SiyasaJamhuriyar Kwango
Kwale-kwale ya kama da wuta a Kwango ya kashe mutane 143
April 19, 2025Talla
Gobarar da ta tashi a cikin jirgin ruwan katakon da ke dauke da man fetir a ranar Talata a wajen Mbandaka, babban birnin lardin Equateur dake a ke arewa maso yammacin Kwangon:
Har yanzu ba a san dalilan tashinta ba, sai dai ana gani ba za ta rasa nasaba,ba da man fetir din dake cikin jirgin.Tun farko an gano rukunin gawarwaki 131 a ranar Laraba, yayin da wasu 12 aka ganosu a ranakun Alhamis da Juma'a. in ji Joséphine-Pacifique Lokumu, yar majalisar dokokin kasar da ta ziyarci wurin da lamarin ya afku.