Isa ga babban shafi
Chadi-Boko Haram

Chadi na nan daram a yaki da Boko Haram

Gwamnatin Faransa ta ce, har yanzu kasar Chadi na nan cikin dakarun da ke yaki da 'yan ta’adda a rundunar G5 Sahel duk da ikrarin shugaba Idris Deby na cewar dakarun kasarsa za su janye daga yaki a wajen iyakokin kasar.

Shugaban Chadi Idriss Deby Itno
Shugaban Chadi Idriss Deby Itno REUTERS/Carlo Allegri
Talla

Ministar Tsaron Faransa Florence Parly ta sanar da haka lokacin da take yi wa kwamitin tsaro a Majalisar Dattawa bayanai, wanda ya kunshi shirin Chadi na tura bataliyan soji zuwa Mali nan gaba.

Shugaba Deby cikin fushi ya ce, zai janye dakarun kasar daga duk wani yaki a wajen iyakokin kasarsa bayan kisan gillar da mayakan Boko Haram suka yi wa sojojinsa kusan 100, abin da ya sa ya kaddamar da yaki akan su, inda kasar ta sanar da samun gagarumar nasara bayan kashe mayakan kungiyar sama da 1,000.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.