Faɗin "Zata Haihu
kika ce Basma..?" Kai ta gyaɗa mai tana Share Ƙwallah da Hanzari ya Dirko Daga kan
gadon Da gashi sai Dogon Wando Jallabiyansa ya Laluba ya saka ya zari Key ɗin Mota
ya Fita Da Sauri Basma Tabi Bayanshi Fitowarsu Da Hanzari ya Fito Da Farida Daga
Ɗaki Ganin Tahir da gudu ya Sauka Ƙasa yasa Itama Tabi Bayansu da Sauri Tana
mamakin Me ya Razana Tahir Lokaci Ɗaya Haka..?
Tahir ko na Shiga Ɗakin Mufeeda Yaga ba yarda Take Innaro na mai magana bai
Saurareta ba kawai ya Cicciɓi Mufeeda Zuwa Waje yana Faɗin "Innaro ki Ɗauki Mayafi
mutafi Asibiti.." Farida Dake Ƙoƙarin Shiga Ɗakin Mufeeda Tayi Baya ganin Tahir ya
Ɗauko Mufeeda Tana Faman kuka tana Yarfa Hannu, suman Tsaye Tayi Cike Da Takaichi
da Kishi Wai Tahir ne ya Ɗauki Mufeeda da Hannunsa Niko Nace Yamata Cikin ma balle
Ɗauka.
Bata gama Mamaki ba Iya da Innaro Da Suka Rufa mai baya Da Gudu Mayafai A hannu
Saboda Zullumi sai ga Basma Ita ma da Hijabi Ta Runtuma tabi Bayansu, baki ta Riƙe
Cike da Baƙin ciki Lokaci Ɗaya kuma Falon ya ƙara Ɗaukan Kukan Naila, Daga Nailan
Har Bassam D'in Da Harara Ta Bisu kafin Ta Saki Tsaki ta koma Sama Tana Ƙunƙuni Ita
kaɗai.
Tahir ko Garzali bai Saurara ba ya Kai Mufeeda Bayan Mota, Ya Dawo Gidan Gaba
Mazaunin Direba ko Su Innaro Dake Fitowa Haraban Gidan bai Jira ba ya Kunna Mota
yayi Reverse da Ƙarfi lokaci Ɗaya ya saki Hon ya Fice Da Gudu, Su Innaro basu Tsaya
ba Suka Faɗa Mota Basma Ta Shiga Gaba Innaro Tace "Garzali bi mana bayan
Attahiru..." Cikin Bin Umarni Garzali yaja mota Yabi Bayan Tahir Daya Nufi Asibitin
Iyali Hospital Dake Kusa Dasu.
****
Koda Tahir ya gama Faka Motarsa Cikin Haraban Asibitin Bai Jira Wani ba, Ya Fito
Daga Mota ya Buɗe Baya ya Cicciɓo Mufeeda Dake kuka Wurjajan Lokaci Ɗaya Da Salati
Domin Ji Take kamar Zata mutu da Gudu ya Nufi Cikin Asibitin Da Ita ganinshi Haka
ne ya saka Nurses Da Gudu suka gungoro Gadon Ɗaukan Marasa Lafiya Zuwa Gareshi
ganin kamar ya Fita Daga Hayyacinsa yana Kiran Likita.
Kan Gadon ya Ɗora ta da Hanzari Suka Shiga Turata yana Bin Bayansu cikin Tashin
Hankali Labour Room Suka Shiga da Ita Suka Rufo ƙofa Dole Tahir ya Tsaya Awaje yana
Safa da Marwa sai ga Su Innaro Sun Shigo Asibitin Hankalinsu Tashe Cikin Fargici
Innaro Tace "Attahiru Ya Ake Ciki...?" Numfashi ya Sauke yana Faɗin "Bansani ba
Innaro Sun Dai Shiga da Ita Ciki..." Gefe Suka Koma kowa na Addu'a Cikin Ransa
Basma ko Hawaye Take Sharewa Suna nan Tsaye Wata Nurse Ta fito da Gudu Ta Wuce
Office d'in Likita, Sai gashi Sun Fito A tare Cikin Hanzari Sun Koma Cikin Ɗakin
Daga Wajen Suna Jin Salatin Mufeeda Da Kukanta Lokaci Ɗaya Tahir yaji Jikinsa ya
Saki Ƙwalla Ta Cika mai ido yana Fatan Allah ya Sauki Yarinyar nan lafiya kada ta
Mutu Da Cikin nan ya Shiga Uku.
Tsawon Awa Ɗaya Likitoci na Shige da Fice kan Mufeeda Haihuwa Shiru nan da nan Suka
mata Scanning Nan Suka gano yan Biyu ne A cikinta amma Sun Galabaita, yunƙurin
Fitowarsu da kansu Matsala ne, Nan da nan Wani Likita ya Fito Yana Faɗin "Ina
Mijinta...?" Da Hanzari Tahir ya Isa Gabanshi yana Faɗin "Gani Dr..Hop ta Sauka
lafiya.." Kai ya girgiza mai kafin yace "Biyoni Office da Sauri bamu da Lokaci.."
Jin Haka yasa ya bishi da Hanzari, Zuwa Cikin Office Ɗinshi Suna Shiga Ciki ko zama
baiyi ba ya Miƙa mai Wata Takarda yana Faɗin "Muna Buƙatar saka Hannunka anan, zamu
Shiga da Ita Aiki ne yanzu Domin Ceto Rayuwarta data yaran Dake Cikinta.." Tahir na
Zufa ya karɓa Takardan Haɗe da Biron ya Rattaba Hannu, kafin Likitan ya karɓa yana
miƙa mai Wata ƙaramar Takarda yana Faɗin "Ka biya Kuɗin Aiki yanzu..." Tahir bai
Tsaya ba ya Fito da Sauri su Innaro Dake Zaune Suka miƙe Suna kallonshi Kanshi ya
Shafa yana Faɗin "Sun ce aiki zasu mata yanzu...Ku zauna anan Bari naje na Biya
Kuɗin Aikin Na Dawo.." Innaro tace "Toh kana da Kuɗi A hannunka..?"
Yana Tafiya yake Faɗin "A'a Sai dai Atm ɗina zanyi Amfani Dashi.." Ya faɗa yana
Ƙara Sauri Cikin Minti goma Sai gashi ya Dawo da Resit ya Riga ya Biya Kuɗin Aikin
bai Daɗe da Isowa Wajen ba Sai ga Mufeeda An Gungurota Zuwa Ɗakin Tiyata an Chanza
mata kaya, Kuka Take da Salati Lokaci Ɗaya Suna kallo Aka Shiga Da Ita Gefe Suka
koma Kowa Da kalan Addu'an Dake Ranshi barin ma Tahir da Abun Duniya Suka Taru Suka
mai yawa...
Shuɗewar Awa Biyu Kafin wasu Nurses Guda Biyu Su Fito Daga Ɗakin Tiyatan Ɗauke da
Yara Guda Biyu Cikin Wasu Showels, da Hanzari Suka miƙe Suna kallonsu Cikin Fara'a
Ɗaya Tace "Congratulation ta Sauka An Samu Twins, mace da Namiji..." Gaba ɗayansu
Suka Haɗa baki Wajen Faɗin "Alhamdulillah." Innaro Ta karɓi Namijin Iya kuma Ta
karɓi Macen Dukkansu bakinsu yaƙi Rufuwa Shiko Tahir Hamdala yake Acikin Ranshi
kafin yace "Ina ita Maman Yaran..?" hope tana lafiya.." Ɗayar tace "Eh ana gyarata
ne da Zarar an kammalah zamu maidata Ɗakin Hutu.." Daga Haka Suka Wuce, Chan sai ga
Likitocin Suma Sun Fito Suna Cire Safan Hannu, Musabaha sukayi da Tahir Suna mai
Murna, Bakin kowa yaƙi Rufuwa, Bai Ɗauki yaran ba Domin Wani Tausayinsu ne ya
Tsirga mai na Ya samar Dasu Ta Hanyar da bai dace ba, Ashe Dalilin Daya sa ya
Afkama Mufeeda Kenan Rabon samun Waɗannan ne ya Kawo Haka.
Ba ɓata Lokaci aka Gunguro Mufeeda Zuwa Ɗaki na Mussaman Domin Hutu, Suka ce Kar
wanda ya Shiga Inda Take Sai ta Farfaɗo bayan Awa biyu da wani Abu, Yanzu aje azo
da kayan Jarirai da Kayan Tea d'in da Mai Jego zata Buƙata in ta Farfaɗo, Tahir ne
ya barsu anan ya Koma gida, Farida na Jin Dirin Mota ta Zabura ta Fito Falo Suka Ci
karo da Tahir Cikin Rawan Baki Tace "Ta Haihu..?"
Bai kalleta ba yace "Eh amma C.s Aka mata an Ciro 'Yara Biyu mace da Namiji.." Dafe
ƙirji Farida Tayi kafin Tace " 'Yan biyu fa kace...?" Ta faɗa Tana kallonsa Bai
mata magana ba illah binta da Kallo Da yayi kafin yace "Eh Abunda Kunnenki ya jiye
miki..." daga Haka ya Wuceta ya Barta sama ya Koma ya Ɗauko Wayarsa ya Sauko, Ɗakin
Mufeeda ya Shiga Inda ya Tatarro Duka kayan Babies, Sai kuma Dogayen Riguna da Riga
da Zani, ya Fito Nan ya Wuce Farida Tsakiyar Falon Tana Binshi da Kallo, Bassam ne
ya Biyosa yana Tambayansa Mufeeda Ta Haihu Cike da Fara'a Tahir ya Ɗaga mai kai
kafin yace "Kun samu ƙanne Bassam 'Yan'uwanku ne Twince ne Suma.." Washe Baki
Bassam yayi Harda Tsalle yana Faɗin "Daddy Zan Bika.." Bai ce mai komai ba sai ma
Miƙa mai Jakar Kayan Mufeeda da yayi Suka Fice Daga Falon.
Sai da Tahir ya kawo Kayan Kana Aka maida Yaran Ciki aka Sake Gyarasu aka Shiryasu
Cikin kayan Sanyi pick masu kyau Ɗakin da Mufeeda Suke Suka maidasu, suka ce suma
abarsu Su Huta Haka nan, Bakin Basma da Bassam yaƙi Rufuwa saboda Murna Sai Lokacin
Tahir ya samu Damar Kiran Baba Hakimi yake Sanar Dashi Baba Hakimi Dake Shirin Fita
Sallar Azahar ya Washe Baki yana Faɗin "Kai Masha Allahu...Allah ya inganta.." Daga
nan Abba ya Kira Shima ya Sanar Dashi, Shima ya Saka albarka, Daga Abba sai ya Kira
Ishaq ya Sanar mai, Wanda ke Zuba kabbara Cikin Waya kafin Kace me Haihuwan Mufeeda
Ta isa Kunnan Wanda ya kamata Farin ciki kamar bata Gurɓattaciyar Hanya aka samesu
ba.
****
Baba Hakimi Na gama Waya da Tahir ya Shiga Cikin Turakarsa ya Ɗauko Huhun Goro da
Dabino Cikin Wata Leda Waje ya Fita Zuwa Masallacin Kusa da gidan nashi Lokacin Har
An Tada Sallar Jumma'a Domin Babban Masallaci ne Wanda ke Jikin Gidan nashi Inda
Suke Gudanar da Sallar Jumma'a.
Bayan An idar da Sallah Baba Hakimi Ya bada Sanarwan Akwai ɗaurin Aure nan da nan
ko Kowa ya Matso kuɗi ya Fito Dashi Duba 30k ya bama Liman yana Faɗin "Ina so
kazama Wakilin Ɗana Tahir, ni kuma zan zama Wakilin Mufeeda A Ɗaura musu Aure.."
Liman ya Washe baki ba tare Da bata Lokaci ba nan Take Shaidu Suka Shaida Ɗaurin
Auren Tahir Mansur Ɗanbatta da Mufeeda Bello Ɗanbatta, Auren Daya bama Kowa Mamaki
Domin Mutane Da dama Sun san Mufeeda A matsayin Wacce ke Reno A gidan Tahir, Cikin
Fari ciki Taro ya Watse bayan an Raba Goro da Dabino Baba Hakimi ya ɗibi Wasu ya
Shiga Dasu Cikin Gida Har Ɗakin Goggo Abu Wacce ke Cike da Murnan Wayar Da Tahir ya
mata yanzu Yana sanar da Ita Haihuwan Mufeeda, goro da Minti ya miƙa mata yana
Fadin "Na Ɗaura ma Tahir Aure da Mufeeda Yanzu bayan Mun Sauko Daga Sallar
Jumma'a..." Baki Goggo Ta Washe kafin tace "Mallam kamar kasan Abunda Ke Raina
kenan...Allah ya basu zaman lafiya.." Da Ameen ya amsa Cikin Jin Daɗin Haɗin kanta
Duk Da yasan bazai Samu Matsala ba.
******
Har Yammah Su Innaro na Asibitin Sun cika Ɗakin da Mufeeda Take bayan ta Farfaɗo,
Basma da Bassam Sun ƙanƙame yara Ko Tahir basu Bari ya Ɗauka ba, sai da Innaro ta
karɓe Macen Ta Hannun Basma Ta Miƙa mai ya karɓa Cikin Jin kunya Lokaci Ɗaya yana
Tsurama Jaririyar Ido Sak Basma Tana Jaririya, Lokaci Guda Idanuwansa Suka kawo
kwallah yayi Saurin Mayar Dasu Mufeeda Dake Jingine da Gado Tana kallonshi yana
Dagowa Suka Haɗa ido sai tayi Saurin Kauda kai Murmushi yayi ya ƙarasa Kusa da Ita
yana Faɗin "Mufee ya Jikin..?" Kanta na Ƙasa Tace "Da Ɗauki Daddy..." Kai ya gyaɗa
kafin yace "Masha Allah...Allah ya ƙara baki lafiya.." Da Ameen Ta amsa Ƙasa ƙasa,
kan Jikinta ya Ɗora mata Jaririyan Yana Faɗin "Kina Sonta...?" Kallonsa Tayi kafin
tace "Kaifa kana Sonsu...?" Kai ya Gyaɗa mata kafin yace "Ina sonsu Sosai kuma Zan
Cigaba da Ƙaunarsu Har Ƙarshen rayuwata.." Murmushi Ta Saki kafin tace "Nima ina
sonsu...." Dariya yayi yana kallonta kafin ya Miƙa Hannu ya karɓi na Hannun Bassam
ya Ɗora mata Bisa Jikinta yana Ƙoƙarin Zama Kusa Da ita Wayarsa ta Shiga Ƙara
Miƙewa yayi ya Zarota Ciki Aljihu sai yaga Hakimi ne Da Hanzari ya Fice Mufeeda ta
Bisa da Kallo Cikin Wani yanayi.
Fita yayi Haraban Asibitin kana Ya Ɗaga Kiran Cikin Farin ciki Baba Hakimi yace "Ya
Wajen Maijegon da Sabuwar Amarya don bazan Tambayi sabon Megidan Salamatu ba
Tunkafin ya Fito Duniya Take Nuna min Son kai.." Dariya Tahir yayi kafin yace "Duk
Suna lafiya Ranka ya Daɗe.." Baba Hakimi yace "Madallah kafin ya Zarce da Faɗin
"Attahiru na yanke Wani Hukunci ba tare Da nayi Shawara Da kai ba Domin ina ganin
Hakan Shine Daidai.." Tahir ya Jinjina kai yana Faɗin "Ka isa ne Ranka ya Daɗe
kowani Hukunci ne zan karɓa Hannaye Bibbiyu.." Baba Hakimi ya saki Murmushin Jin
Daɗi yana Faɗin "naji Daɗin Haka ba Komai Illah Ɗazu bayan sallar Jumma'a Na Ɗaura
maka Aure da Mufeeda yanzu Haka tana Matsayin Matarka ne Attahiru..Bata da wanda ya
fika ku Haɗu ku Rungumi 'ya'yanku Karsu Tashi suga bakwa Tare Su Tuhume ku Wata
rana.." Ajiyar Zuciya Tahir ya Sauke kafin yace "Hakane Baba...Allah ya bani ikon
Adalci.." Da Ameen Baba Ya amsa kafin Su yanke Kiran Bayan Baba Hakimi ya tabbatar
mai Suna Tafe ko yaushe.
Bai koma Cikin Asibitin ba yayi Tsaye yana Tunanin Wannan Al'amarin Guda Biyu
Lokaci Ɗaya Haihuwa da Aure, Dafe kansa yayi yana Faɗin "Alhamdulillah...Allah ne
Abun Godiya.." Yana Cikin Wannan Halin ya hangi motar Ishaq Ta Shigo Cikin Asibitin
Bai Matsa daga Wajen Ba Har Suka ƙaraso Shida Zahra ta gaisheshi Bayan Ta mai
barka, Shi ya musu Jagora zuwa cikin Ɗakin Suka Gaida Mufeeda Suka kuma Ɗauki Yaran
Bayan Sun gaisa da su Innaro Nan Suka bar Zahra Tahir yaja Ishaq suka Fita Waje
Cikin Damuwa ya labarta mai Abunda Baba Hakimi ya Kirasa ya gaya mai Baki Ishaq ya
Washe kafin yace "Finally...Baba Hakimi ya gama maka Komai Friend...Mufeeda Ta
Chanchanci Haka Domin Bata da Wani Gata Nan Duniya bayan kai...Gaskiya Allah sakama
Baba Hakimi da alheri Yayi Abunda ya Dace.." Tahir dai Shiru yayi yana Jin Ishaq
Shi kuma yana Cigaba da Bashi baki basu koma Cikin Ɗakin ba sai da Sukayi sallar
Mangariba, suna komawa Tahir yace Su Basma Su Shirya su Koma gida, Harda Iya gobe
da Safe sai su Dawo Innaro kaɗai Aka bari zata kwana da Mufeeda, Zahra tayi musu
sallama Bayan ta ijiye musu kwandon Abincin Da tazo Dashi. Tare Suka Fita Bayan
Tahir yayi musu Sai da Safe Mufeeda kuwa na Kwance Tana Binsu da kallo har Suka
Fice Daga Ɗakin.
*Anitha..*
*Aisha Alto..*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
"""Suna Shigowa gidan da Farida Suka ci karo tana Zaune Afalo Tana Zare ido Domin
gama wayarsu kenan da Umma tana Tambayanta ya Wajen masu jego tace suna lafiya
tanama Asibitin ne Tafito amsa waya ne,Umma taji Dadi tace mata suna nan Zuwa Cikin
Satin nan Ita da Abbanta......
Daga Tahir har ya"yansa Babu Wanda ya Tankata Kowannensu Dakinsa ya Nufi Haka Shima
Tahir ya Haura sama ya Fada Dakinsa A matukar gajiye yake Shiyasa yafada wanka,Iya
ce kadai ta iya tsayawa tana gaida Faridan wacce Tabi su Basma da kallon
Mamaki,Tahir ta Daina Damuwa dashi Domin baya Shiga Harkanta Tuni.
Bayan ta amsa gaisuwan Iya ne ta kalleta tana Fadin"Wai iya da gaske ne Mufeeda yan
biyu ta Haifa...? Gyada mata kai Iya Tayi Lokaci Daya tana Washe baki tace"Eh
Hajiya mace da Namiji yara nan kamar su Basma suna Jarirai inji innaro.."Harara
Farida ta Zabgamata Lokaci Daya Tana Fadin"Kul kar na sake ji...Ni ya"yana na
Sunnah ne karki kara Hadasu da Shegu wanda ba ya"yan Sunnah ba.."Cike da mamaki Iya
ke kallonta bata samu Zarafin mgana sai ma gyada kai Datayi ta juya Zuwa Daki bayan
ta kalli Naila dake barci kan kujera tagaji da kuka Barci ya kwasheta.
Da Harara Farida ta Bita kafin ta koma ta Zauna tana karkaɗa ƙafa, Iya tana Komawa
ɗaki ta Fito ta Shiga kichen domin sama musu saukakkan Abinci da zasu ci Shiko
Tahir Bayan ya Fito Wanka yayi sallar Isha'i da Shafa'i da Wuturi ya koma ya kwanta
domin Haka kurum yaji Cikinsa ya Cika baya Sha'awan Cin komai kwance yake kawai
yana Tunanin Wai shi yanzu mijin Mufeeda ne, Lalle Allah ne mai Tsara komai kuma ya
aiwatar yana Fatan Allah yasanya alheri yabashi ikon kwatanta Adalci Domin baya ta
Farida Ita yanzu bazai ƙara Ɗaukan Wani Iskancinta ba, Itama ta sani.
Da Iya ta gama Dafa musu macaroni da Kifi, Su Basma kaɗai Suka ci sai Iya ko Farida
bata ci ba ɗaki ta koma tana kukan Bakin ciki da Takaichin Wai Mufeeda Ta haihu har
'ya'ya biyu lalle ma wato zata Haɗa kafaɗa da ita, ba wanda yabi ta kanta Har
Washegari da Safe Tahir ya Tafi Office Su kuma Iya da Basma da Bassam da Naila data
saka Rigimar sai ta tafi Tahir baima sani ba Ya bari sai zuwa yammah su koma Tunda
ya tafi musu da Abun karyawan da Iya tayi musu Ashe su kuma suna Gama Dafa na Rana
suka tafi dashi Keke Napep Suka Shiga Zuwa Asibitin Suka bar Farida agida tana
kallon ikon Allah.
Sanda suka isa asibitin ma Sun Iske Zahra matar Ishaq itama ta kawo Abinci Mufeeda
na Zaune Innaro na bata Tea abaki Taji Sauƙi ba kamar jiya ba, Namijin ne ke Hannun
Zahra Shine mai Rigima macen na kwance Tana barci Naila Haka ta saka Rigiman sai an
bata Ta Ɗauka ganin Su Basma Sun Ɗauka harda kukanta Su Iya na mata Dariya, cikin
ikon Allah Ruwan Nonon Mufeeda ya Fara Zuwa ba laifi Tunda Dukkansu suna samu Suna
Sha Duk da baya isarsu Da Safe ma da Tahir yazo Likita yamai maganar za'a Haɗa musu
da madara saboda kada yunwa ta kamasu.
Kumburin Jikin Mufeeda ya Ragu amma ba Sosai ba, Sunyi Waya da Baba Hakimi da Goggo
Abu Awayar Innaro Kunya Mufeeda keyi Jin Suna Tambayanta Ya Jikinta bata magana sai
dai Murmushi Suna nan har Dare nan Ishaq da Tahir suka samesa bayan Sun Dubata Suka
Wuce gida Gaba ɗayansu bayan ya kawo musu Kayan marmari da Nama gashasshe saboda
Mufeeda Ta maida Jikinta.
Haka Suka Din gayi Har Tsawon Kwana Biyar, amma Farida bata taka Asibiti ba sai
Ranar da Mufeeda ta cika kwana Shida taji Sauki ma, har ta fara Zuwa Bayi da kanta
aikin ya fara Bushewa, Farida kunya taji Yasa ta Shirya taje Asibitin Aikwai Tayi
Nadama Sosai Domin ba wanda ma yabi Ta kanta Bata Raina kanta ba sai da Yammah
Bayan Tahir ya Shigo Asibitin yana Shigowa Ɗakin Su Basma da Iya da Innaro Suka
Fice Suka barshi amma ita sai ma gyara zama Datayi kuma Abun Haushi ko Yaran bata
Ɗauka ba Daga Cikin gidansu ta leƙasu Idanuwanta na kawo ƙwallah ganin Tsabar kama
da Tahir da yaran Suke ko Mufeeda Da ƙyar ta iya gaisheta ta amsa itama ta kauda
kai saboda Nauyi Itako Hararanta kaɗai take Acikin Ranta tana Faɗin "Kin kusa bar
min gida makira.."
Bata gama Jin Nadama ba sai Dataga Tahir ya Shigo ko ɓarayin Datake bai kallah Data
gaisheshi ma Kansa na gefe ya amsa, amma yana isa kusa da Mufeeda ya saki Fuska
yana tambayanta ya Jikinta ita kuma Munafukar tana Sunne kai Numfashinta bai kusa
Ɗaukewa ba sai taga ya zauna gefen Gado ya Duƙa yana ma yaran Wasa Mufeeda kuma na
kallonsa Tana Murmushi, macen ya Ɗauko yana Faɗin "Yarinyar taso ta ɗauke ki fa
Mufee..? Ya faɗa yana kallonta.
Sunne kai tayi Tana Murmushi batace komai ba, sake kallonta yayi yana kallon
Jinjiran kafin yace "Kila yau ko gobe ku koma gida, in kun koma sai mu Shawaran
Wasu suna zasu saka musu.." Kan Mufeeda na ƙasa tace "Basai kayi Shawara dani ba
Daddy Duk Sunan da ka saka musu Dai-dai ne.." Ta faɗa tana Wasa da Hannayenta
Kallonta kawai yake yi Tausayinta na ƙara Shiganshi kaɗa kai yayi yana Faɗin
"A'ah...zamu magana in kun koma gida kema kina da Hakki yaranki ne.." Bata sake
magana ba illah Kallonsa Datake kasan Ido bataso ya Fahimci Tana kallonshi batasan
kuwa yana Kallonta ta gefen ido sai dai yayi murmushi kaɗai
Farida Dake Zaune ba tasan Sanda Ta miƙe A fusace ba tana Faɗin "Asirin mutum ya
Tonu yace Ƙaddara ne, Kuma ko kunya Yazo yana Abu goɗai goɗai, Wlh mutum bai isa ba
Zuwa za'ayi abar min gida Nida Mijina da 'ya'yana, bana son karuwancin Ƙauye.." Ta
faɗa tana Ficewa Daga Ɗakin Daga Mufeedan Har Tahir da ido Suka bita Shiko Tahir ko
Damuwa da kalamanta baiyi ba Mufeeda ce Idanuwanta Suka cika da Hawaye Tahir bai ce
mata komai ba Cikin Ranshi Dariya ce Ke Cinsa na Tunanin yadda Farida zataji in
Taji Mufeeda matarsa ce yanzu.
Haka ko akayi Washegari da Safe aka sallami Mufeeda suka koma gida kafin su Dawo
Iya da Basma Sun riga sun gyara Ɗakin na Mufeeda suna Dawowa nan suka Sauketa ita
da 'ya'yanta Aranar kuma sai ga Ashe da Tawagarta ita da Laila da Muda tazo da
kayan Wanka Goggo Abu ta bata Sakon ta kawo Itama Data Ɗauki yaran Sai da tayi
ƙwallar Tausayi da Jinjina ma Rabo, Nan ta kwana Washegari kuwa sai ga Baba Hakimi
ya iso gidan bai jima da Zuwa ba sai ga Abba da Umma suma sun iso Tunda Farida Taga
Haka Jikinta bai bata ba illai kuwa Domin Taro Aka Sake zama kamar na Farko harda
Mufeedan Shiko Baba Hakimi na Rike da Jaririn Namiji Abba na Riƙe da macen Tunda
Farida Taga an Kirata Gabanta ke Faɗuwa Tana Addu'an Allah yasa Tafiya da Mufeeda
Zasu yi ƙauye.
Bayan Buɗe Taro da sallama da Godiya Ga Allah Baba Hakimi ya Fara Magana yana Cewa
"Kowa anan yasan Abunda ya Faru Har Aka samu Waɗannan yaran Munyi Tawassali da
Sunayen Allah kuma mun yarda da Ƙaddara..Gashi Ashe Rabon bana Ɗaya bane Rabon Har
na 'ya'ya Biyu ne Hakan Kaɗai ya isa kowa yagane Ƙudurar Allah ne.." Kowa ya gyaɗa
kai banda Farida dake kallon kowa ɗai ɗai.
Cikin Dattako Hakimi ya Cigaba da Faɗin "Magana Ɗaya zanyi Zuwa biyu dama Abunda Ya
kawoni kenan, na Farko nazo ne naga Ƙaruwar Da aka samu na Biyu kuma na gabatar
muku da Hukuncin Dana yanke ko nace Wanda na Zartar nasan Wasun ku sun sani kamar
Kai Tahir da Ke Innaro Tare Da Aisha, toh ba wata Magana bace Illah Aranar da
yarinyar ta sauka Attahiru na Kirana banyi ƙasa a Gwiwa ba na Biya Sadaki aka Ɗaura
musu Aure..." Kowa maganar bata Razana Shi ba Umma da Abba da Iya Cikin Farin ciki
Suke Faɗin "Masha Allah hakan yayi Dai dai.
Farida ko Kamar Saukan Aradu Haka Taji mganar Arzane ta miƙe Hannnunta Bisa
Ƙirjinta tana Faɗin "Aure...? Mijin nawa kuka Aura mata kanbura uba..." Ta faɗa
Tana girgiza jiki, Tahir Da yaji kamar Ta Tsikara mai allura na Zagin Data ƙunduma
kafin ya Ɗauki mataki Umma ta miƙe ta Sharara mata mari tana Faɗin "Kinci Ubanki
Farida Baban Mijin naki kike cema Kan Bura uba Saboda baki da Tarbiya..?" Kuka
Farida ta Fashe Dashi Ta Duƙe tana Faɗin "Wayyo Allah na na Shiga uku ni Farida Ina
zan saka kaina kowa baya sona." Umma ta Ɗuma mata Dundu Tana Faɗin "Eh ɗin ba'a
sonki ɗin Uban waye zai soki Kina da Mugun Hali Tir Dake Farida iliminki bai miki
amfani ba.." Kuka Farida take kamar Ranta Zai Fita kowa A falon yaji Daɗin Hukuncin
Umma Barin ma Ashe da Haushin Farida ya cika mata Ciki Abba ko Kunyace Ta Hanashi
Magana Shiko Baba Hakimi mamakin Rashin ɗa'ar Farida ne ya kamashi.
Basma da Bassam Dake gefe ko Ajikinsu basu damu da Kukan Da Farida keyi ba sai ma
murnan Da Suke Daddynsu ya auri Mufeeda Zasu Dinga ganin Twince dama Fargabansu kar
a ɗauke musu su suna sonsu sosai kuma suna son zama da ita.
Mufeeda kuwa kanta na Duƙe Tana Share hawaye Wai Abun Mamaki itace matar Daddy,
Lalle Allah mai yarda yaso amma Maganar gaskiya ba' ajinta bane ya Fita komai da
komai, Ta Daɗe tana Fatan Allah ya bata Miji Irin Daddy koda bai kaisa ba koda
Rabinsa ne sai gashi shi ɗin Allah ya mallaka mata, Babu Abunda Zatama su Baba
Hakimi sai godiya Domin Sun inganta Rayuwarta.
Hakimi ne ya Kaɗa kai yana Faɗin "Banzaci Haka Daga gareki ba Farida..Assha Abun
bai min Daɗi ba..Karki manta Mufeeda yanzu amana take garemu, Tun mahaifiyarta na
Raye take ƙarƙashin Ikon mu kuma in bai Aureta ba Alhalin Shi ya ɓata mata Rayuwa
Wa kikeso ta Aura ga 'ya'ya baki Tunanin Watarana agoranta musu..? Saboda Haka
Tahir shine Rufin Asirin Mufeeda Itama Shine Rufin Asirinta ina Fatan zaku zauna
lafiya da Junanku Ku Rungumi ƙaddaranku Tunda Haka Allah ya Tsara muku.." Ko ɗago
kai Farida batayi ba sai Gunjin kuka take Baba Hakimi bai Damu ba Illah maida
kallansa Da yayi kan Mufeeda yana Faɗin "Kiyi Haƙuri Mufeeda kiyi ma Mijinki
biyayyah kuma ki kula da 'ya'yanki na Tabbata Attahiru bazai barki kiyi Kukan
Maraici ba.." Mufeeda kanta na ƙasa Tana Share Ƙwallah tace "Bakomai Ranka ya
Daɗe...Bani da Bakin da zan mika godiyata zuwa gareku..Tun Mahaifiyata nada Rai
kuke Jin ƙaina kuna Wahala dani, Daddy ya ingata Rayuwata ya Wahala dani ya
Tarbiyantar dani kamar 'yar daya Haifa na yarda Ƙaddara ne ya Faɗa mana Babu Abunda
zan ce muku Sai Fatan Gamawa da Duniya lafiya, Allah ya saka muku da Gidan Aljannah
Firdausi.." Ta faɗa tana kuka Sosai kowa Afalon sai da kalaman Mufeesda ya Sakashi
kwallah Shi kanshi kafeta da Ido yayi yana Jinjina ma Kaifin Tunanin Mufeeda Kukan
kuwa kara Narkamai da Zuciya yake.
Baba Hakimi ya Jinjina kai yana Faɗin "Ameen Ameen...Allah yayi muku
albarka...Allah ya albarkaci Aurenku ya kuma baku zaman lafiya.." Yake Faɗa yana
Share Siririyar ƙwallar Data Zubo mai, Abba ne yayi gyaran Murya yana Faɗin "Masha
Allah...Allah ya bada zaman lafiya Haƙiƙa Mansur kayi Tunani mai kyau Allah ya
sanya alheri.."
Kowa ya amsa da Ameen Baba Hakimi ne ya kalli Tahir yana Faɗin "Ka sanya musu
suna..?" Kai ya gyaɗa kafin yace "Eh jiya da Daddare nayi ma Namijin Huɗuba da
Sunanka macen kuma na mata Huɗuba da Sunan mahaifiyar Mufeeda.." Kowa ya Washe baki
yana Faɗin Masha Allah Mufeeda kuwa Ɗagowa tayi tana kallon Tahir Lokaci Ɗaya Tana
Kuka tana Dariyar Farin ciki Shima Murmushin ya sakar mata.
Baba Hakimi yace "Kai...kai Naji Daɗi sosai nagode..Allah ya Raya Mansur da
Hulairatu.." Kowa ya karɓa da Ameen kafin ya cigaba da Faɗin "In zaku yi taron
Sunanku Ku haɗashi duka da Tarewar Mufeeda Tunda Duka gida ne, Bana son Bidi'a
Komai kuyi shi Lokaci Ɗaya.." Ashe tace "Insha Allahu Baba Dama munyi magana da
Yaya Tahir In Sati ya Zagayo za'a Yi Taron Suna sai A haɗa da Tarewarsa Allah ya
basu zaman lafiya.."
Ta faɗa tana makama Farida Harara Wacce tabar kuka sai ajiyar Zuciya, babu wanda ma
ya ƙara bi takan Farida aka Rufe Taro da Addu'a Baba Hakimi ya miƙama Innaro
Takawaranshi Shi kuma Abba ya miƙawa Iya mai sunan Inna Fulera suka Fita Waje,
Farida kuwa Umma ta jata ɗaki ta Zaunar da Ita tana Faɗin "Farida..Farida.Farida..!
Ta faɗa tana kallonta Cikin Muryan Ɓacin Rai tace "Farida Sau nawa na kiraki..?" Ta
faɗa tana Murɗe mata kunne Cikin Hawaye tace "Sau uku Umma.." Sakin mata kunne Tayi
tana Faɗin "Kinga Duk Abunda ya Faru ko..? Kinji kuma kin gani yadda kika zama bora
banza a idon Mijinki da 'ya'yanki harda Dangin Mijinki...ko..?" Kai Farida Ta gyaɗa
tana Kuka sosai Umma tace "Toh ya rage naki ki Zauna kima kanki karatun ta natsu In
ba Haka ba Wlh Tallahi Tahir zai koreki Daga gidan nan Kina ji kina gani yarinya
ƙarama ta ƙwace miki miji Tunda kin zama Sakarya Kina sane yanzu ba Da bane Wlh
Tahir bazai ƙara Ɗaukan Abun da ya Ɗauka abaya ba, Ya Rage naki Farida Ki gyara
Rayuwarki da Halayyarki in ba Haka ba Wlh Zaki Kwashi Nadaman Dayafi Wanda kike
karɓa yanzu, Daga ƙarshe ina Fatan Allah ya Sausauta Zuciyarki ya Kori Sheɗan
acikin Rayuwarki." Ta faɗa tana miƙewa kafin tace "Zamu Tafi..Sai an kwana biyu
ƙila nazo Ranar Tariyan, Don Allah Farida ki maida komai ba komai ba, ki nemi
Gafaran Mijinki ki kuma Rungumi 'ya'yanki Da Mufeeda Ko kimarki ta Dawo don Allah
ba domin Halina ba..." Ta faɗa Tana Haɗa Hannuwanta Waje Ɗaya.
Farida ta miƙe ta Rungume Umma tana kuka take Faɗin "Insha Allahu Ummah naji
maganarki...Nayi miki alƙawarin Zan Chanza Halina Umma zan Nemi gafaran Tahir dashi
da Mufeeda Umma, Na gane kuma na Fahimta Duk Abunda ya Faru laifina ne.." Rungumeta
Umma Tayi tana Bubbuga bayanta take Faɗin "Naji Daɗin Haka Allah yayi miki
albarka.."
Ta faɗa tana Share mata ƙwallah, Har Falo ta Rakota Ta Shiga wajensu Innaro ta musu
sallama ta Fice Haraban gidan inda Abba ke Jiranta Daga nan suka ma Tahir sallama
suka Tafi, Baba Hakimi ko Tuni Garzali ya Miƙa Dashi Farida kuwa ɗaki ta koma tana
kuka Cikin Zuciyarta tana Fatan Allah ya bata ƙarfin Gwiwan Gyara Rayuwarta.
*Anitha...*
*Aisha Alto..*
*NANNY..!*
_(Mai Reno..)_
*Alkaluman:*✍️
*AISHA ALTO*💞
*JAMILA UMAR(Janafty)*💕
Sai da Farida taci uban kukanta ta gode Allah, sannan ta share hawayenta ta miƙe
jiki a sanyaye ta shiga toilet tayo wanka ta fito ko mai bata tsaya shafawa ba ta
zira doguwar rigar atamfa a jikinta ta zauna a bakin gado ta zabga tagumi ta
tsurawa guri guda idanu tana saƙe saƙe a zuciyarta.
Bayan sallar Isha'i Tahir ya shigo gidan, tana jin motsin shigowarsa ta miƙe a
sanyaye ta ɗauki hijabinta ta fice ta nufi ɗakinsa, yana ƙoƙarin shiga toilet ta
shigo, kallo ɗaya yayi mata kawai ya ɗauke kansa gefe ya buɗe ƙofar toilet ɗin zai
shige abinsa, da sauri ta isa gabansa ta riƙo hannunsa ƙwallah na taruwa a cikin
idanunta ta marairaice gwanin tausayi tace "Don Allah don sonka da Annabin rahama
kayi haƙuri kazo muje ɗakin Mufeeda...Akwai maganar sa nakeso nayi daku ne
dukkanku...Don girman Allah Abban Basma kar kace a'a..." Ta faɗa da magiya ƙwallah
na gangarowa daga cikin idanunta suna zubowa kan fuskarta, tsam yayi kawai ya tsura
mata ido yana kallonta kamar ba zai je ba, can sai ya janye hannunsa a nata ya raɓa
ta gefenta ya nufi ƙofa, da sauri tabi bayansa suka fice suka nufi ɗakin Mufeeda.
Suna shiga suka iske su Innaro da Iya dasu Basma da Bassam a ɗakin tare da Mufeedan
suna hira, a hankali ta taka ta shiga tsakiyar ɗakin ta tsaya agaban Tahir daya
tsaya ya zuba mata ido yana kallonta yayinda gaba ɗaya su Iya da Innaro dasu Basma
suma suka zuba mata ido suna kallonta, a hankali ta durƙusa a gaban Tahir ta zube
gwiwoyinta a ƙasa hawaye na zubo mata ta duƙar da kai cikin rawar murya tace "Don
Allah don Annabi don girman Allah...Kayi haƙuri ka yafe min na tuba..Ka yafe min
duka laifin dana aikata, bazan sake ba, na yarda nayi kuskure kuma zan gyara
halayena..." Ta faɗa tare da fashewa da kuka, a hankali yace "Na yafe miki...Allah
ya yafe mana baki ɗaya.." Wani sanyin daɗi taji ya ziyarci zuciyarta har sai da ta
saki ƙaramin murmushi ta juya tana share hawayen fuskarta ta matsa gaban Mufeeda
dake zaune ta duƙar da kanta tana wasa da farcenta, a hankali Farida ta riƙo
hannunta tana kallon cikin idanunta take faɗin "Nasan nayi miki abubuwa da dama
waɗanda bazasu lissafu ba Mufeeda..amma karki dubi munin abunda nayi miki ki dubi
girman alkhairina agareki ki yafe min kuskurena..nasan na cutar dake sakacina ya
jefaki cikin wani yanayi, na cuci rayuwarki...Kuka ya hanata ƙarasawa. Da sauri
Mufeeda ta faɗa jikinta itama ta fashe da kuka tana faɗin "Bakiyi min komai ba
Momy..kuma duk abunda ya faru dani daga Allah ne dama dole sai ya faru dani ban isa
na kauce masa ba, kuma na ɗauki hakan a matsayin ƙaddarata, don haka ki daina cewa
na yafe miki bakiyi min komai ba, nice ma zan roƙeki yafiya...Don Allah ki yafe
min, kuma duk abunda kika yi min wanda na sani da wanda ma ban sani ba duka na yafe
miki..." Ta faɗa tana ƙara ƙanƙame Faridan a jikinta, ƙara rungumeta Faridan tayi
itama suna sharɓan kuka, Tahir dai na tsaye yana kallonsu jikinsa duk yayi sanyi, a
hankali Farida ta janye Mufeeda a jikinta ta durƙusa agaban Iya itama ta roƙeta ta
yafe mata sannan ta durƙusa agaban Innaro itama ta yafe mata sannan Basma da Bassam
suma duk suka yafe mata. Nan take taji ta fayau zuciyarta tayi mata wasai taji
kanta kamar an sauke mata wasu tulin kaya.
Haka a ɓangaren Tahir yaji daɗin abunda Faridan tayi sosai a ransa har hakan ya
nuna a fuskarsa kuma yana fatan Allah yasa hakan ya zama gaskiya har a zuciyarta
tayi tuban ba tuban muzuru ba.
Miƙewa tayi a hankali ta ƙarasa inda gadon jariran yake inda suke ciki a kwance luf
abinsu ta tsaya tana murmushi ƙwallah na taruwa a cikin idanunta ta buɗe ta ɗauko
macen ta riƙe sannan ta ɗauki namijin shima ta haɗasu ta rungume a jikinta tana
jijjigasu kafin kuma ta cirosu daga jikinta ta tsura musu ido tana kallonsu har
bata san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba, ƙarasa tayi gaban Tahir da fara'a a
fuskarta tana faɗin "Abban Basma zoka gani, wallahi yaran nan tamkar Basma da
Bassam lokacin dana haifesu suna jarirai.." Ta faɗa tana ƙarasawa gabansa, yana
dariya ya karɓi namijin a hannunta yana kallonsa yace "Wallahi haka nace nima.."
Innaro tace "Nima dai haka nace.."
Tahir yana murmushi yace "Ai kamarsu da 'yan uwansu ce ta fito sosai." Ya faɗa
yana miƙa mata yaron. Karɓarsa tayi ta miƙa masa macen tana faɗin "Yanzu da wane
suna za'a dinga kiransu kenan..?" Ta faɗa tana kallonsa, yana dariya yace "Mufeeda
wane suna za'a dinga ce musu..?" Ƙara sunkuyar da kanta ƙasa tayi cike da kunya
tana faɗin "Duk abunda kuka zaɓa yayi Momy.." Ta faɗa tana murmushi. Farida tace
"To shikenan, namijin zamu dinga kiransa da Ayman macen kuma mu ce mata Airah.." Da
murna Basma tace "Yauwa Momy...Wallahi sunan yayi mana daɗi sosai..kuma ya dace
dasu..Allah ya raya mana ƙannen mu.." Da Ameen duk suka amsa, kafin daga nan suka
shiga hirar yanda taron suna da bikin tariyar zata kasance, kowa ka gani fuskarsa
cike da fara'a da farin ciki take, har ta su Basma da Bassam ma walwalarsu ta ƙaru
a wannan daren, sai farin ciki da annashuwa suke.
Sun daɗe sosai a ɗakin suna hira har ƙarfe 10:30pm kafin Tahir da Farida sukama su
Innaro da Iya da ita kanta Mufeedan data fara barci sallama suka fice tare dasu
Basma da Bassam kowa ya shige ɗakinsa bayan sun musu sallama suma, suka nufi
bedroom ɗin Tahir.
A hankali ya fara shafa bayanta alamar lallashi yana hura mata iskar bakinsa a
cikin kunnenta cike da wani irin salo mai tafiyar da ruhi haɗe da zuciya mai ƙara
azalzala wutar ƙauna, ƙara shigewa jikinsa tayi ta lafe tana karɓar saƙonsa, a
hankali ya fara tafiya da ita zuwa gurin gadon dake ɗakin tana jikinsa a narke tana
shaƙar daddaɗan ƙamshin turarensa mai sanyaya zuciya, a haka suka isa gaban gadon,
cike da shauki ya ɗagata cak ya ɗorata a saman gadon ya kwantar da ita flat, sannan
ya hau kai shima bayan ya zare rigar shadda dake jikinsa yayi saura daga shi sai
dogon wandon kayan.
Wani irin shauki da tsantsar soyayyar mijinta Farida taji tana ƙara kamata, tana
daga kwancen tana kallonsa ya hayo saman gadon ya fara ƙoƙarin zare mata rigar
jikinta, wani irin daɗi da farin ciki mara misaltuwa Farida taji sun kamata lokaci
ɗaya daɗi ya baibayeta ta ɗago ta faɗa jikinsa tana ji a ranta yau zata gwada masa
tsantsar ƙauna wacce bata taɓa nuna masa ba, zata nuna masa tsabtatacciyar ƙauna
mara iyaka wacce babu algus a cikinta, zata sa yayi alfahari da ita ta tsaya a
ransa ya kasa gogeta a zuciyarsa. Cike da salo ta jawo makunnin wuta ta kashe wutar
ɗakin, ɗakin yayi duhu kaɗan ta miƙe ta sauka daga kan gadon ta cire rigar da kanta
yayi saura daga ita sai pant da bra suma a hankali ta zaresu ta koma saman gadon ta
haye jikin Tahir dake zaune mamaki ya gama cikasa ya zuba mata ido kawai yana
kallonta, ganin irin kallon da yake mata mai cike da mamaki yasa ta ƙara zagewa ta
jawosa jikinta ta haye saman cinyarsa a hankali ta fara shafo fuskarsa zuwa leɓensa
da wani irin salo kafin ta ɗago haɓarsa tana kallon cikin ƙwayar idanunsa ta haɗa
bakinsa da nata, wani irin lumshe idanu Tahir yayi cike da jin daɗi ya ƙara matso
da ita jikinsa sosai ya kamo tattausan harshenta ya fara mata wani irin tsotsa mai
tayar da hankali dasa mutum mantar dashi kansa waye.
Sake zagewa Farida tayi sosai ta kamo harshensa ta shiga aika masa da wani
lafiyayyen kiss mai kashe jiki da zuciya, Tana yi tana shafar sumar kansa tana tura
yatsunta ciki tana masa wani irin salo kamar tafiyar tsutsa, a haka ta sauka har
kan gadon bayansa tana shafa bayan tana masa tafiyar tsutsa kamar tana masa susa,
idan ta ja har tsakiyar bayansa sai ya gantsare ta dawo da hannunta sama tana shafo
ƙeyarsa, in banda sauke numfashi da gurnani babu abunda Tahir ke yi, hakan ya ƙara
mata ƙwarin gwiwa ta zage sosai ta dage ta shiga nuna masa tsantsar ƙauna mai cike
da nuna tattali da tsantsar so mai tsayawa a zuciya.
Duk wani salo mai kashe zuciya da saka rai cikin tsantsar buƙatuwa, sai da Farida
tayi amfani dasu gurin kashe jikin Tahir ta mantar dashi kowa da komai a wannan
dare, ta zage ta nuna masa cikakkiyar kulawa da tattali.
Wani al'ajabi da mamakin Farida ne ya kama Tahir, sagale ya tsaya kawai yana
kallonta a ransa yana tambayar kansa dama kenan ta iya komai take tsaya masa kamar
gunki ta barsa yayi kiɗinsa yayi rawarsa? Ko ta nuna masa bata son komai da yake
mata ita ta gaji bata iya ɗaukar lalurarsa? Lallai Farida yau ta bashi matuƙar
mamaki, kuma yaji kimarta da darajarta sun fara dawowa a zuciyarsa.
Sosai Farida ta zage ta kafa tarihi mai tsayawa a zuciyar Tahir a wannan dare, tayi
duk abunda tasan zai faranta ransa ya manta da komai da kowa sai ita. A ɓangaren
Tahir kuwa shima tsayawa yayi tsam ya nuna mata tsantsar kulawa mai dasa farin ciki
mara gushewa da walwala mai matuƙar tasiri a zuciyar duk wasu ma'aurata masu so da
ƙaunar junansu.
Washegari da sassafe Farida ta tashi bayan sunyi wanka da Asuba sunyi sallah Tahir
ya koma barci ta fice ta nufi ɗakin Mufeeda, lokacin ko tashi Mufeedan bata yi ba
tana ta sharar barci abinta, sai Innaro dake zaune akan darduma tana lazumi Iya
kuma na kichen zata dafa ruwan wanka, bayan sun gaisa da Innaro ne ta fice taje ta
haɗo ruwan zafi a babban robar wanka, Innaro tace ta bari za suyi musu wankan taje
ta kula da mijinta, amma Farida tace A'a su bari ita zata wanke 'ya'yanta tas. Haka
kuwa akayi ta ɗauko jariran a cikin gadonsu ta fara yiwa Ayman sannan ta yiwa Airah
itama, ta shiryasu tsab cikin lafiyayyun kayan sanyinsu masu kyau da tsada, Innaro
na zaune tana kallonta gwanin sha'awa. Sai data gama musu sannan ta fesa musu
turare mai sanyin ƙamshi ta sakasu a cikin shawul ta miƙawa Innaro su sannan ta
miƙe ta ɗauke robar ta kai Toilet d'in Mufeeda ta zubar da ruwan ciki, sannan ta
sake haɗawa Mufeeda ruwan wankan itama ta fito ta tasheta, ta cire kayanta suka
shiga toilet. Farida Ita ta taimakawa Mufeeda tayi mata wankan jego tsab ta gasata
sosai Mufeedan sai sunkuyar da kai take tana jin kunya amma ita Farida ko a jikinta
ta zage ta gyarata tas ta rufa mata babban tawul suka fito..Suna fitowa ta zaunar
da ita a bakin gado ta ɗauko mai ta bata ta shafa kafin ta buɗe akwatinta ta ciro
mata wata atamfa riga da zani ta ajiye mata, ta koma ta ɗauko humra da kulacca da
Innaro tazo mata dasu ta bata ta shasshafa a jikinta sannan ta saka kayan ta zauna
ita kuma Farida ta fita. Bata jima da fita ba ta dawo ɗauke da babban kofi da kayan
tea a hannunta, Mufeeda dai sai binta da kallo kawai take tana jin tsananin farin
ciki a ranta, Farida kuwa tana jin bala'in kishin Mufeeda a ranta amma tana dannewa
kada a gane, a haka ta haɗa mata tea mai kauri ta miƙa mata ta tura mata bread da
filet ɗin soyayyen kwai ta tasata gaba sai da taci tayi dam zufa sai keto mata
take, haɗa kayan Farida tayi ta fitar dasu ta kai kichen sannan ta dawo ta haɗa
kayan da Mufeedan ta cire da waɗanda ta cirewa jariran ta fita dasu can bayan gidan
ta wankesu tsab ta shanya sannan ta dawo lokacin ƙarfe 8:20am tace Mufeedan ta koma
ta kwanta ta huta bari taje su gama haɗa breakfast da Iya, Innaro ta amsa tana sa
mata albarka ta fita a ɗakin ta nufi kichen.
Lallai Farida ta sauya sosai kuma duk wanda ya santa a ranar ya ganta dole zai gane
hakan, Iya ma sai kallonta take suna aiki, tare suka gama haɗa komai suka jera a
dinning table kafin ta nufi bedroom, tana shiga ta samu Tahir ya tashi yana Toilet
yana wanka. Tuɓe kayan jikinta tayi itama ta shige toilet d'in don suyi wankan
tare.
Mintuna talatin suka ɗauka a toilet d'in sannan suka fito ɗaure da tawul a jikinsu
suna rungume da juna suna dariya, ita ta shafa masa mai ta shiryashi tsab sannan
shima ya tayata ta shirya ta feshesu da turarensa mai daɗi da sanyaya zuciya ta
ɗauko hularsa zanna bukar ta kafa masa yayi kyau sosai tana kallonsa tana jin wani
kishi na taso mata tayi saurin kawar dashi ta riƙo hannunsa tana murzawa a nata
cikin kwantar da murya ta fara faɗin "Abban Basma ya kamata fa a siyo kayayyakin da
Mufeeda zata saka tunda tare za'a haɗa da taron suna da fitar biki..." Ta faɗa tana
sumbatar tsakiyar tafin hannunsa, lumshe idonsa yayi ya kamota jikinsa yana faɗin
"To shikenan, zan turo miki kuɗi ta account ɗinki sai ku sayi abunda ya dace.." Ya
faɗa yana sakar mata kiss a goshinta, tana murmushi ta kama hannunsa suka fice daga
ɗakin suka sauka ƙasa.
Sai da suka shiga ɗakin Mufeeda ya dubasu ita da yara suna ta barci suka gaisa da
Innaro da Iya dake shirya Naila kafin suka fice bayan Farida ta ɗauki Naila tace su
Innaro su fito Dinning suci abinci, suna fitowa daga ɗakin suka samu Basma da
Bassam sun fito daga ɗakinsu wanda da alama sun shiga su gaishesu ne basu samesu
ba, da murna suka nufesu suka faɗa jikinsu, Tahir ya ɗago Basma daga jikinsa yana
murmushi yake faɗin "Karki kayar da Daddy mana..ko bakisan kin girma bane..?" Ya
faɗa yana jan kumatunta, turo baki tayi ta duƙa ta gaisheshi ya amsa cikin sakin
fuska tare da shafa kanta, sannan ta juya ta gaishe da Farida dake kallonsu tana
murmushin jin daɗin gyara rayuwarta da tayi, shima Bassam ya gaishesu kafin Tahir
ya kama hannunsu yace suje Dinning su karya, da sauri Basma ta zame hannunta tana
faɗin "Zanje na ga ƙannena da Aunty Mufeey tunkunna Daddy.." Ta faɗa tare da
ƙoƙarin rugawa da gudu, saurin kamota Farida tayi tana harararta tace "To barci
suke yi..baza kije ki tashesu ba.." Ta faɗa tana nufar dinning, ba don Basma taso
ba tabi bayanta tana turo baki, Tahir dai na kallonsu yana murmushi bai ce komai
ba.
Sai da suka gama karyawa sannan Farida ta rakashi harabar gidan ya shiga mota
Garzali yaja har suka fice tana ɗaga masa hannu kafin ta koma cikin gida ta shiga
bedroom ɗinsa ta gyarashi tsab ta fesa room freshener mai ƙamshi ta saka turaren
wuta mai daɗi ta janyo ƙofar ɗakin ta fice..tana saukowa taji alert ya shigo
wayarta tana dubawa taga transfern kuɗi ne masu yawa Tahir yayo mata tana murmushi
ta nufi ɗakin Mufeeda tace Innaro ta shirya zasu fita kasuwa.
Haka kuwa akayi ita da Innaro suka je kasuwa ta narkowa Mufeeda siyayya sosai ita
da jariranta ta haɗo musu kaya masu kyau da tsada, a nan kasuwar ta samu haɗaɗɗen
shagon ɗinki ta bada kayan Mufeeda ta zaɓar mata ɗinkuna masu kyau da ɗaukar
hankali, bayan ta biya kuɗin ya faɗa mata ranar da zata zo karɓa suka dawo gida.
Duk waɗannan abubuwan da Farida take yi kawai tana daurewa ne don tayi alƙawarin ta
gyara halayenta, bazata ƙara yin abunda tasan zai sa wani yaga baƙinta ba balle
mijinta da iyayenta da 'ya'yanta su tsaneta su dinga jin haushinta ba, saboda haka
ma duk wasu ƙawayen banza tayi watsi dasu ta daina bi ta kansu, yanzu ta gyara
rayuwarta zata tsaya ta kula da mijinta da 'ya'yanta.
Bayan kwana biyu da haihuwa Goggo Abu tazo duba Mufeeda da yaran taji daɗin yanda
ta ga Farida ta koma ta saki jikinta tana ta kula da Mufeeda da yaranta nan ta
tarasu tayi musu nasiha sosai mai ratsa jiki da zuciya.
Ana gobe taron suna da yamma Farida ta ɗauki Mufeeda suka tafi cikin gari ta kaita
wani haɗaɗɗen Saloon inda take zuwa aka tsantsara mata ƙunshi da kitso ta biya
kuɗin suka dawo gida. Suna zuwa suka tarda Ashe dasu Muda da Laila sun zo, nan Ashe
tayi ta yaba kyaun da Mufeedan tayi, ita dai Farida sai dai tayi dariyar yaƙe kawai
tana ƙoƙarin danne abun data ji yana taso mata.
Washegari tunda sassafe Zahra matar Ishaq da 'ya'yanta suka zo. Nan suka haɗu dasu
Innaro da Iya da Farida da Ashe suka shiga aiki baji ba gani, don ba wani taro
za'ayi sosai ba, iya yasu yasu ne kawai suka cika gidan.
Farida da kanta ta kira mai kwalliya tazo har gida ta tsantsarawa Mufeeda kwalliyar
data ƙara fito da ita tayi kyau sosai, ta ɗauko mata wani haɗaɗɗen leshi blue mai
adon stones cikin waɗanda aka ɗinko mata ta bata ta saka tayi cacas a ciki, nan
kyaun Mufeeda ya ƙara fitowa sosai ita da kanta Farida sai da ta kalleta ta ƙara
kallonta don gani take kamar ba Mufeedan data sani bace a gabanta, Farida da kanta
tayi mata lafiyayyen ɗaurin ɗankwalin daya sake fito da kyawun fuskarta tayi fayau
abinta sai ɗaukar ido take tana ƙyalli. Haka jariran suma expensive kaya aka saka
musu haɗaɗɗu masu kyau da tsada sai ƙamshi suke suna walwali abinsu, Basma da
Bassam ma da Naila sunyi gayu abinsu sun sha kyau suna rungume da ƙannensu Ayman da
Airah sun hana kowa ɗaukarsu sai dai ka gansu a hannayensu duk inda sukai dasu
Naila na nan nane dasu itama.
Taro yayi taro an gama lafiya an tashi lafiya, sai dare Ishaq yazo ya ɗauki Zahra
da 'ya'yansa bayan Farida ta haɗa musu kayan suna cike da leda ta rakasu har gurin
mota sukayi sallama ta koma cikin gida, don yau duk a gajiye take ko hirar dare da
suka saba yi a ɗakin Mufeeda bazata tsaya yau ayi da ita ba, wanka kawai zatayi ta
haye gado kafin kuma uban gayyar shima ya dawo.
Washegari Ashe dasu Muda da Laila suka koma Ɗanbatta suma, nan Innaro da Farida da
Iya suka cigaba da kula da Mufeeda da yaranta, Basma da Bassam kuwa indai suna gida
kullum suna nan liƙe da ƙannensu haka Naila sai tasa rigima itama sai ta ɗaukesu.
Wannan kulawar da Farida ta gani kowa na ba Mufeeda shiya ƙara saka mata kwaɗayin
son taga ta sake haihuwa itama, don taga duk wata kulawar Tahir da tattalinshi ya
ɗorasu duka ne akan Mufeeda da 'ya'yanta.
Ranar da Mufeeda tayi arba'in a ranar Innaro tace bazata ƙara kwana a Kaduna ba,
itama Ɗanbatta zata koma, haka kuwa akayi Tahir da Farida suka haɗa mata sha tara
ta arziki da kaya niki niki Garzali ya maidata.
*Anitha...*
*Aisha Alto...*
*NANNY...!*
(Mai Reno..)
✍🏻
*Alƙaluman:*
*AISHA ALTO💞*
*JAMILA UMAR (Janafty💕*
Ranar da Innaro ta tafi Farida ta samu Mufeeda a cikin Ɗakinta tana bama Ayman Nono
Domin shiyafi Airah rigima, Gefenta ta Zauna Tana Faɗin "Kina nan Ashe..? Ina Airah
take ne..?
Mufeeda tace "Wlh Ayman ya tashi Da Rigima ni nagaji da Tsotsan nan nashi Momy.."
Hararanta tayi kafin tace "Kin me..? Lallai Awo ki Yarinya don sai sun Shekara 2
zaki yayemin yara.." Shagwaɓe Fuska tayi tana Faɗin "Kai Momy.."
Bata bi ta kanta ba ta fara faɗin "Kinsan Abunda Nake so Dake..? Mufeeda ta girgiza
kai Farida ta cigaba da Faɗin "Yau zaki karɓi girki ma'ana Yau kece keda Abban
Basma.." Ido Mufeeda ta Zaro gabanta na Faɗuwa Kallonta Farida tayi tana Faɗin "Eh
Sai ki Shirya, yanzu tashi zakiyi mu shiga Kichen tare muyi Dinner, kinga ya kamata
ace mun gyara komai bai dace ace yana da mata har guda biyu ba amma ace kullum Sai
dai Iya ta girka ta bashi yaci ba sai na yanke Shawaran Duk wacce keda miji Ranar
toh zamu Shiga kichen tare mu taimakama juna ko ya kika gani..?
Mufeeda ta Sadda kai ƙasa Tana Faɗin "Duk Abunda kika yanke Dai-dai ne Momy.."
Kafaɗarta ta Dafa tana Faɗin "A'a karki ce Haka kema fa matar gidan nan ce kina da
Hakki kan komai.." Mufeeda batayi magana ba Farida ta cigaba da Faɗin "Iya zata shi
ci gaba da taimaka mana wajen kula da Airah da dai Sauransu.." Kai Mufeeda ta gyaɗa
tana Faɗin "Hakan yayi Momy.." Sun daɗe suna hira kafin Ayman ya gama shan Nono
Farida ta ɗaukeshi su Fito Falo, Su miƙawa Iya wacce ke goye da Airah tayi barci an
samu 'yar Rigima Naila an tafi islamiya, Farida ce ta miƙa ma Iya Ayman ta faɗa
mata Shawaran da suka yanke taji Daɗi sosai, Ko babu komai yanzu Tahir zai Fara
Ɗanɗanan daɗin Aure.
Farida da Mufeeda Haka suka Zage suka Shiga Sukayi girki mai rai da lafiya, Tuwon
Shinkafa suka yi miyar Agushi saboda Tahir yana bala'in son Tuwo ga miyar taji man
Shanu da naman rago zuƙu-zuƙu, Zobo suka haɗa suka sanyashi cikin Fridge, Dai-dai
Dawowarsu Basma Daga Makaranta suka gama komai har gyara kichen ɗin Farida ta Fita
ta bar Mufeeda na wanke wanke Abun da suka ɓata, Su kansu yaran sunyi matuƙar
mamaki ganin Duka iyayen nasu acikin kichen suma sun Nuna murnansu suna tsalle Cewa
yau zasu ci girkin Momy dana Aunty Mufeeda.
Farida ta matsama Mufeeda taje tayi wanka itama Sama ta Haura ta Shiga wankan,
Bayan ta Fito tayi sallar Magriba ta Shirya cikin wani ubansun Leshi Riga da zani
batayi kwalliya ba amma Tayi kyau sosai Tana Fesa Turare taji Ihun yaran suna Faɗin
Daddy oyoyo Murmushi tayi tana Ƙoƙarin Ɓoye Abunda ke Taso mata acikin ƙasan Ranta
ta Fito Tun daga saman Steps d'in yake kallonta yana Riƙe da Naila harta ƙaraso
tana Faɗin "Sannu da zuwa Abban Basma.."
Murmushi ya sakar mata yana Faɗin "Yauwa Umm Airah ko..? 'yar Dariya tayi Briefcase
ɗinsa ya Miƙa mata ta maƙale kafaɗa tana Faɗin "Yau bani keda kai ba Mufeeda ce.."
Duk da acikin Ranshi yaji daɗi domin wajen Wata goma kenan yana Fatan sake komawa
wannan ƙorama amma sai bai nuna ba yawani Ware ido yana Faɗin "Bangane ba..? Baki
ta murguɗa mai tana Faɗin "Baka gane ba ko..? Zaka gane anjima.." Dariya yayi yana
kallonta saboda yarda tayi magana su Basma kuwa Tuni sun Wuce ɗakunansu, Farida ce
ta Ɗaga Murya tana Faɗin "Mufee...Wai me kikeyi ne Haka bakiji Shigowar Megidan
naki bane...? Ta faɗa tana Murmushi..
Mufeeda Dake laɓe Tun Ɗazu ta kasa Fitowa saboda kunya ta Fito kanta Sunkuye tana
Faɗin "Gani Momy sallah na idar..." Ajiyar Zuciya Tahir ya sauke yana kallonta ƙasa
ƙasa Tana Sanye cikin Riga da Siket na wata atamfa wanda yasan Mufeeda abaya ba
wanda zai ce itace yanzu domin Mufeeda yanzu haihuwa da Namiji Sun Buɗata tayi kiɓa
kamar ba ita ba hips da nonuwa kuwa sun cika ko'ina, ƙarasowan tayi ta ranƙwafa
tana faɗin "Sannu da zuwa Daddy." Amsawa yayi yana kallon Fuskarta ido cikin ido
Farida Dataga Haka sai ta wuce kichen tana Faɗin "Ki bishi Sama ki Taimaka mai yayi
wanka Mufee, kafin ku Fito na Shirya Tebur.." Ta faɗa tana Shigewa kichen da Sauri
kamar zata faɗi Domin bazata iya jurar irin wannan kallon Sha'awan da Tahir ke bin
Mufeeda dashi ba.
Ganin ta tsaya tana Wasa da Hannunta yasa kawai ya juya ya fara Haura step Naila
kuma Tun ɗazu ta sauka Daga hannunsa tabi Basma Ɗakinta cikin Sanyi jiki tabi
bayansa yana jin takunta ya mata banza Har Suka Shiga bedroom ɗinsa, ko kallonta
baiyi ba ya ijiye Jakar Briecafe ɗinsa da wayarsa ya Buɗe Ƙofar Toilet ya Shiga
Haushinsa Ɗaya da Mufeeda Yadda komai wai sai Farida tace mata tayi Zatayi alhalin
yana da tabbacin Daga Iya har Innaro basu barta Haka ba.
Kuma yayi gaskiya domin Innaro ta mata nasihan ta kuma ta bata wasu Shawarwarin,
ƙara zama da Miji, Harda gyaran Jego Haka Innaro ta Tiƙe ta ma Mufeeda, kayan
lambun nan Duk matsa mata take tana Sha Tsarki da ruwan zafi mai bagaruwa, shan
madara da Zuma, kuma kafin ta tafi ta tarasu ita da Farida ta sake musu nasihan
Zama lafiya, Amma Duk mufeeda tayi biris tana jiran komai sai Farida tace tayi kana
zata Da Haushin Abun ya gama wanka ya Ɗauro alwala ya Fito Kansa Ɗaure da karamin
Towel yana goge kansa Jikinsa kuma sanye da wani baƙin dogon wando Tana nan tsaye
inda ya barta yana ganin Haka yace "Kinga ki Tafi kawai Nagode.." faɗin haka da
yayi yasa ta Ɗago kanta suka Haɗa ido saurin kauda kai tayi ganin Ƙirjinsa yana
waje ga gashi Duk ya kwanta cikin kasala ta ƙarasa kusa dashi tana Faɗin "Kayi
haƙuri Daddy..."
Kallonta yayi yana Faɗin "Baki man komai ba Mufeeda Abu Ɗaya nake so ki gane yadda
nake Mijin Farida haka kema nake Mijinki.." Gyaɗa kai tayi kanta na ƙasa tace
"Bazan ƙara ba.." Ta faɗa Muryanta na rawa ganin Haka yasa ya Riƙo kafaɗunta yana
Faɗin "Meye Abun kuka..? Kinga Zauna na gama Shiryawa mu sauka tare.." Ya faɗa yana
Zaunar da ita Kan gado shi kuma ya juya yana neman kayan da zai saka Wasu Riga da
wando ya saka ƙirar Armani ya Taje kansa sai gashi ya fito kamar ɗan Saurayi dan
Shekara Talatin da Biyar, Tana ta satar kallonsa bai nata magana ba, sai da ya gama
kana ya Riƙo Hannunta ya miƙar da Ita yana Faɗin "Muje ko.."
Kasa kallonshi tayi ta sadda kanta ƙasa, har suka Fito Daga Bedroom Farida na Saman
Dining bayan ta gama Shirya komai ita da Basma da Bassam da Naila da Iya, Hangosun
da yayi yasa ya saki hannun Mufeeda saboda idanuwan yaran, Farida ko Sau Ɗaya ta
kallesu bata ƙara ba Har suka ƙarasa Saukowa, Farida Jikinta na rawa Ta ja musu
kujeru suka Zauna yana amsa gaisuwan iya Cikin Fara'a yace "Ina su Airah...? Farida
Tace "Har sunyi barci kasan su Da sunji Ruwan zafi Shikenan.." Bai ce komai ba
Illah Basma Da tace "Daddy yau fa girkin Momy zamu ci dana Aunty Mufeeda." Baki
Tahir ya washe yana Faɗin "Realy...? Lokaci Ɗaya yana kallon Farida Ita kuma tana
kallon Mufeeda Suna Dariya hannu yasa bisa Ƙirji yana Faɗin "Uhm..Lalle Tahir ya
zama Ɗan gata.."
Ya faɗa yana Murmushi Farin ciki ya Cika ranshi, ba wanda ya ƙara magana har Farida
ta sallami kowa suka Fara cin abinci, Tahir kuwa ya Zuba santi kamar ba gobe har
Farida na saka mai Waigi Ranar Haka Suka gama cin abinci Cikin Farin ciki wanda
Suka Daɗe basuyi ba bayan sun koma suka koma Falo Suka Zauna suna Hira da 'ya'yansu
Har su Airah suka tashi Iya ta kawo ma Mufeeda ta basu Nono bayan ta gama ne Tahir
ya Ɗaukesu yana Musu Wasa Farida bata bari Hiran yayi tsawo ba tace kowa ya wuce
ɗakinsa yayi wanka yayi sallah kafin ya kwanta Tun da yau basu Fita sallah ba...
Ita ta karɓi Su Airah tana Faɗin "Allah tashemu lafiya...Ango Asha Amarci lafiya.."
Ta faɗa ta Wuce da Sauri Jikinta na Ɗan Rawa Sabida yadda wani Duhu ya mamaye mata
Zuciya, Da kallo Suka Bita Tahir ne kaɗai ya amsa mata da Allah tashemu lafiya.
Miƙewa yayi bai tsaya wata magana ba ya Riƙo hannun Mufeeda ya miƙar da ita Tsaye
kuma bai yarda sun Haɗa ido ba suka Nufi Bedroom ɗinshi, Ita kuwa Farida kan
gadonta ta kwantar dasu Airah Itama ta Sulale tana Sakin kukan Data ke Danewa wani
kishin Tahir ne ke taso mata, Sheɗan na Zugata amma tana ƙoƙarin yakiceshi Da ƙyar
ta miƙe ta Faɗa Toilet tana Rangaji.
Suna Shiga Bedroom ɗin Tahir ya saketa yana Faɗin "Ki shiga ki ɗauro alwala.." Bata
yi musu ba ta Shiga ya bita da kallo yana Murmushi bata jima ba ta Fito tana Faɗin
"Daddy na Fito.." Kallonta yayi kai tsaye kafin yace "Sallah zamu yi.." Kai ta
gyaɗa kafin tace "Bani da Hijabi anan Ɗakin.." Bai mata magana ba illah Ficewa Da
yayi har Zuwa Ɗakinta ya Buɗe Wardrope ɗinta ya Ɗauko mata Hijabi da wata Arniyar
Rigar barci ya kawo mata Duk Farida najin Fitarshi da Dawowarshi tana Zaune kan
sallaya bayan ta idar da sallah Hawaye na Zuba daga cikin idanuwanta..
Miƙa mata yayi Haɗe da Rigar barcin yana Faɗin "In mun idar sai ki saka wannan
rigar barcin.." Ido ta Waro Tana Faɗin "Kai Daddy.." hararanta yayi ya wuce bai
mata magana da Sauri ta kama bakinta tana Faɗin "Bazan ƙara ba." Murmushi kawai ya
saki shima ya Faɗa Toilet d'in Mufeeda daban take, Komai tayi cikin bada Haƙuri
take, Alwala ya Ɗauro Shima ya Fito kafin yajasu sallar sai da sukayi sallar Isha'i
kana yajasu Raka'a Huɗu bayan sun idar ya dinga kwaroro musu Addu'ar zaman lafiya
Mufeeda na amsawa da Ameen.
Tashi yayi ya isa saman Side Drower d'in gadon ya Ɗauko Madaran Hollandia ya
Tsiyaya cikin Kofi ya cikashi yazo gabanta ya Zauna ya miƙa mata ta saka hannu zata
karɓa ya Girgiza mata kai yana nuna mata bakinta ganin yadda ya Haɗe Rai, yasa ta
buɗe baki ya shiga bata sai da tasha fin Rabi, kana ta kauda kai bai matsa mata ba
shima sai ya ƙafa kai ya ƙarashe Shanyewa ya Miƙe ya maida komai inda ya Ɗauko
kafin ya Dawo Agabanta ya Ƙara Zama wannan karon gwiwowinsa yana Gugan nata, Lokaci
Ɗaya ya Riƙo Hannnayeta yana Faɗin "Kinga kalleni.." Ɗagowa tayi tana kallonsa
Cikin kunya ganin yadda yake mata wani kallo yace "Ki saki jiki dani mana Mufeeda
bana son Abunda ki kemin kinji..." Gyaɗa kai tayi tana Faɗin "Bazan ƙara ba.."
Hannunta ya Sumbata yana Faɗin "In kika ƙara sai na Hukuntaki.." Jikinta ya mutu
cikin Sanyinta ta langwaɓar da kai tana Faɗin "Allah bazan ƙara ba.."
Yana yar Dariya yace "Naƙi wayon..? Hukunci ne baki so ko..? Ta gyaɗa kai bazato ba
Tsammani taji ya kama kanta ya Ɗora Leɓensa bisa nata ya Fara Tsotsa Lokaci Ɗaya
taji jikinta ya ɗau kyarma jin Baƙon lamari ya Daɗe yana Tsotsan Leɓenta Cikin
Fitan hayyaci ta saki Bakin nata har ya kama harshenta, cikin ƙwarewa yake Sumbatar
ta lokaci Ɗaya yana maida Numfashi sun Ɗauki Tsawon Lokaci kafin ya saketa ya koma
kuma ya Kwantar da kanshi Bisa Ƙirjinta yana maida Numfashi Itama jikin gado ta
maida kanta tana Sauke Numfashi Cikin Shakewar Murya Tahir yace "Koda irin wannan
Hukuncin ne Mufee..?
Ba tayi magana ba illah Runtse ido Datayi wani yanayi na Shigarta Jinsa Acikin
Jikinta, bai ɗago ba sai da ya Daidaita kansa kana ya Tashi Lokaci Ɗaya ya Ɗagota
Suka miƙe tare Hijabin jikinta ya Cire mata yana Faɗin "Ki saka Rigar barcin Mufee,
I need u bazan miki ƙarya ba karki jamin Rai plz.." Ya faɗa yana ƙura mata
Lumsassun idanuwansa Da Suka Fara Chanza Launi, Rigar barcin ya Ɗauko ya miƙa mata
Shi kuma ya Buɗe Wardrope ya Ɗauki wata jallabiyarsa ya Shiga Toilet saboda ya bata
daman Shiryawa, cikin Sauri ko ta kwaɓe tana yi tana kallon kofar Bedroom d'in,
Tana ƙoƙarin Saka Hijabi ya Buɗe ƙofa ya Fito da Sauri ya ƙaraso yana Riƙo Hijabin
Cikin Wani narkakken kallo yake Faɗin "A'a bana so.."
Ya faɗa yana marairaice Fuska jin haka yasa Jikinta ya Mutu ta sakar mai tana kare
Ƙirjinta Tunda pant ta bari kaɗai hatta bra sai da ta cire, Nonuwanta da Suka cika
da ruwa sunyi ɓul ɓul dasu Bai tsaya Sauraranta ba ya rungumota ta baya ya saka
hannu ya Cire Hannayenta Daga kan Ƙirjinta ya Ɗora nashi Lokaci Ɗaya yaja Numfashi
Cikin Shinshinar Wuyanta lokaci Daya kuma yana Shafa Ƙirjinta Zuwa Wuyanta Cikin
Lokaci kaɗan ya Rikita kansa kuma ya Rikita ta Domin Mufeeda Haka Ta saki jikinta
Sosai Tun Suna Tsaye Har Suka Danganta Da kan gado Cikin Dubara Tahir ya saka hannu
ya kashe Wutar Ɗakin ya Kunna Dum light.
Cikin ƙwarewa Yake Sarrafa Mufeeda Ƙirjinta Su sukafi Jan Hankalinsa kuma suke
Rikitashi, Itama banƙaro mai ƙirji kawai take tana jin Wani Daɗi na Tsirga mata Har
ya Saɓule Rigar barcin bata sani ba kai Tahir ƙarshe ne ya kai makura wajen iya
Sarrafa mace, Domin ko'ina na Jikin Mufeeda sai ya amsa Domin babu inda bai bi ya
lashe da Harshensa ba Mufeeda ta Haukace sosai Lokacin da Bakin Tahir ya kai
ƙasanta Haka ta Riƙe kanshi tana kukan da batasan ko na mene ne ba, Ya gama Rikita
ta Shima ya Rikita kansa bata yi Aune ba Taji ya Sunkuyo da kansa yana karanta
addu'ar Saduwa da iyali ya haɗe bakinsu Waje Ɗaya, kafin ya Danna kai sai Lokacin
Mufeeda ta dawo Hayyacinta jin Azaba na cinta ta Shiga Tureshi amma Ina ta makara
domin da ƙarfinsa ya Danna kai cikin magagi Tahir yace "Ya salam..." jinshi Tsundum
cikin ƙoramar Daya Daɗe yana mafarki bai tsaya wasa ba ya Shiga Haƙarta cikin
Zaucewa da Fitar Hayyaci, Kuka Mufeeda keyi Domin tasha gyara ta koma ta Haɗe duk
da Azaban bai kai na Farko ba amma ta Ɗanɗana.
Sai da ya shafe minti Arba'in yana Abu Ɗaya kafin ya ƙanƙameta yana Sakin Numfashi,
Haka ya ƙanƙame Mufeeda yana Kwarara mata albarka Tana kuka tana komai ya Ɗauketa
suka Shiga Toilet ya gasata kana sukayi wankan Tsarki Suka Fito Domin Tun Mufeeda
najin kunyarsa har ta ware Domin karatun Daddyn nata ya Girmi Shekarunta Naɗota
yayi Cikin Towel Suka koma Suka kwanta Ya Rungumeta Yana mai Jin Wani farin ciki
sosai, Barci Tuni ya sace ta Shima Daga baya barcin ya Tafi dashi mai Daɗi.
*****
Da Asuba ma tare sukayi wanka Mufeeda sai Zille zille take, Shiko ko Ajikinsa,
wajen wanka ma sai da ya ƙara morewa son Ranshi kafin suyi wankan Su Fito, Ya barta
shi kuma ya saka kaya agurguje zuwa masallaci yau ɗin ko Tsayawa Ma Sauraran
Wa'azin da akeyima kullum Safiya bai tsaya ba jiki na rawa ya Dawo gida Mufeeda na
cikin bargo ko kaya bata saka ba Tunda bata da kaya a ɗakin ya Sake Ƙwaƙumarta
Mufeeda taga ta kanta Domin Duk Kukanta sai Da Tahir ya sake, Sai Da ya samu
natsuwa sosai kana ya Rungumeta yana lallashinta ita ko Tana tamai Taɓaran Shagwaɓa
Yana biye mata Abun na ƙara Rikitashi, kwanciya sukayi Daga nan kuma sai barci Sai
Wajen 9 suka tashi, wannan karon kuwa Mufeeda taga Abun Da ya isheta Cikin Jazucci
haka yake lasanta kamar zai Cinyeta Ɗayan Cikin Kunya da Nauyi tace "Kai Daddy..."
Yana wasa da Boobs Dinta da Suka Sake cika Yake fadin "U better stop calling me ur
Dad...Ni ba babanki bane.." Cikin Tura baki tace "Kai Babana ne.." Bai bata amsa ba
sai da ya Tsotsi bakinta kana yace "Babanki bazai miki irin Abun da nake miki ba.."
Ya faɗa yana kashe mata ido Ɗaya ƙirjinsa ta faɗa tana mai Dukan wasa Da ƙyar yayi
wankan Tsarki ya fice ya barta bayan ya gama latsata son Ranshi gasa kanta tayi
kafin tayi wankan Tsarki ta Fito, Jin Nonuwanta nata Zuba ne yasa ta gane Su Airah
sun tashi suna kuka Tahir ta kallah wanda ke murza Hulan kansa tace "Daddy su Airah
sun tashi..?
Yana Ɗaure agogon Hannunsa yace "Eh Suna wajen my Farida karki damu muje.." Hijabi
tasaka Bayan Towel na Daure Ajikinta Suka Fice Daga Ɗakin, Suna Zuwa Falo suka iske
Farida na goye da Airah, Ayman na Hannunta tana ta Faman Jijjigashi yana kuka Tahir
ne ya samu daman ƙarasowa gareta ta gaisheshi ya amsa yana karɓan Ayman Cikin Kauda
kai Mufeeda ta gaida Farida ta amsa itama bata kalleta ba da Sauri ta Shige ɗakinta
Sauri Sauri ta saka wata Riga da Zani na les cikin kayan Tariyar da Tahir yayi mata
ne, Ta Fito Zata karɓi Ayman Farida ta Hana tace su Fara karyawa Tukunnah gidan
babu kowa Sun Tafi makaranta Harda Naila itama an saka ta Iya ce kaɗai ke Kichen
tana Wanke wanke, shi kuma ya kama Hannun Mufeeda suka Nufi Dinning d'in tana ta
Zillewa amma Tahir yaƙi sakinta Farida Sau Ɗaya ta kallesu ta juya kanta tana ta
Jijjiga Ayman dake Hannunta, Idanuwanta suna Fitar da Ƙwallah domin Daga yanayinsu
ta san komai ya sake Faruwa Saurin koran Sheɗan Tayi.
Ko wajen cin Abinci Haka Tahir ya dinga tsokanar Mufeeda ita kuma kunya Duk ya
kamata, Farida Data ga Haka sai ta koma sama kawai abunta bata son ganin Abunda zai
sa Aga Rauninta, Tana Tafiya Mufeeda ta marairace tana Faɗin "Don Allah Daddy ka
bari kaga Momy taji ba Daɗi har ta koma sama.." Shuru yayi kafin yace
"Hakane...Bazan ƙara ba Cutie.." Ya faɗa yana lakace mata hanci Dariya tayi Suka
Cigaba da cin Abincin nasu cike da ƙauna Lokaci Ɗaya suna aikama juna kallon
Soyayyah da ƙauna mara yankewa.
Haka rayuwar gidan Tahir ya cigaba da kasancewa cikin Murna da Farin ciki da Zaman
lafiya Abun sai wanda ya gani, duk wacce keda miji zasu haɗu suyi girki tare komai
nasu gwanin ban sha'awa Wahalan Renon su Airah kuwa Farida ne da Iya Tsakaninsu da
Mufeeda kuwa sai in zata basu Nono Farida na bala'in so wad'annan 'ya'yan gashi ita
kuma Haihuwa Shuru Duk da taje Asibiti An buɗe mata bakin Mahaifa amma kuma Har
Zuwa Wani Lokaci Shiru sai ta maida Hankalinta wajen Kula da Su Airah kamar ta
lashesu Saboda yadda Take bala'in sonsu.
Zamansu gwanin ban sha'awa ko Su Umma suna alfahari da Chanzawar Farida, hakama
chan Ɗanbatta Hakimi hankalinsa ya kwanta ganin Walwalar Ɗansa ta Dawo Awajen Aiki
kuwa Ishaq sai ma Tahir Tsiya yake wai yaji daɗin Mata sai kiɓa yake yana Tumbi
kuma da gaske ne Domin Tahir ya samu kwanciyar Hankali sosai, Duka matan nashi suna
ƙoƙarin kyautata mai shima kuma yana ƙoƙarin kwatanta Adalci Baya nuna wanda yafi
Wani Afili sai dai ya bar kanshi kawai Ɓangaren Mufeeda kuwa dama Akwai ɓoyayyiyar
soyayyar Daddynta Cikin Lokaci ta Fito Dashi, Bata mai gardama komai ya keso shi
take mai shiyasa Cikin Lokaci ƙanƙani ta mamaye mai Zuciya, gashi baya gajiya da
ita kamar yadda itama bata gajiya dashi Farida kuwa Tana da matsayi sosai amatsayin
ta na Uwargida kuma uwar 'ya'yansa Uwa uba kuma Dalilin ta ne Zaman lafiya ya Zauna
a gidan Tahir Yanzu Zumuncinsu ya Dawo Sabo da Zahra matar Ishaq, Bilkisu har gida
tazo tana Zugata wai ta zama baiwar Mufeeda ta zama mai mata rainon 'ya'ya, nan
tayi mata Fata fata ta koreta Ta watsar kuma da duka ƙawayen banza ta riƙe Mufeeda
da Zahra kawai domin Samun Sukunin Zuciya Tana ƙoƙarin Ɓoye Kishinta Saboda Tahir
na kwatanta Adalci a tsakaninsu...
*******
*AFTER 5 YEARS*
Bayan Shekara Biyar Abubuwa Da dama sun Faru na Farin ciki da Akasinsa amma Aciki
na Farin cikin yafi yawa Domin A shekarar Data gabata ne Iyalan Tahir suka tattara
suka koma Lagos a Victoria Island, Inda ya gina wani katafaren gida Haɗe da
katafaren Kamfani mai Taken *ƊANBATTA MOTORS LIMITED* da guminsa, Bayan ya barma
Ishaq wanchan kamafanin na Abba a Kaduna yana kula Dashi, saboda amanarsa da
Hazaƙarsa Duk da Dukkansu Cigaba ne ya Samesu amma Sunyi baƙin cikin Rabuwa da
Juna.
A waɗannan Shekarun Tahir ya ƙara zama magidanci domin Arziki yaci uban nada, Baga
iyalansa kaɗai ba Hatta ga iyayensa ma suna yabansa, Garinsa ko Ɗanbatta basu da
abun alfahari sama dashi, yana ƙoƙarin Biya musu Buƙatunsu, ya gina musu Rijiyoyi
da kuma Bohol, hadda k'aramin Asibiti ya gina musu mai suna MANSUR CLINIC, Abun sai
wanda ya gani Ashe kuwa Yanzu ta zama Hajiya Aisha Tuni Tahir yayi ma Mijinta hanya
ya samu aiki a kamfanin Abba Dake Kaduna in da ya bari suna aiki tate da Ishaq, Sun
bar garin Ɗanbatta Tuni suka koma Kaduna da zama, Baba Hakimi babu Abunda ke Shiga
Tskaninsa da Tahir sai godiya da Fatan Alheri, haka su goggo Komai na Jin Daɗin
Rayuwa ya mallaka musu, Duk Da Baba Hakimi ya Tsufa amma yana gudanar da Sha'anin
mulkinsa Domin ya Jiƙu da Hutu da Jin Daɗi Tuni Tahir ya maida Garzali makaranta
yana Ɗaukan Nauyin karatunsa, Rayuwa tayi kyau Abun sai wanda ya gani.
Su Airah nada wata goma sha Biyar Mufeeda ta sake samun Wani Cikin Farida ta karɓi
su Airah ta yayesu ita kuma Mufeeda ta cigaba da kula da rainon cikinta, Lokacin
har ta yi Jsce ta koma Makaranta,Sai da cikin ta ya Tsufa kana ta daina Zuwa
Makaranta lokacin tana Ss2 ne Achan ko garin Ɗanbatta kowa Ɗauka yake cikin jikin
Mufeeda Shine na Farko su Airah kuma Farida Ta Haifesu Tunda ba wanda ya sani sai
su kansu da komai ya Faru suna nan, Hajiya Iya kuwa 'yan'uwanta sun so su Ɗauketa
amma Tahir ya hana yace Ai Iya Ta Riga ta zama tamu Dole suka yi Haƙuri Suka
ƙyaleta.
Na ƙara Haihuwan mace Ta ci Sunan Goggo Abu muna kiranta Ayda, tana da Wata Takwas
na ƙara Samun wani cikin wanda nayi ta kuka Farida ko da Tahir nata Murna ta karɓi
Ayda ta yayeta Lokacin su Airah suna Ɗanbatta wajen Innaro, cikina na wata Bakwai
suka Tafi Aikin Hajji Dukkansu, Goggo Abu, Innaro Ashe, Iya, Tahir, Ishaq, Zahra,
Farida, sai Abba da Umma da Baba Hakimi, Ashe da Mijinta da su Basma.
Ni Kaɗai kawai aka bari agida sai Maman Lantana ita ta Zauna dani har Suka Dawo
Wacce nake Kallo tamkar mahaifiyata Lantana ma tana Kano abunta muna waya sosai
itama, ta cigaba da karatu, Lokacin da suka Dawo Cikina yayi girma kwana goma da
dawowarsu na Haifi Santalelen yarona Namiji wanda yaci sunan mahaifina muna kiransa
Walid, Duka 'ya'yana Ba zaka ce ni na Haifesu ba Domin komai nasu yana Ɗakin Farida
ne, itace uwarsu, Tsakani na Dasu Aunty Mufeeda ne kaɗai, in ka kalleni bazakace
nine keda 'ya'ya Har Huɗu ba saboda yanayin Jikina, Bayan na Haihu da wata uku Ciki
ya Ɓulla a jikin Farida Murnan da mukayi ba kama Hannun yaro bamu tafi Hajji ba
Nida Tahir sai da mukayi Jarabawar WAEC da NECO lokacin Walid nada wata goma Sha
Uku Na yayeshi na Damkama Farida da Iya, Bamu samu Tafiya ba sai da mukayi Walimar
Buɗe kamfanin Tahir da kuma Tariyarmu Asabon Gidanmu kana Muka Tafi Ni dashi,
kwananmu Talatin agarin Makka muka Wuce England, Mukayi kwana goma, sai muka Dira a
India saboda nacema Tahir ina son garin mune Har America munsha yawo, Honey Moon da
bamuyi abaya ba muke Ramawashi yanzu, Sai da muka Shafe wata biyu da wani Abu kana
muka dawo Gida, koda na Dawo na kwaso Tsaraban Honey Moon, Munyi kiɓa munyi jajir
alamun munsha Hutu Sosai Farida da yaran sukaje Filin Jirgi Suka Ɗauko mu Lokacin
Cikinta Har ya Fito, Duka duka kwanan mu goma ne da Dawowa Duka yaran da Suka
Tattara suka Tafi Ɗanbatta Hutu suda Iya da Maman Lantana, Su kuma Basma da Bassam
Dama Suna chan Tun bayan Tafiyarmu Farida kuma ta tafi Kano Duba jikin Abba Nida
Tahir kaɗai suka bari agida naso na Bita Amma Laulayin Ciki ya Hanani Sukuni Dole
na Zauna agida.
Tun muna India na Nuna ma Daaddy ina son na Cigaba da karatu na, nan ko ya nuna bai
yarda ba kuma bazai taba yarda ba ya tambayeni a faɗin Duniya mai na rasa nace mai
babu yace toh matuƙar ban rasa komai na Duniya ba maganar karatu na barta Karatuna
kenan na Zauna na kula da mijina Haɗe da 'ya'yana Lokacin Kuma ina Cigaba da
Zazzage mai kwansa A duniya.
Maganar gaskiya ban Rasa komai na Duniya ba, Ilimin nan dai-dai gwargwado ina dashi
waye wa ma Haka domin yanzu na zama babbar mace babu Abunda wata macen zata Nuna
min game da Namiji Daddy ya riga ya gama Zama malami na kuma bango na Shi ɗin da
gaske garkuwa ne agareni bai taɓa bari nayi kukan maraici ba ko sau ɗaya Koda
yaushe Cikin bani kulawa yake, Yana tattalina kowani Jin Dadin na Duniya yana bani
ni kuwa mai Zan je na Tsinta in na cigaba da karatun mijina na sona, iyayensa naji
dani kamar su lashe ni ina da 'ya'ya Me zan nema nan Duniya wanda Allah bai bani
ba..? Babu domin Bayan Iyayena da suka kawoni Duniya Bani da kamar Daddy shine
Mijina, kuma bango na kana kuma Shi ɗin wata Garkuwa ne agareni.
*****
Ina Zaune Ina Sauke Numfashi Bisa makeken gadonmu Tahir Dake kwance cikin blanket
na Mintsina ina Sakin Kukan Shagwaɓa Cikin barci ya Buɗe ido yana kallona
Hankalinsa tashe ya Miƙe yana Faɗin "Cutie wai lafiya kike ta ƙananun kuka Tun
Ɗazu..?
Ya faɗa idanuwansa da barci, Kan Jikinsa na Sulale ina Faɗin "Toh ba cikin ka bane
ke Wahalar dani ba...Komai naci baya zama sai na amayar dashi.." Murmushi ya saki
yana gyara min kwanciya Lokaci Ɗaya yana wasa da gashin kaina yace "Umh..Wato na
gane so kike kawai Dai na Taɓaki ko..? Ya faɗa yana Kallonta Kwaɓe Fuska tayi kafin
tace "Ni..Yaushe nace kai dai Daddy kace zaka min wayau da ka saba.." Bata ankara
ba taji ya maidata ƙasanshi yana Faɗin "Ni Wlh ke kemin wayau koda yaushe cikin
amshe min Kuzarina kike, ke ɗin fa da ba domin ina ƙarawa da maganin ƙarfin maza ba
da Tuni kinfi ƙarfina.." Ya faɗa yana mata Dariya baki ta Buɗe Tana Kallonsa Lokaci
Ɗaya ta fara Tureshi tana sakin mai kukan Shagwaɓa Shi kuma yana dariya Lokaci Ɗaya
ya Kama bakinta yana Faɗin "Muyi aikin lada Cutie bayan mun gama nayi lallashin
Gaba ɗaya.." Ya faɗa yana haɗe bakinsu waje Ɗaya, cikin Sauri itama ta tallabi
kanshi, Suka Fara Sumbatar juna cikin ƙwarewa Lokaci Ɗaya suna ƙara Rikita juna da
Salon da kowanne yasan yana Kunno Ɗan'uwanshi Sai da Suka Ɗauki Tsawon Lokaci kafin
Tahir ya saki bakinta yana kallon Cikin idanuwanta yace "Cutie ina Sonki...Ina
ƙaunarki ƙaddarar Data Haɗamu ta Alheri ce..Allah yayi miki albarka.." Ya faɗa
cikin Sanyin Murna Rungumeshi tayi tana Faɗin "Alhamdulillah...Kai ne
garkuwata..Mijina Abun alfaharina..Ina matuƙar Sonka..."
Ta faɗa Lokaci Ɗaya tana Haɗe bakinsu Waje Ɗaya, Cikin Zalama kowannensu ke aikama
da Ɗan'uwansa Saƙo.
*ƘARSHE...*
*ALHAMDULILLAH...*
```Godiya ta mussaman ga Groups din da sukayi Jimarin Binmu Tun daga Farko Har Zuwa
ƙarshe basu gajiya da Sharhi koda yaushe kamar su JANAF NOVELL 1&2,,AISHA ALTO
NOVELS,TASKAR LITTAFAN HAUSA,NANNY CANSERVATION ROOM,NANY FANS GROUP,MARYAM
NOVELS,ZAUREN JANAFTY,MASAURATAR SHAKIRA JANAFTY,ZAUREN KHADIJA CANDY,INTELLIGENT
FANS,1&2,ZAUREN SAINA,FEEDHOM NOVELL, BENEFICIAL WRITER'S, MASOYAN SHALELE, Da duka
Sauran groups d'in da bamu ambata ba Muna godiya gareku masoyanmu Wanda muka sani
da wanda bamu sani ba Muna godiya Sosai Allah yabar Zumunci our wattpadians Fans
ɗinmu kuma muna godiya sosai Da Soyayyarku muna ganin Vote ɗinku da Shairhinku Muna
godiya Love u all....Allah ya bar Zumunci...One luv```
_Albishirinku Masoyanmu Muna tafe muku da wani albishir na Sabbin *SANYAYA BIYU*
wanda zasu zo muku Daga Alƙaluman Tagwayen marubutanku ɗin nan Guda Biyu, Wato *MR
BELLO...* na Jamila umar Janafty, wacce ta Daɗe tana Nishaɗantar da ku cikin
Zafafan Littafanta, masu matuƙar Daɗi da Faɗakarwar, Kunsanta kuma ta sanku, kun
gwada kuma kun gani ku zaku ba wasu labari, Labari ne mai cike da Cin Amana,
Tausayi,da mugunta, haɗe da Soyayyah mai Zafi mai tsayawa azuciyar masoya, Domin
kasancewa cikin Waɗanda zasu ci karo da wadanan Abubuwan zaku Biya kuɗin karatu
akan Naira ₦300 kachal domin more karatunku cikin kwanciyar Hankali da Aminci._
_Itama Ɗayar gwanar taku Wato Aisha Alto itama tana tafe muku da Nata salon mai
taken *MATAR NASEER...* ku Daga jin sunan kunsan namu ba irin nasu bane labari ne
mai Shiga Zuciyar mai karatu yadda mata ke Shanye Takaichin ɗa namiji, gori da kuma
Soyayyah mai Tsuma Zuciya Duk zaku samesu ne kan Farashi mai Sauƙi ₦300 kachal babu
Tsada mai buƙatar guda biyun kuma Zai biya ₦500, zamu yi muku VIP shima wanda ke
Buƙatar ƙarin bayani Zai iya Tuntuɓarmu ta lambobin wayar da zamu bada...Ina kuke
masoyanmu ku Hanzarta, ku yunƙuro wajen Nuna mana naku salon Soyayyar wajen Siyan
Sabbin Novels ɗinmu Mun san bazaku bamu kunya ba...Kar ku manta koda kuɗinka sai da
Rabonka..._
Domin neman ƙarin bayani ko ƙorafi ko gyara Za'a iya Tuntuɓarmu ta waɗannan
Nombobin wayar kamar Haka👇
09069067488
08147672049
*Anitha..*
*Aisha Alto*